< Jonas 4 >

1 Mais cela déplut fortement à Jonas, qui se mit en colère.
Sai abin ya ɓata wa Yunana rai ƙwarai har ya yi fushi.
2 Il pria Yahvé et dit: « Je t'en prie, Yahvé, n'est-ce pas ce que j'ai dit quand j'étais encore dans mon pays? C'est pourquoi je me suis hâté de fuir à Tarsis, car je savais que tu es un Dieu miséricordieux et compatissant, lent à la colère et riche en bonté, et que tu ne fais pas de mal.
Sai ya yi addu’a ga Ubangiji ya ce, “Ya Ubangiji, ba irin abin da na faɗa ke nan ba tun ina gida? Wannan ne ya sa na yi ƙoƙarin tserewa zuwa Tarshish. Ai, na sani kai Allah ne mai alheri da tausayi, mai jinkirin fushi da cikakkiyar ƙauna, kai Allah ne mai dakatar da nufinka na yin hukunci.
3 C'est pourquoi maintenant, Yahvé, enlève-moi la vie, je t'en supplie, car il vaut mieux pour moi mourir que vivre. »
Yanzu, ya Ubangiji, ka ɗauki raina, domin ya fi sauƙi a gare ni in mutu da in rayu.”
4 Yahvé dit: « Est-ce que tu as raison de te mettre en colère? »
Amma Ubangiji ya amsa, ya ce; “Daidai ne ka yi fushi?”
5 Alors Jonas sortit de la ville et s'assit à l'est de la ville; il se fit une tente et s'assit dessous à l'ombre, jusqu'à ce qu'il puisse voir ce qu'il adviendrait de la ville.
Sai Yunana ya fita daga birnin ya yi wajen gabas, ya zauna. A nan ya yi wa kansa rumfa, ya zauna cikin inuwarta yana jira yă ga abin da zai sami birnin.
6 Yahvé Dieu prépara une vigne et la fit monter au-dessus de Jonas, afin qu'elle soit un ombrage sur sa tête et le délivre de son malaise. Et Jonas se réjouit beaucoup à cause de la vigne.
Sai Ubangiji Allah ya sa wata’yar kuringa ta tsiro, ta yi girma a inda Yunana yake, don ta inuwantar da shi, yă ji daɗi. Yunana kuwa ya yi murna matuƙa da wannan kuringa.
7 Mais le lendemain, à l'aube, Dieu prépara un ver qui rongea la vigne et la fit se dessécher.
Amma kashegari da safe sai Allah ya sa tsutsa ta cinye’yar kuringar har ta mutu.
8 Lorsque le soleil se leva, Dieu prépara un vent d'est très fort, et le soleil frappa la tête de Jonas, qui se sentit faible et demanda à mourir. Il dit: « Il vaut mieux pour moi mourir que vivre. »
Sa’ad da rana ta yi sama, sai Allah ya sa iskar gabas mai zafi ta huro, zafin ranar kuma ya buga kan Yunana, har ya ji sai ka ce zai suma. Ya so a ce ya mutu ma, sai ya ce, “Gara in mutu da a ce ina zaune da rai.”
9 Dieu dit à Jonas: « Est-ce bien que tu sois en colère contre la vigne? » Il a dit: « J'ai le droit d'être en colère, même jusqu'à la mort. »
Amma Allah ya ce wa Yunana, “Daidai ne ka yi fushi saboda wannan kuringa?” Sai Yunana ya ce, “I, daidai ne, ina fushi matuƙa, har ina so da na mutu ma.”
10 L'Éternel dit: « Tu t'es préoccupé de la vigne, pour laquelle tu n'as pas travaillé et que tu n'as pas fait croître, qui est montée en une nuit et qui a péri en une nuit.
Sai Ubangiji ya ce, “Ai, wannan kuringa ta tsira dare ɗaya ta kuma ɓace kafin dare na biyu, ba ka yi wata wahala dominta ba, ba kai ne ka sa ta yi girma ba, duk da haka ranka ya ɓace saboda ita.
11 Nedevrais-je pas m'inquiéter de Ninive, cette grande ville, dans laquelle il y a plus de cent vingt mille personnes qui ne savent pas distinguer leur main droite de leur main gauche, et aussi beaucoup d'animaux? ».
Ashe, ba dole ne in ji tausayin babban birnin nan Ninebe mai mutum sama da dubu ɗari da ashirin marasa alhaki, da kuma dabbobi masu yawa ba?”

< Jonas 4 >