< Jonas 1 >

1 Or la parole de Yahvé fut adressée à Jonas, fils d'Amittaï, en ces termes:
Maganar Ubangiji ta zo wa Yunana ɗan Amittai cewa,
2 « Lève-toi, va à Ninive, la grande ville, et prêche contre elle, car leur méchanceté est montée devant moi. »
“Tafi babban birnin nan Ninebe ka yi mata wa’azi, saboda muguntarta ta haura zuwa gabana.”
3 Mais Jonas se leva pour fuir vers Tarsis, loin de la présence de Yahvé. Il descendit à Joppé, et trouva un navire qui allait à Tarsis; il paya le prix du navire, et y descendit, pour aller avec eux à Tarsis, loin de la présence de Yahvé.
Amma Yunana ya gudu daga Ubangiji ya nufi Tarshish. Ya gangara zuwa Yaffa, inda ya sami jirgin ruwa mai shirin tashi daga tashar. Bayan ya biya kuɗin tafiya, sai ya shiga jirgi ya kama hanya zuwa Tarshish don yă tsere wa Ubangiji.
4 Mais Yahvé fit souffler un grand vent sur la mer, et il y eut une grande tempête sur la mer, de sorte que le navire risquait de se briser.
Sai Ubangiji ya aika da babban iska a bisan teku, hadiri ya tsananta ƙwarai har jirgin ya yi barazanar farfashewa.
5 Alors les marins eurent peur, et chacun cria à son dieu. Ils jetèrent à la mer la cargaison qui se trouvait dans le navire pour alléger le navire. Mais Jonas était descendu dans les profondeurs du navire, il était couché et dormait profondément.
Dukan matuƙan jirgin suka tsorata, kowannensu kuma ya yi kuka ga allahnsa, suka kuma jefar da kayan jirgi a cikin teku domin su rage nauyin jirgin. Ana cikin haka, ashe, Yunana ya sauka can ƙarƙashin jirgi ya je ya kwanta, yana ta sharar barcinsa.
6 Alors le capitaine du navire s'approcha de lui et lui dit: « Que veux-tu dire, dormeur? Lève-toi, invoque ton Dieu! Peut-être ton Dieu nous remarquera-t-il, afin que nous ne périssions pas. »
Sai kyaftin ɗin ya je wajensa ya ce masa, “Don me kake barci? Tashi ka kira bisa ga allahnka! Mai yiwuwa yă ji mu, yă cece mu don kada mu hallaka.”
7 Ils se dirent tous les uns aux autres: « Venez! Tirons au sort, afin de savoir qui est responsable de ce mal qui nous frappe. » Ils tirèrent donc au sort, et le sort tomba sur Jonas.
Matuƙan jirgin suka ce wa juna, “Ku zo, mu jefa ƙuri’a mu ga wa ke da alhakin wannan masifa.” Sai suka jefa ƙuri’a, ƙuri’ar kuwa ta fāɗa a kan Yunana.
8 Ils lui demandèrent alors: « Dis-nous, je t'en prie, à cause de qui ce malheur est sur nous. Quelle est ta profession? D'où viens-tu? Quel est ton pays? De quel peuple es-tu? »
Saboda haka suka tambaye shi suka ce, “Yanzu, gaya mana, dalilin da ya sa wannan masifa ta zo mana? Mene ne aikinka? Daga ina ka fito? Ina ne ƙasarka? Daga wacce kabila ce ka fito?”
9 Il leur dit: « Je suis hébreu et je crains Yahvé, le Dieu des cieux, qui a fait la mer et la terre sèche. »
Sai ya amsa, “Ni mutumin Ibraniyawa ne, ina kuma bauta wa Ubangiji Allah na sama, wanda ya yi teku da tuddai.”
10 Alors les hommes eurent une grande peur et lui dirent: « Qu'as-tu fait? » Car les hommes savaient qu'il fuyait la présence de Yahvé, parce qu'il le leur avait dit.
Sai matuƙan jirgin suka tsorata ƙwarai, suka ce masa, “Wane irin mugun abu ne ka aikata haka?” (Sun gane cewa yana gudu ne daga wurin Ubangiji, domin ya riga ya faɗa musu.)
11 Et ils lui dirent: « Que te ferons-nous, pour que la mer se calme à nos yeux? » Car la mer devenait de plus en plus houleuse.
Sai tekun ya daɗa rikicewa. Sai suka tambaye shi, “Me za mu yi da kai domin tekun yă daina hauka?”
12 Il leur dit: « Prenez-moi, et jetez-moi dans la mer. Alors la mer se calmera pour vous, car je sais que c'est à cause de moi que cette grande tempête est sur vous. »
Ya amsa musu ya ce, “Ku ɗauke ni ku jefa a cikin teku, tekun zai kwanta. Na san cewa laifina ne ya jawo wannan babban hadirin da ya auka muku.”
13 Les hommes ramaient avec force pour les ramener à terre, mais ils ne pouvaient pas, car la mer devenait de plus en plus agitée contre eux.
Maimakon mutanen su yi haka, sai suka yi ƙoƙari su tura jirgin ruwan zuwa bakin teku. Amma ba su iya ba, saboda iskar ta sa tekun ya yi ta ƙara hauka.
14 Alors ils crièrent à Yahvé et dirent: « Nous te supplions, Yahvé, nous te supplions de ne pas nous laisser mourir pour la vie de cet homme, et de ne pas faire retomber sur nous le sang innocent; car toi, Yahvé, tu as fait ce qui t'a plu. »
Sai suka yi kuka ga Ubangiji suka ce, “Ya Ubangiji, in ka yarda kada ka bar mu mu mutu saboda ran mutumin nan. Kada ka yi mana hukuncin masu kisankai, gama kai ne, ya Ubangiji, ka ga ya gamshe ka.”
15 Ils prirent donc Jonas et le jetèrent dans la mer, et la mer cessa de se déchaîner.
Sa’an nan suka ɗauki Yunana suka jefar da shi daga jirgin, sai tekun ya kwanta.
16 Les hommes eurent une grande crainte de l'Éternel, et ils offrirent un sacrifice à l'Éternel et firent des vœux.
Ganin haka sai mutanen suka cika da tsoron Ubangiji, suka kuma miƙa wa Ubangiji hadaya, suka yi wa’adi da shi.
17 Yahvé prépara un énorme poisson pour engloutir Jonas, et Jonas resta dans le ventre du poisson trois jours et trois nuits.
Amma Ubangiji ya tanada wani babban kifi da zai haɗiye Yunana, Yunana kuwa ya yi yini uku da dare uku a ciki cikin kifin.

< Jonas 1 >