< Jérémie 50 >

1 La parole que Yahvé a prononcée sur Babylone, sur le pays des Chaldéens, par Jérémie, le prophète.
Ga maganar Ubangiji da ya yi ta wurin Irmiya annabi game da Babilon da kuma ƙasar Babiloniyawa.
2 « Déclarez parmi les nations et publiez, et établir une norme; publier, et ne pas dissimuler; disent: « Babylone a été prise, Bel est déçu, Merodach est consterné! Ses images sont déçues. Ses idoles sont consternées.
“Ka yi shela ka kuma furta a cikin al’ummai, ka tā da tuta ka kuma furta; kada ku ɓoye kome, amma ku ce, ‘Za a ci Babilon da yaƙi; za a kunyata Bel, Marduk ya cika da tsoro. Siffofinta za su sha kunya gumakanta za su cika da tsoro.’
3 Car une nation monte du nord contre elle, qui rendra sa terre désolée, et personne n'y habitera. Ils ont fui. Ils sont partis, l'homme et l'animal.
Al’umma daga arewa za tă fāɗa mata su mai da ƙasar kango. Ba wanda zai zauna a cikinta; mutane da dabbobi za su gudu.
4 « En ces jours-là, et en ce temps-là, » dit Yahvé, « les enfants d'Israël viendront, eux et les enfants de Juda ensemble; ils poursuivront leur chemin en pleurant, et chercheront Yahvé leur Dieu.
“A kwanakin nan, a wannan lokaci,” in ji Ubangiji, “mutanen Isra’ila da mutanen Yahuda gaba ɗaya za su tafi cikin hawaye su nemi Ubangiji Allahnsu.
5 Ils s'informeront sur Sion, le visage tourné vers elle, en disant: « Venez, joignez-vous à Yahvé par une alliance éternelle ». qui ne sera pas oublié.
Za su tambayi hanyar zuwa Sihiyona su kuma juya fuskokinsu wajenta. Za su zo su haɗa kansu ga Ubangiji a madawwamin alkawari da ba za a manta da shi ba.
6 Mon peuple est une brebis égarée. Leurs bergers les ont fait s'égarer. Ils les ont repoussés sur les montagnes. Ils sont passés de montagne en colline. Ils ont oublié leur lieu de repos.
“Mutanena sun zama ɓatattun tumaki; makiyayansu sun bauɗar da su suka sa suna ta yawo a cikin duwatsu. Sun yi ta yawo a bisa dutse da tudu suka manta wurin hutunsu.
7 Tous ceux qui les ont trouvés les ont dévorés. Leurs adversaires ont dit: « Nous ne sommes pas coupables, parce qu'ils ont péché contre Yahvé, la demeure de la justice, Yahvé, l'espoir de leurs pères.
Duk wanda ya same su ya cinye su; abokan gābansu suka ce, ‘Ba mu da laifi, gama sun yi zunubi wa Ubangiji, wurin kiwonsu na gaske, Ubangiji, abin sa zuciyar kakanninsu.’
8 « Fuyez du milieu de Babylone! Sortez du pays des Chaldéens, et être comme les boucs devant les troupeaux.
“Ku gudu daga Babilon; ku bar ƙasar Babiloniyawa, ku zama kamar awakin da suke bi da garke.
9 Car voici que je vais susciter et fais monter contre Babylone une troupe de grandes nations du pays du nord; et ils se rangent en bataille contre elle. Elle sera prise à partir de là. Leurs flèches seront comme celles d'un homme puissant et expert. Aucun d'entre eux ne reviendra en vain.
Gama zan kuta in kuma kawo a kan Babilon haɗinkan manyan al’ummai na arewa. Za su ja dāgār gāba da ita, kuma daga arewa za a ci ta da yaƙi. Kibiyoyinsu za su zama kamar na gwanayen jarumawa waɗanda ba sa dawowa hannu wofi.
10 La Chaldée sera une proie. Tous ceux qui s'en prennent à elle seront satisfaits », dit Yahvé.
Saboda haka za a washe Babiloniyawa; dukan waɗanda suka washe ta za su ƙoshi,” in ji Ubangiji.
11 « Parce que vous êtes heureux, parce que vous vous réjouissez, O vous qui pillez mon héritage, car tu es dévergondée comme une génisse qui foule le grain, et hennir comme des chevaux forts,
“Saboda kuna farin ciki kuna kuma murna, ku da kuka washe gādona, domin kuna tsalle kamar karsana mai sussuka hatsi kuna kuma haniniya kamar ingarmu.
