< Jean 4 >

1 Le Seigneur, sachant que les pharisiens avaient appris que Jésus faisait et baptisait plus de disciples que Jean
Yesu ya ji labari cewa Yahudawa sun ji cewa ya wuce Yohanna samun masu bi, yana kuma yin musu baftisma,
2 (bien que Jésus lui-même ne baptisât pas, mais ses disciples),
ko da yake ba Yesu ne yake baftismar ba, almajiransa ne.
3 quitta la Judée et se rendit en Galilée.
Da ya sami wannan labari, sai ya bar Yahudiya ya sāke koma Galili.
4 Il lui fallait passer par la Samarie.
To, ya zama dole yă bi ta Samariya.
5 Il arriva donc dans une ville de Samarie appelée Sychar, près de la parcelle de terre que Jacob avait donnée à son fils Joseph.
Sai ya zo wani gari a Samariya da ake ce da shi Saikar, kurkusa da filin da Yaƙub ya ba wa ɗansa Yusuf.
6 Le puits de Jacob était là. Jésus, fatigué de son voyage, s'assit donc près du puits. C'était environ la sixième heure.
Rijiyar Yaƙub kuwa tana can, Yesu kuwa, saboda gajiyar tafiya, sai ya zauna a bakin rijiyar. Wajen sa’a ta shida ne.
7 Une femme de Samarie vint puiser de l'eau. Jésus lui dit: « Donne-moi à boire. »
Sa’ad da wata mutuniyar Samariya ta zo ɗiban ruwa, sai Yesu ya ce mata, “Ba ni ruwa in sha?”
8 Car ses disciples étaient partis à la ville pour acheter des vivres.
(Almajiransa kuwa sun shiga gari don sayi abinci.)
9 La Samaritaine lui dit donc: « Comment se fait-il que toi, qui es Juif, tu demandes à boire à moi, une Samaritaine? ». (Car les Juifs n'ont pas affaire aux Samaritains).
Sai mutuniyar Samariyar ta ce masa, “Kai mutumin Yahuda ne, ni kuwa mutuniyar Samariya ce. Yaya za ka roƙe ni ruwan sha?” (Don Yahudawa ba sa hulɗa da Samariyawa.)
10 Jésus lui répondit: « Si tu savais quel est le don de Dieu, et qui est celui qui te dit: « Donne-moi à boire », tu lui aurais demandé, et il t'aurait donné de l'eau vive. »
Yesu ya amsa mata ya ce, “Da kin san kyautar Allah, da kuma wanda yake roƙonki ruwan sha, da kin roƙe shi, shi kuwa da ya ba ki ruwan rai.”
11 La femme lui dit: « Monsieur, vous n'avez rien pour puiser, et le puits est profond. Où vas-tu puiser cette eau vive?
Sai macen ta ce, “Ranka yă daɗe, ba ka da guga rijiyar kuwa tana da zurfi. Ina za ka sami wannan ruwan rai?
12 Es-tu plus grand que notre père Jacob, qui nous a donné le puits et y a bu lui-même, ainsi que ses enfants et son bétail? »
Ka fi mahaifinmu Yaƙub ne, wanda ya ba mu rijiyar ya kuma sha daga ciki da kansa, haka ma’ya’yansa da kuma garkunan shanunsa da tumakinsa?”
13 Jésus lui répondit: « Quiconque boit de cette eau aura encore soif,
Yesu ya amsa ya ce, “Kowa ya sha wannan ruwa, zai sāke jin ƙishirwa,
14 mais celui qui boira de l'eau que je lui donnerai n'aura plus jamais soif; l'eau que je lui donnerai deviendra en lui une source d'eau jaillissant en vie éternelle. » (aiōn g165, aiōnios g166)
amma duk wanda ya sha ruwan da zan ba shi, ba zai ƙara jin ƙishirwa ba. Tabbatacce, ruwan da zan ba shi, zai zama masa maɓuɓɓugan ruwa da yake ɓuɓɓugowa har yă zuwa rai madawwami.” (aiōn g165, aiōnios g166)
15 La femme lui dit: « Seigneur, donne-moi cette eau, afin que je n'aie pas soif et que je ne vienne pas jusqu'ici pour puiser. »
Sai macen ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ka ba ni ruwan nan, don kada in ƙara jin ƙishirwa, in yi ta zuwa nan ɗiban ruwa.”
16 Jésus lui dit: « Va, appelle ton mari, et viens ici. »
Sai ya ce mata, “Je ki zo da mijinki.”
17 La femme répondit: « Je n'ai pas de mari. » Jésus lui dit: « Tu as bien dit: « Je n'ai pas de mari »,
Sai ta amsa ta ce, “Ai, ba ni da miji.” Yesu ya ce mata, “Gaskiyarki da kika ce ba ki da miji.
18 car tu as eu cinq maris, et celui que tu as maintenant n'est pas ton mari. Tu l'as dit en vérité. »
Gaskiyar ita ce, kin auri maza biyar, wanda kuke tare yanzu kuwa ba mijinki ba ne. A nan kam kin yi gaskiya.”
