< Job 17 >

1 « Mon esprit est consumé. Mes jours sont éteints et la tombe est prête pour moi.
Na karaya, kwanakina sun kusa ƙarewa, kabari yana jirana.
2 Il y a certainement des moqueurs avec moi. Mon regard s'attarde sur leur provocation.
Ba shakka masu yi mini ba’a suna kewaye da ni; idanuna suna ganin tsokanar da suke yi mini.
3 « Maintenant, donnez un gage. Sers-toi de toi-même comme garantie pour moi. Qui est là pour me donner la main?
“Ya Allah, ka ba ni abin da ka yi mini alkawari. Wane ne zai kāre ni?
4 Car tu as caché leur cœur à l'intelligence, c'est pourquoi vous ne les exalterez pas.
Ka rufe zuciyarsu yadda ba za su iya ganewa ba, saboda haka ba za ka bari su yi nasara ba.
5 Celui qui dénonce ses amis pour le pillage, même les yeux de ses enfants seront défaillants.
In mutum ya juya wa abokansa baya don a ba shi wata lada’ya’yansa za su makance.
6 « Mais il a fait de moi la risée du peuple. Ils me crachent au visage.
“Allah ya sa na zama abin da kowa yake magana a kai wanda kowa yake tofa wa miyau a fuska.
7 Mon œil aussi est obscurci par la tristesse. Tous mes membres sont comme une ombre.
Idanuna ba sa gani sosai don baƙin ciki; jikina ya zama kamar inuwa kawai
8 Les hommes droits s'étonneront de cela. L'innocent se soulèvera contre l'impie.
Mutanen da suke masu adalci wannan abu ya ba su tsoro; marasa laifi sun tayar wa marasa tsoron Allah.
9 Mais le juste s'en tiendra à sa voie. Celui qui a les mains propres deviendra de plus en plus fort.
Duk da haka, masu adalci za su ci gaba da tafiya a kan hanyarsu, waɗanda hannuwansu suke da tsabta kuma za su ƙara ƙarfi.
10 Mais quant à vous tous, revenez. Je ne trouverai pas d'homme sage parmi vous.
“Amma ku zo dukanku, ku sāke gwadawa! Ba zan sami mutum ɗaya mai hikima ba a cikinku.
11 Mes jours sont passés. Mes plans sont rompus, comme les pensées de mon cœur.
Kwanakina sun wuce, shirye-shiryena sun ɓaci haka kuma abubuwan da zuciyata take so.
12 Ils changent la nuit en jour, dire « La lumière est proche » en présence de l'obscurité.
Mutanen nan sun juya rana ta zama dare. A tsakiyar duhu suka ce, ‘Haske yana kusa.’
13 Si je considère le séjour des morts comme ma maison, si j'ai étendu ma couche dans l'obscurité, (Sheol h7585)
In kabari ne begen da nake da shi kaɗai, in na shimfiɗa gadona a cikin duhu, (Sheol h7585)
14 si j'ai dit à la corruption: « Tu es mon père ». et au ver: « Ma mère » et « Ma sœur ».
In na ce wa kabari, ‘Kai ne mahaifina,’ tsutsa kuma ke ce, ‘Mahaifiyata’ ko ‘’yar’uwata,’
15 Où est donc mon espoir? Quant à mon espoir, qui le verra?
To, ina begena yake? Wane ne zai iya ganin wani bege domina?
16 Il descendra avec moi jusqu'aux portes du séjour des morts, ou descendre ensemble dans la poussière? » (Sheol h7585)
Ko begena zai tafi tare da ni zuwa kabari ne? Ko tare za a bizne mu cikin ƙura?” (Sheol h7585)

< Job 17 >