12 votre mère sera totalement déçue. Celle qui t'a porté sera confondue. Voici qu'elle sera la plus petite des nations, un désert, une terre aride, et un désert.
Mahaifiyarku za tă sha babbar kunya; ita da ta haife ku za tă sha kunya. Za tă zama mafi ƙanƙanta na al’ummai, jeji, busasshiyar ƙasa, hamada.
13 A cause de la colère de Yahvé, elle ne sera pas habitée, mais elle sera totalement désolée. Tous ceux qui passeront par Babylone seront étonnés, et siffler sur tous ses fléaux.
Saboda fushin Ubangiji ba za tă zauna a cikinta ba amma za tă zama kufai gaba ɗaya. Duk waɗanda suka wuce Babilon za su ji tsoro su kuma yi tsaki saboda dukan mikinta.
14 Mettez-vous en ordre de bataille contre Babylone tout autour, vous tous qui courbez l'arc; lui tirer dessus. N'épargnez aucune flèche, car elle a péché contre Yahvé.
“Ku ja dāgā kewaye da Babilon, dukanku waɗanda kuke jan baka. Ku harbe ta! Kada ku rage kibiyoyi, gama ta yi zunubi ga Ubangiji.
15 Criez contre elle tout autour. Elle s'est soumise. Ses remparts sont tombés. Ses murs ont été abattus, car c'est la vengeance de Yahvé. Se venger d'elle. Comme elle l'a fait, faites-lui.
Ku yi kuwwa a kanta a kowane gefe! Ta miƙa wuya, hasumiyarta ta fāɗi, katangarta sun rushe. Da yake wannan sakayya ce ta Ubangiji, ku ɗauki fansa a kanta; yi mata yadda ta yi wa waɗansu.
16 Coupez le semeur de Babylone, et celui qui manie la faucille au moment de la moisson. Par peur de l'épée oppressante, ils retourneront chacun à leur propre peuple, et ils fuiront chacun dans leur pays.
Ku datse wa Babilon mai shuka, da mai girbi lauje a lokacin girbi. Saboda takobin mai zalunci bari kowa ya koma ga mutanensa, bari kowa ya gudu zuwa ga ƙasarsa.
17 « Israël est une brebis traquée. Les lions l'ont chassé. D'abord, le roi d'Assyrie l'a dévoré, et enfin, Nebuchadnezzar, roi de Babylone, a brisé ses os. »
“Isra’ila garke ne da ya watse da zakoki suka kora. Na farkon da ya cinye shi sarkin Assuriya ne; na ƙarshen da ya ragargaza ƙasusuwansa Nebukadnezzar sarkin Babilon ne.”
18 C'est pourquoi Yahvé des armées, le Dieu d'Israël, dit: « Voici, je vais punir le roi de Babylone et son pays, comme j'ai puni le roi d'Assyrie.
Saboda haka ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Zan hukunta sarkin Babilon da ƙasarsa yadda na hukunta sarkin Assuriya.
19 Je ramènerai Israël dans son pâturage, et il se nourrira de Carmel et de Bashan. Son âme sera satisfaite sur les collines d'Ephraïm et en Galaad.
Amma zan komo da Isra’ila zuwa wurin kiwonsa zai kuwa yi kiwo a Karmel da Bashan; zai ƙosar da marmarinsa a tuddan Efraim da Gileyad.
20 En ces jours-là, et en ce temps-là, dit Yahvé, « l'iniquité d'Israël sera recherchée, et il n'y en aura pas, aussi les péchés de Juda, et ils ne seront pas trouvés; car je pardonnerai à ceux que j'ai laissés comme restes.
A kwanakin nan, da kuma a lokacin nan,” in ji Ubangiji, “za a yi bincike don laifin Isra’ila, amma ba za a samu ba, kuma don zunubin Yahuda, amma ba za a sami wani abu ba, gama zan gafarta wa raguwar da na rage.
21 « Monte contre le pays de Merathaim, même contre elle, et contre les habitants de Pekod. Tuez et détruisez tout après eux, dit Yahvé, « et faites tout ce que je vous ai ordonné.
“Ku fāɗa wa ƙasar Meratayim da waɗanda suke zama a Fekod. Ku fafara, ku kashe kuma hallaka su sarai,” in ji Ubangiji. “Ku aikata dukan abin da na umarce ku.
22 Un bruit de bataille retentit dans le pays, et de grande destruction.
Hargowar yaƙi tana a ƙasar, hargowar babbar hallaka!
23 Comme le marteau de toute la terre est écarté et brisé! Comme Babylone est devenue une désolation parmi les nations!
Dubi yadda aka karya aka kuma ragargaza gudumar dukan duniya! Dubi yadda Babilon ta zama kufai a cikin al’ummai!
