< Jérémie 46 >

1 Parole de Yahvé adressée à Jérémie, le prophète, concernant les nations.
Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da al’ummai.
2 Sur l'Égypte: sur l'armée de Pharaon Néco, roi d'Égypte, qui était près du fleuve Euphrate, à Carkemish, et que Nebucadnetsar, roi de Babylone, battit la quatrième année de Jojakim, fils de Josias, roi de Juda.
Game da Masar. Ga saƙo game da sojojin Fir’auna Neko sarkin Masar, wanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya ci da yaƙi a Karkemish a Kogin Yuferites a shekara ta huɗu ta Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda.
3 « Préparez la cuirasse et le bouclier, et s'approcher de la bataille!
“Ku shirya garkuwoyinku, manya da ƙanana, ku kuma fito don yaƙi!
4 Harnachez les chevaux, et levez-vous, cavaliers, et mettez-vous debout avec vos casques. Polissez les lances, mettre les manteaux de courrier.
Ku shirya dawakai, ku sa musu sirdi! Ku tsaya a wurarenku saye da hulunan kwano a kai! Ku wasa māsunku, ku yafa kayan yaƙinku!
5 Pourquoi l'ai-je vu? Ils sont consternés et se retournent. Leurs puissants sont battus, ont fui en hâte, et ne regardez pas en arrière. La terreur est de tous les côtés, » dit Yahvé.
Me nake gani? Sun tsorata, suna ja da baya, an ci jarumawansu. Suna gudu da sauri ba waiwayawa, akwai razana a kowane gefe,” in ji Ubangiji.
6 « Ne laisse pas le rapide s'enfuir, ni l'homme fort ne s'échappera. Au nord, près du fleuve Euphrate ils ont trébuché et sont tombés.
“Masu saurin gudu ba sa iya gudu haka ma masu ƙarfi ba sa iya kuɓuta. A arewa ta Kogin Yuferites sun yi tuntuɓe sun fāɗi.
7 « Qui est celui qui s'élève comme le Nil? comme des rivières dont les eaux déferlent?
“Wane ne wannan mai tashi kamar Nilu, kamar koguna masu tafasar ruwaye?
8 L'Égypte s'élève comme le Nil, comme des rivières dont les eaux se déchaînent. Il dit: « Je me lèverai. Je couvrirai la terre. Je détruirai les villes et leurs habitants.
Masar tana tashi kamar Nilu, kamar koguna masu tafasa. Tana cewa, ‘Zan tashi in rufe duniya; zan hallakar da birane da kuma mutanensu.’
9 Montez, chevaux! Ragez, chars! Que les hommes forts sortent: Cush et Put, qui s'occupent du bouclier; et les Ludim, qui manient et plient l'arc.
Ku yi sukuwar hauka, ya dawakai! Ku tashi a guje, ya mahayan kekunan yaƙi! Ku yi ta fitowa, ya jarumawa, mutanen Kush da kuma Ludim masu riƙon garkuwoyi, mutanen Lidiya, masu iya jan baka.
10 Car ce jour-là est celui du Seigneur, Yahvé des armées, un jour de vengeance, pour qu'il se venge de ses adversaires. L'épée dévorera et sera rassasiée, et s'abreuvera de leur sang; car le Seigneur, Yahvé des Armées, a un sacrifice dans le pays du nord, près du fleuve Euphrate.
Amma wannan rana ta Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ranar ɗaukar fansa, gama ɗaukar fansa a kan maƙiyansa. Takobi zai yi ta ci sai ya gamsu, sai ya kashe ƙishirwansa da jini. Gama Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, zai miƙa hadaya a ƙasar arewa kusa da Kogin Yuferites.
11 Monte en Galaad, et prends du baume, vierge fille d'Égypte. Vous utilisez beaucoup de médicaments en vain. Il n'y a pas de guérison pour vous.
“Ki haura Gileyad ki samo magani, Ya Budurwa’Yar Masar. Amma kin riɓanya magani a banza; ba magani dominki.
12 Les nations ont entendu parler de ta honte, et la terre est pleine de ton cri; car le puissant a trébuché contre le puissant, ils tombent tous les deux ensemble. »
Al’ummai za su ji game da kunyar da kika sha; kukanki zai cika duniya. Jarumi zai yi tuntuɓe a kan wani; dukansu biyu za su fāɗi tare.”
13 La parole que Yahvé adressa à Jérémie, le prophète, sur la manière dont Nabuchodonosor, roi de Babylone, devait venir et frapper le pays d'Égypte:
Ga saƙon da Ubangiji ya yi wa Irmiya annabi game da zuwan Nebukadnezzar sarkin Babilon don yă yaƙi Masar.
14 « Déclarez en Égypte, publier à Migdol, et publier à Memphis et à Tahpanhes; dire: « Levez-vous et préparez-vous, car l'épée a dévoré autour de toi.
“Ka yi shelar wannan a Masar, ka kuma furta shi a Migdol; ka yi shelarsa kuma a Memfis da Tafanes. ‘Ku ɗauki matsayinku ku kuma shirya, gama takobi na cin waɗanda suke kewaye da ku.’
15 Pourquoi vos forces sont-elles balayées? Ils ne sont pas restés debout, car Yahvé les a poussés.
Me zai sa a wulaƙanta jarumawanka haka? Ba za su iya tsayawa ba, gama Ubangiji zai ture su ƙasa.