19 La femme lui dit: « Monsieur, je vois que vous êtes un prophète.
Sai macen ta ce, “Ranka yă daɗe, ina gani kai annabi ne.
20 Nos pères se sont prosternés sur cette montagne, et vous, les Juifs, vous dites que le lieu où l'on doit se prosterner est à Jérusalem. »
Kakanninmu sun yi sujada a dutsen nan, amma ku Yahudawa kun ce a Urushalima ne ya kamata a yi sujada.”
21 Jésus lui dit: « Femme, crois-moi, l'heure vient où ce n'est ni sur cette montagne ni à Jérusalem que vous adorerez le Père.
Sai Yesu ya ce, “Uwargida, ina tabbatar miki, lokaci yana zuwa da ba za ku yi wa Uba sujada ko a dutsen nan, ko kuwa a Urushalima ba.
22 Vous adorez ce que vous ne connaissez pas. Nous adorons ce que nous connaissons, car le salut vient des Juifs.
Ku Samariyawa ba ku san abin da kuke yi wa sujada ba; mu kuwa mun san abin da muke yi wa sujada, gama ceto daga Yahudawa yake.
23 Mais l'heure vient, et c'est maintenant, où les vrais adorateurs adoreront le Père en esprit et en vérité, car le Père cherche de tels adorateurs.
Duk da haka, lokaci yana zuwa har ma ya riga ya yi, da masu sujada na gaskiya za su yi wa Uba sujada a Ruhu da kuma gaskiya, gama irin waɗannan masu sujada ne Uba yake nema.
24 Dieu est esprit, et ceux qui l'adorent doivent adorer en esprit et en vérité. »
Allah ruhu ne, masu yi masa sujada kuwa dole su yi masa sujada a ruhu, da gaskiya kuma.”
25 La femme lui dit: « Je sais que le Messie va venir, celui qu'on appelle Christ. Quand il sera venu, il nous annoncera toutes choses. »
Macen ta ce, “Na san cewa Almasihu” (da ake ce da shi Kiristi) “yana zuwa. Sa’ad da ya zo kuwa, zai bayyana mana kome.”
26 Jésus lui dit: « C'est moi, celui qui te parle. »
Sai Yesu ya ce, “Ni mai maganan nan da ke, Ni ne shi.”
27 A l'instant même, ses disciples arrivèrent. Ils s'étonnaient de ce qu'il parlait à une femme; pourtant, personne ne disait: « Que cherchez-vous? » ou « Pourquoi parlez-vous avec elle? »
Suna gama magana ke nan sai almajiransa suka iso, suka yi mamakin ganin yana magana da mace. Amma ba wanda ya ce, “Me kake so?” Ko “Me ya sa kake magana da ita?”
28 La femme laissa donc son pot à eau, s'en alla dans la ville et dit aux gens:
Sai macen ta bar tulunta na ruwa, ta koma cikin gari ta ce wa mutane,
29 « Venez voir un homme qui m'a raconté tout ce que j'ai fait. Est-ce là le Christ? »
“Ku zo, ku ga mutumin da ya gaya mini duk abin da na taɓa yi. Shin, ko shi ne Kiristi?”
30 Ils sortirent de la ville, et s'approchèrent de lui.
Sai suka fita daga garin suka nufa inda yake.
31 Pendant ce temps, les disciples le pressaient en disant: « Rabbi, mange. »
Ana cikin haka, sai almajiransa suka roƙe shi suka ce, “Rabbi, ci abinci mana.”
32 Mais il leur dit: « J'ai un repas à manger que vous ne connaissez pas. »
Amma ya ce musu, “Ina da abincin da ba ku san kome a kai ba.”
33 Les disciples se dirent donc les uns aux autres: « Quelqu'un lui a-t-il apporté quelque chose à manger? »
Sai almajiran suka ce wa juna, “Shin, ko wani ya kawo masa abinci ne?”
34 Jésus leur dit: « Ma nourriture est de faire la volonté de celui qui m'a envoyé et d'accomplir son œuvre.
Yesu ya ce, “Abincina shi ne, in aikata nufin wannan da ya aiko ni, in kuma gama aikinsa.
35 Ne dites-vous pas: « Il y a encore quatre mois avant la moisson? Voici, je vous le dis, levez les yeux et regardez les champs: ils sont déjà blancs pour la moisson.
Ba kukan ce, ‘Sauran wata huɗu a yi girbi ba?’ Ina gaya muku, ku ɗaga idanu ku dubi gonaki! Sun isa girbi.
36 Celui qui moissonne reçoit un salaire et recueille du fruit pour la vie éternelle, afin que celui qui sème et celui qui moissonne se réjouissent ensemble. (aiōnios g166)
Mai girbi na samun lada, yana kuma tara amfani zuwa rai madawwami, domin mai shuka da mai girbi su yi farin ciki tare. (aiōnios g166)
37 Car cette parole est vraie: « L'un sème, l'autre moissonne ».
Karin maganan nan gaskiya ne cewa, ‘Wani da shuka, wani kuma da girbi.’
