< Josué 13 >

1 Or Josué était vieux et avancé en âge. Yahvé lui dit: « Tu es vieux et avancé en âge, et il te reste encore beaucoup de terres à posséder.
Sa’ad da Yoshuwa ya tsufa, Ubangiji ya ce masa, “Ka tsufa ƙwarai, ga shi kuma akwai sauran ƙasa mai fāɗi da ba ku riga kun mallaka ba.
2 « Voici le pays qui subsiste encore: toutes les régions des Philistins et tous les Gueschuriens,
“Ga ƙasar da ta rage, “dukan yankunan Filistiyawa da na Geshurawa.
3 depuis le Schichhor, qui est en face de l'Égypte, jusqu'à la frontière d'Ékron au nord, qui est comptée comme Cananéenne, les cinq seigneurs des Philistins, les Gazites, les Asdodites, les Ashkelonites, les Gittites et les Ékronites, et aussi les Avvim,
Daga Kogin Shihor a gabashin Masar zuwa sashen Ekron a arewa, dukan wannan ƙasa ana lissafta ta a cikin ƙasar Kan’aniyawa, ko da yake tana a sashen da sarakuna biyar na Filistiyawa na Gaza, Ashdod, Ashkeloniyawa, Gat da Ekron; na Awwiyawa.
4 au sud; tout le pays des Cananéens, et Meara qui appartient aux Sidoniens, jusqu'à Aphek, jusqu'à la frontière des Amorrhéens;
Daga wajen kudu kuma, dukan ƙasar Kan’aniyawa ce. Iyakarta a arewa ta fara daga Ara ta Sidoniyawa har zuwa Afek, ta zarce har zuwa iyakar Amoriyawa;
5 le pays des Gébalites, et tout le Liban, vers le soleil levant, depuis Baal Gad au pied de la montagne de l'Hermon jusqu'à l'entrée de Hamath;
da ƙasar Gebaliyawa; da dukan Lebanon wajen gabas daga Ba’al-Gad a gindin Dutsen Hermon zuwa Lebo Hamat.
6 tous les habitants de la montagne, depuis le Liban jusqu'à Misrephoth Maïm, tous les Sidoniens. Je les chasserai de devant les enfants d'Israël. Tu le donneras en héritage à Israël, comme je te l'ai ordonné.
“Dukan mazauna kan yankunan tuddai daga Lebanon zuwa Misrefot Mayim, wato, dukan Sidoniyawa, ni da kaina zan kore su a gaban Isra’ilawa. Ka tabbata ka raba wa Isra’ilawa ƙasar ta zama gādonsu kamar yadda na umarce ka,
7 Maintenant, partagez donc ce pays en héritage entre les neuf tribus et la demi-tribu de Manassé. »
ka raba ta tă zama gādo wa kabilu tara da kuma rabin kabilar Manasse.”
8 Les Rubénites et les Gadites reçurent avec lui l'héritage que Moïse leur avait donné, au-delà du Jourdain, à l'orient, comme Moïse, serviteur de Yahvé, le leur avait donné:
Rabin kabilar Manasse, mutanen Ruben da mutanen Gad suka karɓi rabonsu na gādo wanda Musa ya ba su a gabashin Urdun. Abin da Musa bawan Ubangiji ya ba su ke nan.
9 depuis Aroër, qui est sur le bord du torrent de l'Arnon, et la ville qui est au milieu du torrent, et toute la plaine de Medeba jusqu'à Dibon;
Wannan ya tashi daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, ya kuma haɗa da ƙasar da take tudun Medeba har zuwa Dibon,
10 et toutes les villes de Sihon, roi des Amoréens, qui régnait à Hesbon, jusqu'à la frontière des enfants d'Ammon;
da dukan garuruwan Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulkin Heshbon, har zuwa iyakar Ammonawa.
11 Galaad, le territoire des Gueschuriens et des Maacathiens, toute la montagne de l'Hermon, tout Basan jusqu'à Salca,
Haɗe da Gileyad, inda mutanen Geshur da Ma’aka suke. Dukan Dutsen Hermon, da dukan Bashan har zuwa Saleka,
12 tout le royaume d'Og en Basan, qui régnait à Aschtaroth et à Édréi, le reste des Rephaïm, car Moïse les attaqua et les chassa.
wato, dukan masarautar Og a Bashan, wanda ya yi mulkin Ashtarot da Edireyi, yana cikin waɗanda suke na ƙarshe da ba a kashe ba a cikin Refahiyawa. Musa ya ci su da yaƙi, ya ƙwace ƙasarsu.
13 Cependant, les enfants d'Israël ne chassèrent pas les Gueshuriens et les Maacathiens; mais Gueshur et Maacath vivent en Israël jusqu'à ce jour.
Amma Isra’ilawa ba su kori mutanen Geshur da Ma’aka ba, saboda haka suka ci gaba da zama cikin Isra’ilawa har wa yau.
14 Seulement, il ne donna aucun héritage à la tribu de Lévi. Les offrandes de Yahvé, le Dieu d'Israël, faites par le feu, sont son héritage, comme il le lui a dit.
Kabilar Lawiyawa ne kaɗai Musa bai ba ta gādo ba, gama hadayun ƙonawa da ake miƙa wa Ubangiji, Allah na Isra’ila ne gādonsu, kamar yadda ya yi musu alkawari.
15 Moïse donna à la tribu des fils de Ruben, selon leurs familles.
Ga abin da Musa ya ba kabilar Ruben bisa ga iyalansu.
