< Jérémie 52 >

1 Sédécias avait vingt et un ans lorsqu'il commença à régner. Il régna onze ans à Jérusalem. Sa mère s'appelait Hamutal, fille de Jérémie, de Libna.
Zedekiya yana da shekara ashirin da ɗaya sa’ad da ya ci sarauta. Ya yi mulki a Urushalima shekara goma sha ɗaya. Sunan uwarsa Hamutal,’yar Irmiya, wanda yake zaune a Libna.
2 Il fit ce qui est mal aux yeux de l'Éternel, selon tout ce qu'avait fait Jojakim.
Sarki Zedekiya ya aikata abin da yake mugu a gaban Ubangiji kamar yadda Sarki Yehohiyakim ya yi.
3 Car c'est par la colère de Yahvé que cela arriva à Jérusalem et en Juda, jusqu'à ce qu'il les eût chassés de sa présence. Sédécias se révolta contre le roi de Babylone.
Al’amarin ya zama da muni ƙwarai a cikin Isra’ila da Yahuda, don haka Ubangiji ya husata har ya sa aka kai mutanen bautar talala. Zedekiya kuwa ya tayar wa Sarkin Babilon.
4 La neuvième année de son règne, le dixième jour du mois, Nabuchodonosor, roi de Babylone, vint, lui et toute son armée, contre Jérusalem, et campa devant elle; ils construisirent des forts tout autour.
A kan rana ta goma ga watan goma, a shekara ta tara ta mulkin Zedekiya, Sarkin Yahuda, sai Nebukadnezzar, Sarkin Babilon, ya zo yaƙi da Urushalima tare da dukan sojojinsa. Suka kewaye ta da yaƙi, suka gina katanga kewaye da ita.
5 La ville fut ainsi assiégée jusqu'à la onzième année du roi Sédécias.
An kewaye birnin da yaƙi har shekara ta goma sha ɗaya ta mulkin Zedekiya.
6 Au quatrième mois, le neuvième jour du mois, la famine sévit dans la ville, de sorte qu'il n'y eut pas de pain pour le peuple du pays.
A kan rana ta tara a watan huɗu na wannan shekara, yunwa ta tsananta ƙwarai a birnin. Mutane suka rasa abin da za su ci.
7 Alors il y eut une brèche dans la ville, et tous les hommes de guerre s'enfuirent et sortirent de nuit de la ville par le chemin de la porte entre les deux murs, qui était près du jardin du roi. Or les Chaldéens étaient contre la ville tout autour. Les hommes de guerre se dirigèrent vers la plaine.
Sai aka huda katangan birnin, sojojin kuwa suka gudu, suka fita daga cikin birnin da dare ta hanyar ƙofar da take tsakanin bango biyu, kusa da gonar sarki, sa’ad da Babiloniyawa suke kewaye da birnin. Sojojin suka nufi wajen Araba.
8 Mais l'armée des Chaldéens poursuivit le roi et atteignit Sédécias dans les plaines de Jéricho, et toute son armée fut dispersée devant lui.
Amma sojojin Babiloniyawa suka runtumi sarki Zedekiya, suka ci masa a filayen Yeriko. Dukan sojoji suka yashe shi.
9 Ils prirent le roi, et le firent monter vers le roi de Babylone, à Ribla, dans le pays de Hamath, qui prononça un jugement contre lui.
Da aka kama Zedekiya, sai aka kai shi wurin Sarkin Babilon a Ribla a ƙasar Hamat, a nan ne Sarkin Babilon ya yanke masa shari’a.
10 Le roi de Babylone fit mourir sous ses yeux les fils de Sédécias. Il tua aussi tous les princes de Juda à Ribla.
Sarkin Babilon ya kashe’ya’yan Zedekiya a idonsa. Ya kuma kashe dukan shugabannin Yahuda a Ribla.
11 Il fit crever les yeux à Sédécias, et le roi de Babylone le lia avec des chaînes, le transporta à Babylone et le mit en prison jusqu'au jour de sa mort.
Sa’an nan ya ƙwaƙule idanun Zedekiya, ya kuma sa masa ƙuƙumi, aka kai shi Babilon inda aka sa shi a kurkuku har ran da ya mutu.
12 Le cinquième mois, le dixième jour du mois, qui était la dix-neuvième année du roi Nebucadnetsar, roi de Babylone, Nebuzaradan, chef des gardes, qui se tenait devant le roi de Babylone, entra dans Jérusalem.