38 Je vous ai envoyés pour moissonner ce que vous n'avez pas travaillé. D'autres ont travaillé, et vous avez participé à leur travail. »
Na aike ku girbin abin da ba ku yi aikinsa ba. Waɗansu sun yi aikin nan mai wahala, ku kuwa kun sami ladan aikinsu.”
39 De cette ville, beaucoup de Samaritains crurent en lui, à cause de la parole de la femme, qui témoigne:" Il m'a dit tout ce que j'ai fait. »
Samariyawa da yawa daga wannan gari suka gaskata da shi saboda shaidar macen da ta ce, “Ya gaya mini duk abin da na taɓa yi.”
40 Les Samaritains vinrent donc le trouver et le prièrent de rester avec eux. Il resta là deux jours.
To, da Samariyawa suka zo wurinsa, sai suka roƙe shi yă zauna da su, ya kuwa zauna kwana biyu.
41 Beaucoup d'autres crurent à cause de sa parole.
Saboda kalmominsa kuwa da yawa suka gaskata.
42 Ils dirent à la femme: « Maintenant, nous croyons, non pas à cause de ce que tu as dit, mais parce que nous l'avons entendu nous-mêmes, et nous savons que c'est vraiment le Christ, le Sauveur du monde. »
Sai suka ce wa macen, “Yanzu kam mun gaskata, ba don abin da kika faɗa kawai ba; yanzu mun ji da kanmu, mun kuwa san cewa wannan mutum tabbatacce shi ne Mai Ceton duniya.”
43 Après ces deux jours, il partit de là et se rendit en Galilée.
Bayan kwana biyun nan sai ya bar can zuwa Galili.
44 Car Jésus lui-même a témoigné qu'un prophète n'a pas d'honneur dans sa propre patrie.
(To, Yesu kansa ya taɓa faɗa cewa annabi ba shi da daraja a ƙasarsa.)
45 Lorsqu'il arriva en Galilée, les Galiléens le reçurent, après avoir vu tout ce qu'il faisait à Jérusalem pendant la fête, car eux aussi allaient à la fête.
Da ya isa Galili, sai mutanen Galili suka marabce shi. Sun ga duk abin da ya yi a Urushalima a lokacin Bikin Ƙetarewa, gama su ma sun kasance a can.
46 Jésus revient donc à Cana de Galilée, où il changea l'eau en vin. Il y avait à Capharnaüm un officer du roi dont le fils était malade.
Sai ya sāke ziyarci Kana ta Galili inda ya juya ruwa ya zama ruwan inabi. Akwai wani ma’aikacin hukuma a can wanda ɗansa yake kwance da rashin lafiya a Kafarnahum.
47 Ayant appris que Jésus était passé de la Judée à la Galilée, il alla le trouver et le pria de descendre et de guérir son fils, car il était à l'article de la mort.
Da mutumin nan ya ji cewa Yesu ya isa Galili daga Yahudiya, sai ya je wurinsa ya roƙe shi yă zo yă warkar da ɗansa da yake bakin mutuwa.
48 Jésus lui dit alors: « Si vous ne voyez des signes et des prodiges, vous ne croirez en aucune façon. »
Yesu ya ce masa, “Ku mutane, in ba kun ga alamu da abubuwan banmamaki ba, ba yadda za a yi ku ba da gaskiya.”
49 Le noble lui dit: « Monsieur, descendez avant que mon enfant ne meure. »
Ma’aikacin hukuman ya ce, “Ranka yă daɗe, ka zo kafin ɗana yă mutu.”
50 Jésus lui dit: « Va-t'en. Ton fils est vivant. » L'homme crut à la parole que Jésus lui avait dite, et il s'en alla.
Sai Yesu ya amsa ya ce, “Ka tafi. Ɗanka zai rayu.” Mutumin kuwa ya amince da maganar da Yesu ya yi ya kuwa tafi.
51 Comme il descendait, ses serviteurs vinrent à sa rencontre et lui rapportèrent: « Ton enfant vit! »
Tun yana kan hanya, bayinsa suka tarye shi da labari cewa yaron yana warkewa.
52 Il s'enquit donc auprès d'eux de l'heure à laquelle il commença à aller mieux. Ils lui dirent donc: « Hier, à la septième heure, la fièvre l'a quitté. »
Da ya tambayi lokacin da ɗansa ya sami sauƙi, sai suka ce masa, “Zazzaɓin ya sake shi jiya a sa’a ta bakwai.”
53 Le père sut donc que c'était à cette heure-là que Jésus lui avait dit: « Ton fils vit. » Il crut, ainsi que toute sa maison.
Sai mahaifin ya gane a daidai wannan lokaci ne Yesu ya ce masa, “Ɗanka zai rayu.” Saboda haka shi da dukan iyalinsa suka gaskata.
54 Voici encore le second signe que fit Jésus, après être passé de la Judée en Galilée.
Wannan ce abin banmamaki ta biyu da Yesu ya yi, bayan zuwansa daga Yahudiya zuwa Galili.

< Jean 4 >