16 Leur territoire s'étendait depuis Aroër, qui est sur le bord du torrent de l'Arnon, et la ville qui est au milieu du torrent, et toute la plaine près de Medeba;
Abin da ya kama daga Arower a gefen kwarin Arnon, da kuma daga garin da yake tsakiyar kwarin, da dukan ƙasar tudu kusa da Medeba
17 Hesbon et toutes ses villes qui sont dans la plaine; Dibon, Bamoth Baal, Beth Baal Meon,
zuwa Heshbon, da dukan garuruwan kan tudu, haɗe da Dibon, Bamot Ba’al, Bet-Ba’al-Meyon,
18 Jahaz, Kedemoth, Mephaath,
Yahza, Kedemot, Mefa’at,
19 Kiriathaïm, Sibma, Zereth Schahar sur la montagne de la vallée,
Kiriyatayim, Sibma, Zeret Shahar kan tudu cikin kwari,
20 Beth Peor, les pentes du Pisga, Beth Jeshimoth,
Bet-Feyor, gangaren Fisga da Bet-Yeshimot,
21 toutes les villes de la plaine, et tout le royaume de Sihon, roi des Amoréens, qui régnait à Hesbon, et que Moïse frappa avec les chefs de Madian, Evi, Rékem, Tsur, Hur et Réba, princes de Sihon, qui habitaient le pays.
dukan garuruwan da suke kan tudu da dukan masarautar Sihon sarkin Amoriyawa, wanda ya yi mulki a Heshbon. Musa ya yi nasara da shi, da shugabannin Midiyawa, wato, Ewi, Rekem, Zur, Hur, da Reba, sarakunan Sihon, waɗanda suka zauna a ƙasar.
22 Les enfants d'Israël tuèrent aussi par l'épée Balaam, fils de Beor, le devin, parmi le reste de leurs morts.
Ƙari a kan waɗanda aka kashe a yaƙi, Isra’ilawa suka kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi don yana duba.
23 La limite des fils de Ruben était la rive du Jourdain. Tel fut l'héritage des fils de Ruben, selon leurs familles, les villes et leurs villages.
Gefen Urdun shi ne iyakar mutanen Ruben. Waɗannan garuruwa da ƙauyukansu su ne gādon mutanen Ruben, bisa ga iyalansu.
24 Moïse donna à la tribu de Gad, aux fils de Gad, selon leurs familles.
Ga abin da Musa ya ba kabilar Gad, bisa ga iyalansu.
25 Leur limite était Jaezer, toutes les villes de Galaad et la moitié du pays des enfants d'Ammon, jusqu'à Arœr, près de Rabba;
Yankin ƙasarsu ya ƙunshi Yazer, da dukan garuruwan Gileyad, da rabin ƙasar Ammonawa har zuwa Arower kusa da Rabba,
26 depuis Hesbon, jusqu'à Ramath Mitspé, et Bétonim; depuis Mahanaïm, jusqu'à la frontière de Debir;
da kuma daga Heshbon zuwa Ramat Mizfa da Betonim, da kuma daga Mahanayim zuwa sashen Debir,
27 et dans la vallée, Beth Haram, Beth Nimrah, Succoth et Zaphon, le reste du royaume de Sihon, roi de Hesbon, la rive du Jourdain, jusqu'à l'extrémité de la mer de Chinnereth, au-delà du Jourdain, à l'est.
kuma a cikin kwari, Bet-Haram, Bet-Nimra, Sukkot da Zafon da kuma sauran masarautar Sihon sarkin Heshbon (gabashin Urdun, abin da ya kama har zuwa ƙarshen Tekun Kinneret).
28 Tel est l'héritage des fils de Gad, selon leurs familles, les villes et leurs villages.
Waɗannan garuruwan da ƙauyukansu duka, gādon mutanen Gad ne, bisa ga iyalansu.
29 Moïse donna un héritage à la demi-tribu de Manassé. C'était pour la demi-tribu des fils de Manassé, selon leurs familles.
Ga abin da Musa ya ba rabin kabilar Manasse, wato, wa rabin zuriyar Manasse, bisa ga iyalansu.
30 Leur territoire s'étendait depuis Mahanaïm, tout Basan, tout le royaume d'Og, roi de Basan, et tous les villages de Jaïr, qui sont en Basan, soit soixante villes.
Abin da ya miƙe daga Mahanayim haɗe da dukan Bashan, da gefen masarautar Og sarkin Bashan, da dukan garuruwan Yayir guda sittin da suke a Bashan,
31 La moitié de Galaad, Aschtaroth et Édréi, villes du royaume d'Og en Basan, étaient pour les fils de Makir, fils de Manassé, pour la moitié des fils de Makir, selon leurs familles.
da rabin Gileyad, da Ashtarot, Edireyi (biranen sarki Og a Bashan). Wannan shi ne rabon da zuriyar Makir ɗan Manasse suka samu, domin rabin’ya’yan Makir maza, bisa ga iyalansu.
32 Tels sont les héritages que Moïse distribua dans les plaines de Moab, au-delà du Jourdain, à Jéricho, vers l'est.
Waɗannan su ne rabon gādon da Musa ya yi lokacin da suke cikin filayen Mowab a hayin gabashin Urdun kusa da Yeriko.
33 Mais Moïse n'a pas donné d'héritage à la tribu de Lévi. Yahvé, le Dieu d'Israël, est leur héritage, comme il le leur a dit.
Amma Musa bai ba kabilar Lawiyawa gādo ba; Ubangiji, Allah na Isra’ila, shi ne gādonsu kamar yadda ya yi musu alkawari.

< Josué 13 >