< Jérémie 8 >

1 En ce temps-là, dit Yahvé, on tirera de leurs sépulcres les os des rois de Juda, les os de ses princes, les os des prêtres, les os des prophètes et les os des habitants de Jérusalem.
“‘A wancan lokaci, in ji Ubangiji, za a fitar da ƙasusuwan sarakuna da na shugabannin Yahuda, ƙasusuwan firistoci da na annabawa, da kuma ƙasusuwan mutanen Urushalima daga kaburbura.
2 Ils les étendront devant le soleil, la lune et toute l'armée du ciel, qu'ils ont aimée, qu'ils ont servie, après laquelle ils ont marché, qu'ils ont cherchée et qu'ils ont adorée. Ils ne seront pas recueillis et ne seront pas enterrés. Ils seront comme du fumier à la surface de la terre.
Za a shimfiɗa su a rana da wata da kuma dukan taurarin sammai, waɗanda suka ƙaunata suka kuma bauta wa, waɗanda suka bi suka nemi shawarar suka kuma yi wa sujada. Ba za a tattara su ko a binne su ba, amma za su zama kamar juji a jibge a ƙasa.
3 Tous ceux qui resteront de cette famille méchante, dans tous les lieux où je les aurai chassés, choisiront la mort plutôt que la vie, dit l'Éternel des Armées.
Duk inda na kore su zuwa, dukan waɗanda suka ragu na wannan muguwar al’umma za su gwammaci mutuwa da rai, in ji Ubangiji Maɗaukaki.’
4 Tu leur diras: « Yahvé dit: "'Les hommes tombent-ils et ne se relèvent-ils pas? Est-ce qu'on se détourne et qu'on ne revient pas?
“Fada musu cewa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, “‘Sa’ad da mutane suka fāɗi, ba sa tashi ne? Sa’ad da mutum ya kauce, ba ya dawowa?
5 Pourquoi donc le peuple de Jérusalem a-t-il régressé par un perpétuel retour en arrière? Ils s'accrochent à la tromperie. Ils refusent de revenir.
To, me ya sa waɗannan mutane suka kauce? Me ya sa Urushalima kullum take kaucewa? Sun manne wa ƙarya; suka ƙi su dawo.
6 J'ai écouté et entendu, mais ils n'ont pas dit ce qui est juste. Personne ne se repent de sa méchanceté en disant: « Qu'ai-je fait? » Tout le monde se tourne vers son parcours, comme un cheval qui fonce tête baissée dans la bataille.
Na saurara sosai, amma ba su faɗi wata maganar kirki ba. Ba wanda ya tuba daga muguntarsa, sai ma cewa yake, “Me na yi?” Kowa ta kai-ta-kai yake kamar dokin da ya kutsa kai a fagen fama.
7 Oui, la cigogne dans le ciel connaît les temps qui lui sont impartis. La tourterelle, l'hirondelle et la grue observent le moment de leur venue; mais mon peuple ne connaît pas la loi de Yahvé.
Ko shamuwa ta sararin sama ma takan san lokutan da aka tsara mata, kurciya, mashirare da kuma zalɓe sukan lura da lokacin ƙauransu. Amma mutanena ba su san abubuwan da Ubangiji yake bukata ba.
8 "'Comment dites-vous: « Nous sommes sages, et la loi de Yahvé est avec nous »? » Mais voici que la fausse plume des scribes a fait de cela un mensonge.
“‘Yaya za ku ce, “Muna da hikima, gama muna da dokar Ubangiji,” alhali alƙalamin ƙarya na magatakarda ya yi ƙarya?
9 Les sages sont déçus. Ils sont consternés et pris au piège. Voici qu'ils ont rejeté la parole de Yahvé. Quel genre de sagesse y a-t-il en eux?
Za a kunyatar da masu hikima; za su yi fargaba a kuma kama su. Da yake sun ƙi maganar Ubangiji, wace irin hikima kuka ce kuke da ita?
10 Je donnerai donc leurs femmes à d'autres. et leurs champs à ceux qui les posséderont. Car tous, depuis le plus petit jusqu'au plus grand, se livrent à la convoitise; depuis le prophète jusqu'au prêtre, tout le monde fait du faux.
Saboda haka zan ba da matansu ga waɗansu gonakinsu kuma ga waɗansu da suka ci da yaƙi. Tun daga ƙarami har zuwa babba, kowannensu yana haɗamar cin muguwar riba; har da annabawa da firistoci ma, kowannensu yana ƙarya.
