< Job 30 >

1 « Mais maintenant, ceux qui sont plus jeunes que moi me tournent en dérision, dont j'ai considéré les pères comme indignes d'être mis avec mes chiens de berger.
“Amma yanzu suna yi mini ba’a waɗanda na girme su, waɗanda iyayensu maza ba su isa su zama karnukan kiwon garken tumakina ba.
2 A quoi me sert la force de leurs mains? des hommes chez qui l'âge mûr a péri?
Ina amfani ƙarfin hannuwansu gare ni, tun da ba su da sauran kuzari?
3 Ils sont décharnés par le manque et la famine. Ils rongent la terre aride, dans la pénombre du désert et de la désolation.
Duk sun rame don rashi da yunwa, suna yawo a gaigayar ƙasa a kufai da dare.
4 Ils cueillent des herbes salées près des buissons. Les racines de l'arbre à balais sont leur nourriture.
A cikin jeji suna tsinkar ganyaye marasa daɗi, jijiyoyin itacen kwakwa ne abincinsu.
5 Ils sont chassés du milieu des hommes. Ils crient après eux comme après un voleur,
An kore su daga cikin mutanensu, aka yi musu ihu kamar ɓarayi.
6 de sorte qu'ils vivent dans des vallées effrayantes, et dans les trous de la terre et des rochers.
An sa dole su zauna a kwazazzabai da kuma cikin kogunan duwatsu da kuma cikin ramummuka cikin ƙasa.
7 Ils braillent dans les buissons. Ils sont rassemblés sous les orties.
Suka yi ta kuka kamar dabbobi a jeji, suka taru a ƙarƙashin sarƙaƙƙiya.
8 Ce sont des enfants de fous, oui, des enfants de méchants. Ils ont été chassés du pays à coups de fouet.
Mutane marasa hankali marasa suna, an kore su daga ƙasar.
9 « Maintenant, je suis devenu leur chant. Oui, je suis un mot d'ordre pour eux.
“Yanzu kuma’ya’yansu maza su suke yi mini ba’a cikin waƙa na zama abin banza a gare su.
10 Ils m'abhorrent, ils se tiennent à l'écart de moi, et n'hésitez pas à me cracher au visage.
Suna ƙyamata suna guduna; suna tofa mini miyau a fuska.
11 Car il a détaché son cordon, et m'a fait souffrir; et ils se sont libérés de toute contrainte devant moi.
Yanzu da Allah ya kunce bakana ya ba ni wahala sun raba ni da mutuncina.
12 A ma droite se lève la populace. Ils ont repoussé mes pieds. Ils ont jeté contre moi leurs méthodes de destruction.
A hannun damana’yan tā-da-na-zaune-tsaye sun tayar; sun sa tarko a ƙafafuna, sun yi shirin hallaka ni.
13 Ils marquent mon chemin. Ils favorisent ma destruction sans l'aide de personne.
Sun ɓata mini hanyata; sun yi nasara cikin hallaka ni, ba tare da wani ya taimake su ba.
14 Ils arrivent comme par une large brèche. Ils s'enroulent au milieu des ruines.
Suka nufo ni daga kowane gefe; suka auko mini da dukan ƙarfinsu.
15 Les terreurs se sont retournées contre moi. Ils chassent mon honneur comme le vent. Mon bien-être s'est éteint comme un nuage.
Tsoro ya rufe ni; an kawar mini mutuncina kamar da iska, dukiyata ta watse kamar girgije.
16 « Maintenant mon âme est répandue au-dedans de moi. Des jours d'affliction se sont emparés de moi.
“Yanzu raina yana ƙarewa; kwanakin wahala sun kama ni.
17 Au temps de la nuit, mes os sont percés en moi, et les douleurs qui me rongent ne prennent aucun repos.
Dare ya huda ƙasusuwana; ina ta shan azaba ba hutawa.
18 Mon vêtement est défiguré par une grande force. Il me lie comme le col de ma tunique.
A cikin girman ikonsa Allah ya zama kamar riga a jikina; ya shaƙe ni kamar wuyan rigata.
19 Il m'a jeté dans la boue. Je suis devenu comme de la poussière et des cendres.
Ya jefa ni cikin laka, na zama ba kome ba sai ƙura da toka.
20 Je crie vers toi, et tu ne me réponds pas. Je me lève, et tu me regardes.
“Na yi kuka gare ka ya Allah, amma ba ka amsa mini ba. Na tashi tsaye, amma sai ka dube ni kawai.
21 Tu t'es retourné pour être cruel envers moi. De la force de ta main, tu me persécutes.
Ka dube ni ba tausayi; Ka kai mini hari da ƙarfin hannunka.
22 Tu me soulèves au vent, et tu me pousses avec lui. Vous me dissolvez dans la tempête.
Ka ɗaga ni sama ka ɗora ni a kan iska; ka jujjuya ni cikin hadari.
23 Car je sais que tu me feras mourir, à la maison désignée pour tous les vivants.
Na san za ka sauko da ni ga mutuwa zuwa wurin da kowane mai rai zai je.
24 « Cependant, on ne tend pas la main dans sa chute? Ou dans sa calamité donc crier au secours?
“Ba shakka ba mai ɗora hannu a kan mutumin da yake cikin wahala. Lokacin da ya yi kukan neman taimako a cikin wahalarsa.
25 N'ai-je pas pleuré sur celui qui était dans la détresse? Mon âme n'a-t-elle pas été affligée par les nécessiteux?
Ashe ban yi kuka domin waɗanda suke cikin damuwa ba? Ko zuciyata ba tă yi baƙin ciki domin matalauta ba?
26 J'ai cherché le bien, et le mal est venu. Quand j'ai attendu la lumière, l'obscurité est venue.
Duk da haka sa’ad da nake begen abu mai kyau, mugun abu ne ya zo; Sa’ad da nake neman haske, sai duhu ya zo.
27 Mon cœur est troublé, et ne se repose pas. Des jours d'affliction sont venus sur moi.
Zuciyata ba tă daina ƙuna ba; ina fuskantar kwanakin wahala.
28 Je suis en deuil sans le soleil. Je me lève dans l'assemblée, et je crie à l'aide.
Na yi baƙi ƙirin, amma ba rana ce ta ƙona ni ba. Na tsaya a cikin mutane, na kuma yi kuka don taimako.
29 Je suis un frère pour les chacals, et un compagnon des autruches.
Na zama ɗan’uwan diloli, na zama abokan mujiyoyi.
30 Ma peau devient noire et se détache de moi. Mes os sont brûlés par la chaleur.
Fatar jikina ta yi baƙi tana ɓarewa; jikina yana ƙuna da zazzaɓi.
31 C'est pourquoi ma harpe s'est changée en deuil, et ma pipe dans la voix de ceux qui pleurent.
Garayata ta zama ta makoki, sarewata kuma ta zama ta kuka.

< Job 30 >