< Josué 17 >

1 Tel fut le sort de la tribu de Manassé, car il était le premier-né de Joseph. Quant à Makir, premier-né de Manassé, père de Galaad, car il était homme de guerre, il eut Galaad et Basan.
Wannan shi ne gādon da aka ba wa kabilar Manasse, a matsayin ɗan farin Yusuf. Manasse yana da ɗan farin mai suna Makir. Makir shi ne mahaifin mutanen Gileyad, aka ba shi Gileyad da Bashan gama Makiriyawa jarumai ne ƙwarai.
2 Ainsi en fut-il pour le reste des fils de Manassé, selon leurs familles: pour les fils d'Abiezer, pour les fils de Helek, pour les fils d'Asriel, pour les fils de Sichem, pour les fils de Hepher, et pour les fils de Shemida. Tels furent les fils mâles de Manassé, fils de Joseph, selon leurs familles.
Aka kuma raba wa sauran mutanen kabilar Manasse rabon gādonsu bisa ga iyalansu, wato, Abiyezer, Helek, Asriyel, Shekem, Hefer da Shemida. Waɗannan su ne’ya’yan Manasse, maza, ɗan Yusuf bisa ga iyalansu.
3 Mais Zelophehad, fils de Hépher, fils de Galaad, fils de Makir, fils de Manassé, n'eut pas de fils, mais des filles. Voici les noms de ses filles: Mahla, Noé, Hogla, Milca et Tirza.
Zelofehad kuwa ɗan Hefer, ɗan Gileyad, ɗan Makir, ɗan Manasse ba shi da’ya’ya maza, sai dai mata. Ga sunayensu, Mala, Nowa, Hogla, Milka da Tirza.
4 Elles se présentèrent au sacrificateur Éléazar, à Josué, fils de Nun, et aux princes, en disant: « L'Éternel a ordonné à Moïse de nous donner un héritage parmi nos frères. » C'est pourquoi, selon le commandement de Yahvé, il leur donna un héritage parmi les frères de leur père.
Suka je wurin Eleyazar firist, da Yoshuwa ɗan Nun, da kuma shugabannin, suka ce musu, “Ubangiji ya umarci Musa cewa yă ba mu gādonmu tare da’yan’uwanmu maza.” Saboda haka Yoshuwa ya ba su gādo tare da’yan’uwan mahaifinsu maza bisa ga umarnin Ubangiji.
5 Dix parts échurent à Manassé, en plus du pays de Galaad et de Basan, qui est au-delà du Jourdain,
Dalilin ke nan Manasse ya sami kashi goma ban da ƙasar Gileyad da Bashan a gabashin Urdun,
6 car les filles de Manassé avaient un héritage parmi ses fils. Le pays de Galaad appartenait au reste des fils de Manassé.
domin’ya’ya mata na kabilar Manasse sun sami gādo tare da’ya’ya maza. Aka ba wa sauran mutanen kabilar Manasse ƙasar Gileyad.
7 La frontière de Manassé allait d'Aser à Micmethath, qui est en face de Sichem. La limite passait à droite, vers les habitants de En Tappuach.
Iyakar ƙasar Manasse ta tashi daga Asher zuwa Mikmetat a gabashin Shekem. Iyakar kuma ta miƙe har zuwa kudu wadda ta ƙunshi mutanen da suke zaune a En Taffuwa.
8 Le pays de Tappuach appartenait à Manassé; mais Tappuach, sur la frontière de Manassé, appartenait aux fils d'Éphraïm.
(Manasse ne yake da ƙasar Taffuwa, amma garin Taffuwa kansa, a kan iyakar Manasse ta mutanen Efraim ce.)
9 La limite descendait jusqu'au torrent de Kana, au sud du torrent. Ces villes appartenaient à Éphraïm parmi les villes de Manassé. La limite de Manassé était au nord du torrent, et se terminait à la mer.
Sa’an nan iyakar ta ci gaba ta yi kudu zuwa Rafin Kana. Akwai garuruwan da suke kudancin rafin, waɗanda suke Efraim, ko da yake suna cikin yankin Manasse. Iyakar Manasse ta miƙe zuwa arewa ta bi gefen rafin ta kuma ƙarasa a Bahar Rum.