11 Ils ont légèrement guéri la blessure de la fille de mon peuple, en disant, « Paix, paix », quand il n'y a pas de paix.
Sukan ɗaura mikin mutanena sai ka ce mikin ba shi da matsala. Suna cewa, “Lafiya, Lafiya,” alhali kuwa ba lafiya.
12 N'ont-ils pas eu honte quand ils ont commis des abominations? Non, ils n'avaient pas du tout honte. Ils ne pouvaient pas rougir. Ils tomberont donc parmi ceux qui tombent. Au temps de leur visite, ils seront renversés, dit Yahvé.
Sukan ji kunyar halin banƙyamarsu kuwa? Sam, ba su da kunya ko kaɗan; ba su ma san yadda za su ji kunya ba. Saboda haka sukan fāɗi tare da fāɗaɗɗu; za su fāɗi sa’ad da aka hukunta su, in ji Ubangiji.
13 "'Je les anéantirai, dit Yahvé. Il n'y aura pas de raisins sur la vigne, pas de figues sur le figuier, et la feuille se fanera. Les choses que je leur ai données disparaîtra d'eux. »
“‘Zan ƙwace girbinsu, in ji Ubangiji. Ba a za sami inabi a kuringa ba. Ba za a sami’ya’ya a itacen ɓaure ba, ganyayensu kuwa za su bushe. Abin da na ba su za a ƙwace.’”
14 « Pourquoi restons-nous assis? Rassemblez-vous! Entrons dans les villes fortifiées, et faisons silence là-bas; car Yahvé notre Dieu nous a fait taire, et nous a donné de l'eau empoisonnée à boire, parce que nous avons péché contre Yahvé.
Me ya sa muke zama a nan? Mu tattaru! Mu gudu zuwa birane masu katanga mu mutu a can! Gama Ubangiji Allahnmu ya ƙaddara mana mutuwa ya kuma ba mu ruwan dafi mu sha, domin mun yi masa zunubi.
15 Nous avons cherché la paix, mais rien de bon n'est venu; et pour un temps de guérison, et voici la consternation!
Mun sa zuciya ga salama amma ba lafiya, mun sa zuciya ga lokacin warkarwa amma sai ga razana.
16 On entend l'ébrouement de ses chevaux depuis Dan. Toute la terre tremble au son du hennissement de ses forts; car ils sont venus, et ont dévoré le pays et tout ce qu'il contient, la ville et ceux qui l'habitent. »
Daga Dan ana jin tirjin dawakan abokin gāba; da jin haniniyar ingarmunsu dukan ƙasar ta girgiza. Sun zo su cinye ƙasar da kome da yake cikinta, birni da dukan mazaunanta.
17 « Car voici, je vais envoyer des serpents, des vipères parmi vous, qui ne sera pas charmé; et ils vous mordront », dit Yahvé.
“Duba, zan aika macizai masu dafi a cikinku, kāsā, waɗanda ba su da maƙari, za su kuwa sassare ku,” in ji Ubangiji.
18 Oh, si je pouvais me consoler du chagrin! Mon cœur est faible au fond de moi.
Ya mai ta’aziyyata a cikin baƙin ciki, zuciyata ta ɓaci ƙwarai.
19 Voici la voix du cri de la fille de mon peuple, venant d'un pays très lointain: « Yahvé n'est-il pas à Sion? Son Roi n'est-il pas en elle? » « Pourquoi m'ont-ils provoqué à la colère avec leurs images gravées, et avec des idoles étrangères? »
Ka saurari kukan mutanena daga ƙasa mai nisa suna cewa, “Ubangiji ba ya a Sihiyona ne? Sarkinta ba ya can ne kuma?” “Me ya sa suka tsokane ni da gumakansu har na yi fushi, da baƙin gumakansu marasa amfani?”
20 « La récolte est passée. L'été est terminé, et nous ne sommes pas sauvés. »
“Girbi ya wuce, damuna ta ƙare, ba a kuwa cece mu ba.”
21 A cause du malheur de la fille de mon peuple, je suis blessé. Je suis en deuil. Le désarroi s'est emparé de moi.
Da yake an ragargazar da mutanena, an ragargaza ni ke nan; na yi kuka, tsoro ya kama ni.
22 N'y a-t-il pas de baume en Galaad? Il n'y a pas de médecin là-bas? Pourquoi alors la santé de la fille de mon peuple n'est-elle pas rétablie?
Ba magani ne a Gileyad? Ba likita ne a can? To, me ya sa ba warkarwa wa raunin mutanena?

< Jérémie 8 >