< Josué 4 >

1 Lorsque toute la nation eut entièrement traversé le Jourdain, Yahvé parla à Josué et dit:
Da al’umma gaba ɗaya suka ƙetare Urdun, Ubangiji ya ce wa Yoshuwa,
2 « Prenez douze hommes parmi le peuple, un homme de chaque tribu,
“Ka zaɓi mutum goma sha biyu daga cikin mutane, ɗaya daga kowace kabila,
3 et donnez-leur cet ordre: « Prenez au milieu du Jourdain, à l'endroit où les pieds des prêtres se sont arrêtés, douze pierres, emportez-les avec vous et posez-les à l'endroit où vous camperez cette nuit ».
ka ce musu kowa yă ɗauki dutse ɗaya daga tsakiyar Urdun daidai inda firistoci suka tsaya, ku kai su, ku ajiye a inda za ku sauka yau.”
4 Alors Josué appela les douze hommes qu'il avait préparés parmi les enfants d'Israël, un homme de chaque tribu.
Sai Yoshuwa ya kira mutum goma sha biyu da ya zaɓa daga cikin Isra’ilawa, ɗaya daga kowace kabila
5 Josué leur dit: « Traversez devant l'arche de Yahvé votre Dieu jusqu'au milieu du Jourdain, et chacun de vous ramassera une pierre et la mettra sur son épaule, selon le nombre des tribus des enfants d'Israël.
ya ce musu, “Ku je tsakiyar Urdun inda akwatin alkawari na Ubangiji Allahnku yake. Kowannenku yă ɗauki dutse ɗaya a kafaɗarsa, bisa ga yawan kabilan Isra’ila,
6 Ce sera un signe parmi vous, et lorsque vos enfants demanderont plus tard: « Que signifient ces pierres? »
yă zama muku alama. Nan gaba in yaranku suka tambaye ku suka ce, ‘Mece ce ma’anar kasancewar duwatsun nan a nan?’
7 vous leur répondrez: « Parce que les eaux du Jourdain ont été coupées devant l'arche de l'alliance de Yahvé. Quand elle a traversé le Jourdain, les eaux du Jourdain ont été coupées. Ces pierres serviront de mémorial aux enfants d'Israël pour toujours ».
Sai ku ce musu, ruwan Urdun ya yanke a gaban akwatin alkawari na Ubangiji, a lokacin da akwatin alkawarin ya ƙetare Urdun. Waɗannan duwatsu za su zama abin tuni ga Isra’ilawa har abada.”
8 Les enfants d'Israël firent ce que Josué avait ordonné et ils enlevèrent douze pierres du milieu du Jourdain, comme Yahvé l'avait dit à Josué, selon le nombre des tribus des enfants d'Israël. Ils les transportèrent avec eux jusqu'au lieu où ils campaient, et les y déposèrent.
Isra’ilawa kuwa suka yi yadda Yoshuwa ya umarce su. Suka ɗauki duwatsu guda goma sha biyu bisa ga yawan kabilan Isra’ila, yadda Ubangiji ya gaya wa Yoshuwa; suka tafi da su masauƙinsu, a can suka ajiye su.
9 Josué dressa douze pierres au milieu du Jourdain, à l'endroit où se tenaient les pieds des prêtres qui portaient l'arche de l'alliance; elles y sont encore aujourd'hui.
Yoshuwa ya ɗora duwatsu goma sha biyun a tsakiyar Urdun daidai inda firistoci waɗanda suke ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji suka tsaya. Suna nan a can har wa yau.
10 Car les prêtres qui portaient l'arche se tinrent au milieu du Jourdain jusqu'à ce que soit achevé tout ce que Yahvé avait ordonné à Josué de dire au peuple, selon tout ce que Moïse avait ordonné à Josué; et le peuple se hâta de passer.
Firistocin da suke ɗauke da akwatin alkawari suka tsaya a tsakiyar Urdun, har aka gama dukan abin da Ubangiji ya umarci Yoshuwa yă gaya wa mutane, kamar yadda Musa ya ce Yoshuwa yă yi. Mutanen suka wuce da sauri.