10 Au sud, elle appartenait à Éphraïm, au nord, à Manassé, et la mer était sa limite. Ils s'étendaient jusqu'à Aser au nord, et jusqu'à Issacar à l'est.
Ƙasar a wajen kudu ta Efraim ce, ta wajen arewa kuma ta Manasse ce. Bahar Rum ita ce iyakarsu. Asher yana wajen arewa, Issakar kuma a wajen gabas.
11 Manassé avait trois hauteurs dans Issachar, à Asher Beth Shean et ses villes, et Ibleam et ses villes, et les habitants de Dor et ses villes, et les habitants d'Endor et ses villes, et les habitants de Taanach et ses villes, et les habitants de Megiddo et ses villes.
A yanki tsakanin Issakar da Asher, Manasse yana da waɗannan wurare, Bet-Sheyan, Ibileyam da ƙauyukanta, da mazaunan Dor da ƙauyukanta, da mazaunan En Dor da ƙauyukanta, da mazaunan Ta’anak da ƙauyukanta, da mazaunan Megiddo da ƙauyukanta (Na uku cikin jerin shi ne Nafot).
12 Les enfants de Manassé ne purent pas chasser les habitants de ces villes, mais les Cananéens demeurèrent dans ce pays.
Duk da haka mutanen Manasse ba su iya mallakar garuruwan nan ba, domin Kan’aniyawa sun nace da zama a wannan yanki.
13 Lorsque les enfants d'Israël furent devenus forts, ils soumirent les Cananéens au travail forcé et ne les chassèrent pas complètement.
Da Isra’ilawa suka yi ƙarfi, sai suka sa Kan’aniyawa suka zama masu yin musu aiki, amma ba su iya korarsu duka ba.
14 Les fils de Joseph parlèrent à Josué et lui dirent: « Pourquoi m'as-tu donné en héritage un seul lot et une seule part, puisque nous sommes un peuple nombreux et que l'Éternel nous a bénis jusqu'ici? »
Mutanen Yusuf kuwa suka ce wa Yoshuwa, “Me ya sa ka ba mu rabon gādo ɗaya kawai? Ga shi muna da yawa kuma Ubangiji ya albarkace mu sosai.”
15 Josué leur dit: « Si vous êtes un peuple nombreux, montez dans la forêt et défrichez-vous là, dans le pays des Phéréziens et des Rephaïm, car la montagne d'Ephraïm est trop étroite pour vous. »
Yoshuwa ya ce musu, “In kuna da yawa sosai, in kuma ƙasar kan tudu ta Efraim ba ta ishe ku ba, sai ku je cikin jeji, ku nema wa kanku ƙasa a ƙasar Ferizziyawa da Refahiyawa.”
16 Les fils de Joseph dirent: « La montagne ne nous suffit pas. Tous les Cananéens qui habitent le pays de la vallée ont des chars de fer, tant ceux qui sont à Beth-Shean et dans ses villes que ceux qui sont dans la vallée de Jizréel. »
Mutanen Yusuf suka amsa suka ce, “Ƙasar kan tudu ba ta ishe mu ba, ga kuma Kan’aniyawan da suke zama a filin, da waɗanda suke Bet-Sheyan da ƙauyukanta, da waɗanda suke Kwarin Yezireyel, duk suna da keken yaƙin ƙarfe.”
17 Josué parla à la maison de Joseph, c'est-à-dire à Ephraïm et à Manassé, et dit: « Vous êtes un peuple nombreux, et vous avez une grande force. Vous n'aurez pas un seul lot,
Amma Yoshuwa ya ce wa mutanen Yusuf, wa Efraim da Manasse, “Kuna da yawa, kuna kuma da ƙarfi sosai. Ba wuri ɗaya kaɗai za ku samu gādo ba,
18 mais la montagne sera à vous. Même si c'est une forêt, vous l'abattrez, et son extrémité sera à vous, car vous chasserez les Cananéens, bien qu'ils aient des chars de fer et qu'ils soient puissants. »
amma har da ƙasar kan tudu ma, ko da yake jeji ne, ku je ku gyara shi, duk yă zama naku. Ko da yake Kan’aniyawa suna da kekunan yaƙi na ƙarfe, suna kuma da ƙarfi, duk da haka za ku kore su.”

< Josué 17 >