< Joël 3 >

1 « Car voici, en ces jours-là, et pendant ce temps, quand je restaurerai la fortune de Juda et de Jérusalem,
“A waɗancan kwanaki da kuma a wancan lokaci, sa’ad da zan maido da arzikin Yahuda da Urushalima,
2 Je rassemblerai toutes les nations, et les fera descendre dans la vallée de Josaphat; et je les jugerai là-bas, pour mon peuple, et pour mon héritage, Israël, qu'ils ont dispersé parmi les nations. Ils ont divisé mes terres,
zan tattara dukan al’ummai in kuma kawo su Kwarin Yehoshafat Can zan yi musu shari’a game da gādona, mutanena Isra’ila, gama sun warwatsar da mutanena a cikin al’ummai sun kuma raba ƙasata.
3 et j'ai tiré au sort mon peuple, et ont donné un garçon pour une prostituée, et vendu une fille pour du vin, afin qu'ils puissent boire.
Sun jefa ƙuri’a a kan mutanena suna kuma sayar da yara maza don karuwanci, sun sayar da’yan matan domin ruwan inabi wanda za su sha.
4 « Oui, et qu'êtes-vous pour moi, Tyr et Sidon, et toutes les régions de la Philistie? Vous me rembourserez? Et si vous me remboursez, Je vous renverrai rapidement et promptement votre remboursement sur votre propre tête.
“Yanzu mene ne damuwarku da ni, ya Taya da Sidon da kuma dukan mazaunan yankunan Filistiya? Kuna ƙoƙari ku sāka mini don abin da na yi ne? In kuna sāka mini ne, to, da gaggawa zan mayar muku da sakayya a kanku.
5 Parce que tu as pris mon argent et mon or, et ont transporté mes plus beaux trésors dans vos temples,
Gama kun kwashe azurfata da zinariyata kun kuma washe dukiyata mafi kyau kun kai cikin haikalinku.
6 et ils ont vendu les enfants de Juda et les enfants de Jérusalem aux fils des Grecs, afin que tu les éloignes de leur frontière.
Kun sayar da mutanen Yahuda da na Urushalima ga mutanen Hellenawa, don ku aika da su nesa da ƙasarsu.
7 Voici, je vais les faire sortir du lieu où vous les avez vendus, et vous rendrez votre remboursement sur votre propre tête;
“Duba, zan dawo da su daga wuraren da kuka sayar da su, in kuma yi muku abin da kuka yi musu.
8 et je vendrai tes fils et tes filles entre les mains des enfants de Juda, et ils les vendront aux hommes de Saba, à une nation lointaine, car Yahvé l'a dit. »
Zan sayar da’ya’yanku maza da mata ga mutanen Yahuda, su kuma za su sayar da su ga mutanen Sabenawa, al’umma da take nesa da ku.” Ubangiji ya faɗa.
9 Proclamez ceci parmi les nations: « Préparez-vous à la guerre! Réveillez les hommes forts. Que tous les guerriers s'approchent. Laissez-les monter.
Ku yi shelar wannan ga al’ummai. Ku yi shirin yaƙi! Ku tā da jarumawa! Bari mayaƙa su ja kusa su kai hari.
10 Transformez vos socs en épées, et vos crochets d'élagage en lances. Que le faible dise: « Je suis fort.
Ku bubbuge garemaninku su zama takuba da kuma laujenku su zama māsu. Bari raunana su ce, “Ni mai ƙarfi ne!”
11 Dépêchez-vous et venez, vous toutes les nations environnantes, et rassemblez-vous. » Fais descendre tes puissants, Yahvé.
Ku gaggauta, dukanku al’ummai daga kowane ɓangare, ku tattaru a can. Ka sauko da mayaƙanka, ya Ubangiji!
12 « Que les nations se réveillent! et de monter dans la vallée de Josaphat; car c'est là que je m'assiérai pour juger toutes les nations environnantes.
“Bari a tā da dukan al’ummai; bari su kutsa zuwa Kwarin Yehoshafat gama a can zan zauna in shari’anta dukan al’ummai daga kowane ɓangare.
13 Mettez la faucille; car la récolte est mûre. Venez, foulez, car le pressoir est plein, les cuves débordent, car leur méchanceté est grande. »
Ku fito da lauje, gama girbi ya nuna. Ku zo, ku tattaka inabin, gama wurin matsewar ruwan inabi ya cika randunan tarawa kuma sun cika har suna zuba, muguntarsu da girma take!”
14 Des multitudes, des multitudes dans la vallée de la décision! Car le jour de Yahvé est proche dans la vallée de la décision.
Dubun dubbai suna a cikin kwarin yanke shawara! Gama ranar Ubangiji ta yi kusa a cikin kwarin yanke shawara.
15 Le soleil et la lune sont obscurcis, et les étoiles retirent leur éclat.
Za a duhunta rana da wata, taurari kuma ba za su ba da haske ba.
16 De Sion, Yahvé rugira, et le tonnerre de Jérusalem; et les cieux et la terre trembleront; mais Yahvé sera un refuge pour son peuple, et une forteresse pour les enfants d'Israël.
Ubangiji zai yi ruri daga Sihiyona tsawa kuma daga Urushalima; duniya da sararin sama za su yi rawan jiki. Amma Ubangiji zai zama mafakar mutanensa, mafaka ga mutanensa Isra’ila.
17 « Ainsi, vous saurez que je suis Yahvé, votre Dieu, qui habite à Sion, ma montagne sainte. Alors Jérusalem sera sainte, et aucun étranger ne passera plus par elle.
“Sa’an nan za ku san cewa ni, Ubangiji Allahnku, ina zaune a Sihiyona, dutsena mai tsarki. Urushalima za tă zama mai tsarki; baƙi ba za su ƙara mamaye ta ba.
18 Cela arrivera en ce jour-là, que les montagnes laisseront tomber du vin doux, les collines couleront de lait, tous les ruisseaux de Juda couleront avec des eaux; et une fontaine jaillira de la maison de Yahvé, et arrosera la vallée de Shittim.
“A wannan rana duwatsu za su ɗiga da sabon ruwan inabi, tuddai kuma za su malmalo madara; dukan rafuffukan Yahuda za su yi ta gudano da ruwa. Maɓulɓula kuma za tă fito daga gidan Ubangiji haka ma ruwa a kwarin itatuwan ƙirya.
19 L'Égypte sera une désolation et Edom sera un désert, pour les violences faites aux enfants de Juda, parce qu'ils ont versé du sang innocent dans leur pays.
Amma Masar za tă zama kango, Edom kuma hamada marar amfani, saboda kama-karyar da aka yi wa mutanen Yahuda, a ƙasar da aka zub da jinin marasa laifi.
20 Mais Juda sera habité pour toujours, et Jérusalem de génération en génération.
Za a zauna a Yahuda har abada Urushalima kuma daga tsara zuwa tsara.
21 Je purifierai leur sang que je n'ai pas purifié, car Yahvé habite en Sion. »
Alhakin jininsu, wanda ban gafarta ba, zan gafarta.”

< Joël 3 >