11 Lorsque tout le peuple eut complètement traversé, l'arche de Yahvé traversa avec les prêtres en présence du peuple.
Sai da dukan mutanen suka wuce sa’an nan akwatin alkawari da firistoci suka sha gaba.
12 Les fils de Ruben, les fils de Gad et la demi-tribu de Manassé passèrent armés devant les enfants d'Israël, comme Moïse le leur avait dit.
Mutanen Ruben, Gad da rabin kabilar Manasse suka ƙetare da shirin yaƙi, suka wuce gaban Isra’ila kamar yadda Musa ya ce su yi.
13 Environ quarante mille hommes, prêts et armés pour la guerre, passèrent devant l'Éternel pour combattre, dans les plaines de Jéricho.
Wajen mutum dubu arba’in shirye domin yaƙi, suka wuce a gaban Ubangiji zuwa filayen Yeriko.
14 Ce jour-là, l'Éternel magnifia Josué aux yeux de tout Israël, et ils le craignirent, comme ils avaient craint Moïse, tous les jours de sa vie.
A ranan nan Ubangiji ya ɗaukaka Yoshuwa a gaban Isra’ilawa; suka kuma ba shi girma dukan kwanakin ransa, kamar yadda suka girmama Musa.
15 Yahvé parla à Josué et dit:
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Yoshuwa,
16 « Ordonne aux prêtres qui portent l'arche de l'alliance de sortir du Jourdain. »
“Ka umarci firistocin da suke ɗauke da akwatin Shaida su fito daga cikin Urdun.”
17 Josué donna cet ordre aux sacrificateurs: « Montez du Jourdain! »
Sai Yoshuwa ya umarci firistoci ya ce, “Ku fito daga cikin Urdun.”
18 Lorsque les prêtres qui portaient l'arche de l'alliance de Yahvé furent sortis du milieu du Jourdain, et que la plante des pieds des prêtres fut levée sur la terre sèche, les eaux du Jourdain retournèrent à leur place et passèrent par-dessus toutes ses rives, comme auparavant.
Firistocin kuwa suka fito daga kogin ɗauke da akwatin alkawarin Ubangiji. Nan da nan da ƙafafunsu suka taɓa busasshiyar ƙasa, sai ruwan Urdun ya gangaro ya cika kogin kamar yadda yake a dā.
19 Le peuple sortit du Jourdain le dixième jour du premier mois, et il campa à Guilgal, à la frontière orientale de Jéricho.
A rana ta goma ga wata na farko, mutane suka haura daga Urdun suka sauka a Gilgal a gabashin iyakar Yeriko.
20 Josué dressa à Gilgal les douze pierres qu'ils avaient prises dans le Jourdain.
Sai Yoshuwa ya kafa duwatsu goma sha biyun nan da suka ɗauko daga Urdun.
21 Il parla aux enfants d'Israël et dit: « Lorsque vos enfants demanderont un jour à leurs pères: « Que signifient ces pierres? »
Ya ce wa Isra’ilawa, “Nan gaba in yaranku suka tambayi iyayensu suka ce, ‘Mece ce ma’anar waɗannan duwatsun?’
22 Vous le ferez savoir à vos enfants en disant: « Israël a passé ce Jourdain à sec.
Ku ce musu, ‘Isra’ilawa sun ƙetare kogin Urdun a kan busasshiyar ƙasa.’
23 Car Yahvé ton Dieu a mis à sec les eaux du Jourdain devant toi jusqu'à ce que tu aies traversé, comme Yahvé ton Dieu l'a fait pour la mer Rouge, qu'il a mise à sec devant nous jusqu'à ce que nous l'ayons traversée,
Gama Ubangiji Allahnku ya sa ruwan Urdun ya yanke a gabanku, har sai da kuka gama wucewa, kamar yadda ya yi a Jan Teku, a lokacin da ya busar da shi a gabanmu har sai da muka gama wucewa.
24 afin que tous les peuples de la terre sachent que la main de Yahvé est puissante, et que vous craigniez Yahvé votre Dieu pour toujours. »
Ya yi wannan ne domin dukan mutanen duniya su san cewa Ubangiji mai iko ne, domin kuma ku zama masu tsoron Ubangiji Allahnku.”

< Josué 4 >