24 Je vous ai tendu un piège, et vous êtes aussi pris, Babylone, et vous n'étiez pas au courant. Vous êtes trouvé, et aussi pris, parce que vous avez combattu contre Yahvé.
Na sa miki tarko, Babilon, kika kuwa kamu kafin ki sani; aka same ki aka kuma kama ki domin kin tayar wa Ubangiji.
25 Yahvé a ouvert son arsenal, et a sorti les armes de son indignation; car le Seigneur, Yahvé des Armées, a une œuvre à accomplir dans le pays des Chaldéens.
Ubangiji ya buɗe taskar makamansa ya fitar da makaman fushinsa, gama Maɗaukaki Ubangiji Mai Iko Duka yana da aikin da zai yi a ƙasar Babiloniyawa.
26 Venez contre elle depuis la frontière la plus éloignée. Ouvrez ses entrepôts. Jetez-la en tas. Détruisez-la complètement. Qu'il ne reste rien d'elle.
Ku zo ku yi gāba da ita daga nesa. Ku buɗe rumbunanta; ku jibga ta kamar tsibin hatsi. Ku hallaka ta sarai kada ku bar mata raguwa.
27 Tuez tous ses taureaux. Laissez-les aller à l'abattoir. Malheur à eux! Car leur jour est venu, le moment de leur visite.
Ku kashe dukan’yan bijimanta bari su gangara zuwa mayanka! Kaitonsu! Gama ranansu ta zo, lokaci ya yi da za a hukunta su.
28 Écoutez ceux qui fuient et s'échappent du pays de Babylone, pour annoncer dans Sion la vengeance de Yahvé notre Dieu, la vengeance de son temple.
Ku saurari masu gudun hijira da masu neman mafaka daga Babilon suna furtawa a Sihiyona yadda Ubangiji Allahnmu ya ɗauki fansa, fansa domin haikalinsa.
29 « Convoquez les archers contre Babylone, tous ceux qui tendent l'arc. Encampement contre elle tout autour. Que rien ne s'échappe. Remboursez-la en fonction de son travail. Selon tout ce qu'elle a fait, faites-lui; car elle s'est enflammée contre Yahvé, contre le Saint d'Israël.
“Ku kira’yan baka a kan Babilon, dukan waɗanda suke jan baka. Ku yi sansani kewaye da ita duka; kada ku bar wani ya tsira. Ku sāka mata don ayyukanta; ku yi mata yadda ta yi. Gama ta tayar wa Ubangiji, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
30 C'est pourquoi ses jeunes gens tomberont dans ses rues. Tous ses hommes de guerre seront réduits au silence en ce jour-là, dit Yahvé.
Saboda haka, samarinta za su fāɗi a tituna; za a kawar da dukan sojojinta a wannan rana,” in ji Ubangiji.
31 « Voici, j'en veux à toi, orgueilleux, dit le Seigneur, Yahvé des armées; « car ton jour est venu, le moment où je vous rendrai visite.
“Ga shi, ina gāba da ke, ya ke mai girman kai,” in ji Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, “gama ranarki ta zo, lokacin da za a hukunta ki.
32 L'orgueilleux trébuche et tombe, et personne ne le relèvera. Je vais allumer un feu dans ses villes, et il dévorera tous ceux qui sont autour de lui. »
Mai ɗaga kai za tă yi tuntuɓe ta kuma fāɗi kuma ba wanda zai taimake ta tă tashi; zan hura wuta a garuruwanta da za tă cinye duk waɗanda suke kewaye da ita.”
33 Yahvé des armées dit: « Les enfants d'Israël et les enfants de Juda sont opprimés ensemble. Tous ceux qui les ont fait prisonniers les retiennent. Ils refusent de les laisser partir.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “An danne mutanen Isra’ila, haka ma mutanen Yahuda. Dukan waɗanda suka kama su suna riƙe su kankan, suna kin barinsu su tafi.
34 Leur rédempteur est fort. Yahvé des Armées est son nom. Il va plaider leur cause de manière approfondie, pour qu'il donne du repos à la terre, et de troubler les habitants de Babylone.
Duk da haka Mai Fansarsu yana da ƙarfi; Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa. Zai kāre muradunsu gabagadi don yă kawo hutu ga ƙasarsu, amma rashin hutu ga waɗanda suke zaune a Babilon.
35 « L'épée est sur les Chaldéens, dit Yahvé, « et sur les habitants de Babylone, sur ses princes, et sur ses sages.