A kan rana ta goma ga watan biyar a shekara ta goma sha tara ta sarautar Nebukadnezzar, Sarkin Babilon, sai Nebuzaradan shugaban matsara da kuma ɗan majalisar sarki, ya zo Urushalima.
13 Il brûla la maison de Yahvé et la maison du roi, et il brûla au feu toutes les maisons de Jérusalem, toutes les grandes maisons.
Sai ya ƙone haikalin Ubangiji, da gidan sarki, da dukan gine-gine masu alfarman da suke Urushalima.
14 Toute l'armée des Chaldéens, qui était avec le chef des gardes, abattit toutes les murailles de Jérusalem, tout autour.
Sojojin Babiloniyawa da suke tare da shugaban matsara, suka rushe dukan katangan Urushalima.
15 Puis Nebuzaradan, chef des gardes, emmena en captivité les plus pauvres du peuple, le reste du peuple qui était resté dans la ville, les réfractaires qui s'étaient ralliés au roi de Babylone, et le reste de la multitude.
Sa’an nan Nebuzaradan shugaban matsara ya kwashe waɗansu matalauta, da sauran mutane da aka bari a birnin, da waɗanda suka gudu zuwa wurin Sarkin Babilon, da sauran masu sana’a, ya kai su bautar talala a Babilon.
16 Mais Nebuzaradan, chef des gardes, laissa les plus pauvres du pays comme vignerons et cultivateurs.
Amma ya bar waɗansu matalauta na gaske a ƙasar don su yi aiki a gonakin inabi, da sauran gonaki.
17 Les Chaldéens brisèrent les colonnes d'airain qui étaient dans la maison de l'Éternel, les socles et la mer d'airain qui étaient dans la maison de l'Éternel, et ils emportèrent tout l'airain à Babylone.
Babiloniyawa kuwa suka farfasa ginshiƙan tagulla, da dakalai, da babbar kwatarniya, waɗanda suke a haikalin Ubangiji. Suka kwashe tagulla duka suka kai Babilon.
18 Ils emportèrent aussi les marmites, les pelles, les éteignoirs, les bassins, les cuillères et tous les ustensiles d'airain avec lesquels on faisait le service.
Suka kwashe tukwanen ƙarfe, da manyan cokula, da hantsuka, da daruna, da tasoshin ƙona turare, da kayayyakin tagulla waɗanda ake amfani da su domin hidimar haikali.
19 Le chef des gardes emporta les coupes, les poêles à feu, les bassins, les marmites, les chandeliers, les cuillères et les coupes, ce qui était d'or comme de l'or, et ce qui était d'argent comme de l'argent.
Suka kuma kwashe ƙananan kwanonin sha, da farantan wuta, da daruna, da tukwane, da alkukai, da tasoshin ƙona turare, da kwanonin miƙa hadayar sha. Duk abin da yake na zinariya da azurfa, shugaban matsara ya kwashe.
20 Ils prirent les deux colonnes, la mer unique et les douze taureaux d'airain qui étaient sous les socles, que le roi Salomon avait faits pour la maison de Yahvé. Le bronze de tous ces objets était sans poids.
Tagullar da sarki Solomon ya yi wa haikalin Ubangiji da ita, wato, ginshiƙai biyu, da ƙaton kwano mai suna Teku na tagulla, da bijimai goma sha biyu, waɗanda suke ɗauke da kwatarniya, da dakalai, ta fi ƙarfin a auna.
21 Quant aux colonnes, la hauteur de l'une d'elles était de dix-huit coudées; une ligne de douze coudées l'entourait; son épaisseur était de quatre doigts. Elle était creuse.
Tsawon kowane ginshiƙi kamu goma sha takwas ne, kewayensa kuwa kamu goma sha biyu ne, kaurinsa kuma huɗu ne. Kowannensu yana da rami a ciki.
22 Il était surmonté d'un chapiteau d'airain; la hauteur de ce chapiteau était de cinq coudées, avec un réseau et des grenades sur le chapiteau tout autour, le tout d'airain. Le second pilier avait aussi la même chose, avec des grenades.
A kan kowane ginshiƙi, an yi masa dajiyar tagulla, tsayinta kamu biyar. A bisa kan kowace dajiya akwai raga da siffofin rumman na tagulla kewaye da dajiyar. Ginshiƙi na biyu ma haka yake da siffofin rumman.
