< Josué 20 >

1 Yahvé parla à Josué, et dit:
Sai Ubangiji ya ce wa Yoshuwa,
2 Parle aux enfants d'Israël, et dis: « Attribuez les villes de refuge dont je vous ai parlé par Moïse,
“Ka gaya wa Isra’ilawa su keɓe waɗansu birane su zama biranen mafaka kamar yadda na umarce ku ta wurin Musa,
3 afin que le meurtrier qui tue quelqu'un par accident ou involontairement puisse s'y réfugier. Elles seront pour vous un refuge contre le vengeur du sang.
domin idan wani ya kashe wani bisa kuskure ba da niyyar yin kisankai ba, mutumin zai iya gudu zuwa can yă fake don kada a kashe shi.
4 Il s'enfuira dans l'une de ces villes, se tiendra à l'entrée de la porte de la ville et exposera son cas aux oreilles des anciens de cette ville. Ils le prendront avec eux dans la ville et lui donneront une place, afin qu'il vive au milieu d'eux.
Lokacin da ya gudu zuwa ɗaya daga cikin biranen nan, sai yă tsaya a ƙofar birnin yă gaya wa dattawan wannan birni damuwarsa. Sa’an nan su karɓe shi su ba shi wurin zama a cikin birninsu.
5 Si le vengeur du sang le poursuit, on ne livrera pas entre ses mains le meurtrier de l'homme, parce qu'il a frappé son prochain sans le vouloir et sans le haïr auparavant.
In mai neman yă kashe shi don ramako ya bi shi zuwa can, ba za su miƙa shi ba domin ba da niyya ya kashe wani ba, kuma ba fushi ne ya sa ya yi kisan ba.
6 Il demeurera dans cette ville jusqu'à ce qu'il se présente devant l'assemblée pour être jugé, jusqu'à la mort du grand prêtre qui aura lieu en ces jours-là. Alors l'homme qui a tué son prochain s'en retournera et reviendra dans sa ville et dans sa maison, dans la ville qu'il a fuie.'"
Zai zauna a wannan birni har sai taron jama’a sun yi masa shari’a, kuma har sai lokacin da babban firist wanda yake aiki a lokacin ya mutu, sa’an nan zai iya koma garinsa na dā.”
7 Ils mirent à part Kedesh en Galilée, dans la montagne de Nephtali, Sichem dans la montagne d'Ephraïm, et Kiriath Arba (appelée aussi Hébron) dans la montagne de Juda.
Saboda haka suka keɓe Kedesh a Galili a ƙasar kan tudu ta Naftali, Shekem a ƙasar kan tudu ta Efraim, da Kiriyat Arba (wato, Hebron) a ƙasar kan tudu ta Yahuda.
8 Au-delà du Jourdain, à Jéricho, vers l'est, ils attribuèrent Bezer dans le désert, dans la plaine, à la tribu de Ruben, Ramoth en Galaad, à la tribu de Gad, et Golan en Basan, à la tribu de Manassé.
A hayin Urdun, gabas da Yeriko, suka keɓe Bezer ta jeji a kan tudu a cikin yankin kabilar Ruben, Ramot cikin Gileyad a kabilar Gad, da Golan cikin Bashan a kabilar Manasse.
9 Ces villes étaient destinées à tous les enfants d'Israël et à l'étranger qui vit au milieu d'eux, afin que quiconque tuerait quelqu'un involontairement puisse s'y réfugier et ne pas mourir de la main du vengeur du sang, jusqu'à ce qu'il soit jugé devant l'assemblée.
In wani mutumin Isra’ila ko kuma wani baƙon da yake zama a cikinsu, ya yi kisankai cikin kuskure, zai iya gudu zuwa biranen da aka keɓe, ba za a bari mai neman ramako yă kashe shi kafin jama’a su yi masa shari’a ba.

< Josué 20 >