“Akwai takobi a kan Babiloniyawa!” In ji Ubangiji “a kan waɗanda suke zama a Babilon da kuma a kan fadawanta da masu hikimarta!
36 L'épée est sur les vantards, et ils deviendront des imbéciles. Une épée est sur ses hommes puissants, et ils seront consternés.
Akwai takobi a kan annabawan ƙaryanta! Za su zama wawaye. Akwai takobi a kan jarumawanta! Za su cika da tsoro.
37 L'épée est sur leurs chevaux, sur leurs chars, et sur toutes les personnes mixtes qui se trouvent au milieu d'elle; et ils deviendront comme des femmes. Une épée est sur ses trésors, et ils seront volés.
Akwai takobi a kan dawakanta da kekunan yaƙinta da kuma dukan baƙin da suke cikin mayaƙanta! Za su zama mata. Akwai takobi a kan dukiyarta! Za a washe su.
38 La sécheresse est sur ses eaux, et ils seront desséchés; car c'est un pays d'images gravées, et ils sont fous des idoles.
Fări a kan ruwanta! Za su bushe ƙaf. Gama ƙasa ce ta gumaka, gumakan da za su haukace da tsoro.
39 C'est pourquoi les animaux sauvages du désert avec les loups y habiteront. Les autruches y habiteront. Elle ne sera plus habitée à jamais, Elle ne sera pas non plus vécue de génération en génération.
“Saboda haka halittun hamada da kuraye za su zauna a can, a can kuma mujiya za tă zauna. Ba za a ƙara zauna ko a yi zama a cikinta ba daga tsara zuwa tsara.
40 Comme lorsque Dieu a renversé Sodome, Gomorrhe et ses villes voisines, dit Yahvé, « pour que personne n'y habite, aucun fils de l'homme n'y vivra.
Yadda Allah ya tumɓuke Sodom da Gomorra tare da maƙwabtan garuruwansu,” in ji Ubangiji “haka ma ba wanda zai zauna a can; ba wani da zai zauna a cikinta.
41 « Voici qu'un peuple vient du nord. Une grande nation et de nombreux rois seront suscités des extrémités de la terre.
“Duba! Ga sojoji suna zuwa daga arewa; babbar al’umma da sarakuna masu yawa suna tahowa daga iyakokin duniya.
42 Ils prennent l'arc et la lance. Ils sont cruels, et n'ont aucune pitié. Leur voix gronde comme la mer. Ils montent à cheval, tout le monde dans le tableau, comme un homme à la bataille, contre toi, fille de Babylone.
Suna riƙe da baka da māshi; mugaye ne marasa tausayi. Amonsu ya yi kamar rurin teku yayinda suke hawan dawakansu; suna zuwa kamar mutane a dāgār yaƙi don su fāɗa miki, ya Diyar Babilon.
43 Le roi de Babylone a entendu parler d'eux, et ses mains deviennent faibles. Anguish s'est emparé de lui, des douleurs comme celles d'une femme en travail.
Sarkin Babilon ya ji rahotanni game da su, hannunsa kuma ya yi laƙwas. Wahala ta kama shi, zafi kamar na mace mai naƙuda.
44 Voici que l'ennemi surgit comme un lion. des fourrés du Jourdain contre la forte habitation; car je les ferai fuir soudainement. Celui qui sera choisi, Je le nommerai à ce poste, car qui est comme moi? Qui me fixera une heure? Qui est le berger qui peut se tenir devant moi? »
Kamar zaki mai haurawa daga kurmin Urdun zuwa wurin kiwo mai dausayi, zan fafare Babilon daga ƙasan nan da nan. Wane ne zaɓaɓɓen da zan naɗa domin wannan? Wane ne kamar ni da zai kalubalance ni? Kuma wanda makiyayi zai iya tsaya gāba da ni?”
45 C'est pourquoi, écoutez le conseil de Yahvé qu'il a pris contre Babylone; et ses objectifs qu'il s'est proposé contre le pays des Chaldéens: Ils vont sûrement les traîner loin, même les petits du troupeau. Il fera de leur habitation une désolation.
Saboda haka, ku ji abin da Ubangiji ya shirya a kan Babilon, abin da ya nufa gāba da ƙasar Babiloniyawa. Za a kwashe ƙananan garkensu a tafi; zai hallaka wurin kiwonsu sarai saboda su.
46 La terre tremble au bruit de la prise de Babylone. Le cri est entendu parmi les nations.
Da jin an ci Babilon da yaƙi sai duniya ta girgiza; za a ji kukanta cikin al’ummai.

< Jérémie 50 >