23 Il y avait quatre-vingt-seize grenades sur les côtés, et cent grenades sur le réseau, tout autour.
Akwai siffofin rumman tasa’in da shida da ake gani a gefen. Dukan siffofin rumman da suke a kan ragar kewaye, guda ɗari ne.
24 Le chef des gardes prit Seraja, le souverain sacrificateur, Sophonie, le second sacrificateur, et les trois gardiens du seuil;
Shugaban matsara kuma ya ɗauki Serahiya babban firist, da Zefaniya wanda yake biye da babban firist, da mutum uku masu tsaron ƙofar, ya tafi da su.
25 il prit dans la ville un officier préposé aux hommes de guerre, sept hommes de ceux qui avaient vu le visage du roi et qui se trouvaient dans la ville, le secrétaire du chef de l'armée, qui rassemblait le peuple du pays, et soixante hommes du peuple du pays, qui se trouvaient au milieu de la ville.
Daga cikin birnin kuma ya ɗauki shugaban sojojin, da mutum bakwai’yan majalisar sarki, da magatakardan shugaban sojojin wanda yakan tara sojojin ƙasar, da mutane sittin na ƙasar, waɗanda aka same su a birnin, ya tafi da su.
26 Nebuzaradan, chef des gardes, les prit et les amena au roi de Babylone, à Ribla.
Nebuzaradan shugaban matsara ya tafi da waɗannan mutane wurin Sarkin Babilon a Ribla,
27 Le roi de Babylone les frappa et les fit mourir à Ribla, dans le pays de Hamath. Et Juda fut emmené captif hors de son pays.
Sarkin Babilon kuwa ya kashe su a Ribla a ƙasar Hamat. Haka aka tafi da mutanen Yahuda bautar talala, daga ƙasarta.
28 Voici le nombre de personnes que Nebucadnetsar emmena en captivité: la septième année, trois mille vingt-trois Juifs;
Wannan shi ne yawan mutanen da Nebukadnezzar ya kai su bauta. A shekara ta bakwai ta sarautarsa, ya tafi da Yahudawa 3,023;
29 La dix-huitième année de Nabuchodonosor, il emmena en captivité de Jérusalem huit cent trente-deux personnes;
a shekara ta goma sha takwas ta sarautar Nebukadnezzar, ya tafi da Yahudawa daga Urushalima 832;
30 La vingt-troisième année de Nebucadnetsar, Nebuzaradan, chef des gardes, emmena captifs des Juifs sept cent quarante-cinq personnes. Tout le peuple était au nombre de quatre mille six cents.
a shekara ta ashirin da uku ta sarautarsa, Nebuzaradan shugaban matsara ya tafi da Yahudawa 745. Jimillarsu duka 4,600 ne.
31 La trente-septième année de la captivité de Jojakin, roi de Juda, le douzième mois, le vingt-cinquième jour du mois, Evilmérodac, roi de Babylone, la première année de son règne, releva la tête de Jojakin, roi de Juda, et le fit sortir de prison.
A shekarar da Ewil-Merodak ya zama Sarkin Babilon, sai ya nuna wa Yehohiyacin Sarkin Yahuda alheri. Ya fisshe shi daga kurkuku. Wannan ya faru ran ashirin da biyar ga watan goma sha biyu a shekara ta talatin da bakwai bayan da aka kai Yehohiyacin bauta.
32 Il lui parla avec bonté, plaça son trône au-dessus du trône des rois qui étaient avec lui à Babylone,
Ewil-Merodak ya nuna wa Yehohiyacin alheri, ya ba shi matsayi na daraja fiye da waɗansu sarakunan da aka kai su bautar talala a Babilon tare da shi.
33 et changea ses vêtements de prison. Jehoïachin mangea du pain devant lui continuellement tous les jours de sa vie.
Yehohiyacin ya tuɓe tufafin kurkuku, ya riƙa cin abinci kullum a teburin sarki, har dukan sauran kwanakin ransa.
34 Pour son argent de poche, le roi de Babylone lui donna une allocation continuelle, chaque jour une portion jusqu'au jour de sa mort, tous les jours de sa vie.
Kowace rana akan ba shi kyauta bisa ga umarnin sarkin Babilon, saboda bukatarsa. Haka aka yi masa har rasuwarsa.

< Jérémie 52 >