16 Il a fait trébucher beaucoup de gens. Oui, ils sont tombés l'un sur l'autre. Ils ont dit: « Levez-vous! Retournons auprès des nôtres, et à la terre de notre naissance, de l'épée oppressive.
Za su yi ta tuntuɓe; za su fāɗi akan juna. Za su ce, ‘Mu tashi, mu koma zuwa wurin mutanenmu da kuma ƙasashenmu, daga takobin masu danniya.’
17 Ils criaient: « Pharaon, roi d'Égypte, n'est qu'un bruit; il a laissé passer le temps qui lui était imparti ».
A can za su tā da murya su ce, ‘Fir’auna sarkin Masar mai yawan surutu ne kawai; ya bar zarafi ya wuce masa.’
18 « Je suis vivant », dit le roi, dont le nom est Yahvé des Armées, « sûrement comme le Thabor parmi les montagnes, et comme le Carmel au bord de la mer, pour qu'il vienne.
“Muddin ina raye,” in ji Sarki, wanda sunansa ne Ubangiji Maɗaukaki, “wani zai ɓullo wanda yake kamar Tabor a cikin duwatsu, kamar Karmel kusa da teku.
19 Fille qui habite en Égypte, fournissez-vous pour aller en captivité; car Memphis deviendra une désolation, et sera brûlé, sans habitant.
Ku tattara kayanku don shirin zuwa zaman bauta, ku da kuke zama a Masar, gama Memfis za tă zama kufai ta zama kango, babu mazauna.
20 « L'Égypte est une très belle génisse; mais la destruction est venue du nord. Il est arrivé.
“Masar kyakkyawar karsana ce, amma bobuwa tana zuwa a kanta daga arewa.
21 Et ses mercenaires, au milieu d'elle, sont comme des veaux de l'étable, car eux aussi sont retournés en arrière. Ils se sont enfuis ensemble. Ils ne se sont pas levés, car le jour de leur calamité est venu sur eux, le moment de leur visite.
Sojojin da ta yi hayarsu a cikinta suna kamar’yan maruƙa masu kitse. Su ma za su juya su kuma gudu gaba ɗaya, ba za su iya tsayawa ba, gama ranar masifa tana zuwa a kansu, lokacin da za su sha hukunci.
22 Son bruit sera comme celui du serpent, car ils vont marcher avec une armée, et viennent contre elle avec des haches, comme des coupeurs de bois.
Masar za tă yi huci kamar macijin da yake gudu yayinda abokin gāba yana matsowa da ƙarfi; za su fāɗo mata gatura kamar mutanen da suke saran itatuwa.
23 Ils couperont sa forêt, dit Yahvé, « bien qu'il ne puisse pas être fouillé; car ils sont plus nombreux que les sauterelles, et sont innombrables.
Za su sari kurminta,” in ji Ubangiji, “ko da yake yana maƙare da itatuwa. Sun fi fāra yawa, ba su ƙidayuwa.
24 La fille de l'Égypte sera déçue; elle sera livrée entre les mains des gens du nord. »
Za a kunyatar da Diyar Masar, da aka bashe ga mutanen arewa.”
25 Yahvé des armées, le Dieu d'Israël, dit: « Voici que je vais punir Amon de No, et Pharaon, et l'Égypte, avec ses dieux et ses rois, même Pharaon, et ceux qui se confient en lui.
Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Ina gab da kawo hukunci a kan allahn Amon na Tebes, a kan Fir’auna, a kan Masar da allolinta da sarakunanta, da kuma a kan waɗanda suka dogara ga Fir’auna.
26 Je les livrerai entre les mains de ceux qui en veulent à leur vie, entre les mains de Nebucadnetsar, roi de Babylone, et entre les mains de ses serviteurs. Ensuite, elle sera habitée, comme aux jours d'autrefois, dit Yahvé.
Zan ba da su ga waɗanda suke neman ransu, ga Nebukadnezzar sarkin Babilon da fadawansa. Amma daga baya, Masar za tă kasance da mazauna kamar dā,” in ji Ubangiji.
27 « Mais n'aie pas peur, Jacob, mon serviteur. Ne sois pas consterné, Israël; car, voici, je vous sauverai de loin, et ta descendance du pays de leur captivité. Jacob reviendra, et sera tranquille et à l'aise. Personne ne lui fera peur.
“Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana; kada ka karai, ya Isra’ila. Tabbatacce zan cece ka daga wuri mai nisa, zuriyarka daga ƙasar bautarsu. Yaƙub zai sāke kasance cikin salama, rai kwance, babu kuma wanda zai sa ya ji tsoro.
28 N'aie pas peur, mon serviteur Jacob, dit Yahvé, « car je suis avec vous; car je ferai disparaître toutes les nations où je vous ai chassés, mais je n'en finirai pas avec vous, mais je vais vous corriger sur mesure, et ne vous laissera en aucun cas impuni. »
Kada ka ji tsoro, ya Yaƙub bawana, gama ina tare da kai,” in ji Ubangiji. “Ko da na hallaka dukan al’ummai sarai inda na kora ka, ba zan hallaka ka sarai ba. Zan hore ka amma da adalci kaɗai; ba zan bar ka ba hukunci ba.”

< Jérémie 46 >