< Jérémie 37 >

1 Sédécias, fils de Josias, régna comme roi à la place de Conias, fils de Jojakim, que Nebucadnetsar, roi de Babylone, avait établi roi dans le pays de Juda.
Nebukadnezzar sarkin Babilon ya naɗa Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda; ya yi mulki a madadin Yehohiyacin ɗan Yehohiyakim.
2 Mais ni lui, ni ses serviteurs, ni le peuple du pays n'écoutèrent les paroles de Yahvé, qu'il avait prononcées par le prophète Jérémie.
Shi da masu yin masa hidima da mutanen ƙasar ba su kula da maganar da Ubangiji ya yi ta wurin Irmiya annabi ba.
3 Le roi Sédécias envoya Jehucal, fils de Shelemia, et Sophonie, fils de Maaséja, le prêtre, au prophète Jérémie, pour lui dire: « Priez maintenant Yahvé notre Dieu pour nous. »
Sai sarki Zedekiya ya aiki Yehukal ɗan Shelemiya tare da firist nan Zefaniya ɗan Ma’asehiya da wannan saƙo cewa, “Ina roƙonka ka yi addu’a ga Ubangiji Allahnmu saboda mu.”
4 Or Jérémie entrait et sortait au milieu du peuple, car on ne l'avait pas mis en prison.
To, fa, Irmiya ya sami’yancin kai da kawowa a cikin mutane, gama ba a riga an sa shi a kurkuku ba.
5 L'armée de Pharaon était sortie d'Égypte; et lorsque les Chaldéens qui assiégeaient Jérusalem en eurent vent, ils se retirèrent de Jérusalem.
Sojojin Fir’auna suka fita daga Masar, sa’ad da Babiloniyawa waɗanda suke ƙawanya wa Urushalima suka ji labari game da su, sai suka janye daga Urushalima.
6 Alors la parole de Yahvé fut adressée au prophète Jérémie, en ces termes:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya annabi cewa,
7 « Yahvé, le Dieu d'Israël, dit: Tu diras au roi de Juda, qui t'a envoyé vers moi pour me consulter: « Voici l'armée de Pharaon qui est venue à ton secours: « Voici que l'armée de Pharaon, qui est sortie pour te secourir, retournera en Égypte dans son pays.
“Ga abin da Ubangiji, Allah na Isra’ila, yana cewa ka faɗa wa sarkin Yahuda, wanda ya aika a neme ni cewa, ‘Sojojin Fir’aunan da suka fito su taimake ka, za su koma ƙasarsu, Masar.
8 Les Chaldéens reviendront et combattront cette ville. Ils la prendront et la brûleront par le feu. »''
Sa’an nan Babiloniyawa za su koma su yaƙi wannan birni su ci ta su kuma ƙone shi.’
9 « Yahvé dit: « Ne vous faites pas d'illusions en disant: « Les Chaldéens s'éloigneront de nous », car ils ne s'éloigneront pas.
“Ga abin da Ubangiji yana cewa, kada ku ruɗe kanku, kuna tsammani, ‘Tabbatacce Babiloniyawa sun bar mu.’ Ba za su bari ba!
10 Car si vous aviez frappé toute l'armée des Chaldéens qui vous combattent, et qu'il ne restât parmi eux que des blessés, chacun se lèverait dans sa tente et brûlerait cette ville par le feu.'"
Ko da a ce za ku ci dukan sojojin Babiloniyawan da suke yaƙi da ku har raunana ne kawai aka bari a tentunansu, za su fito su ƙone wannan birni.”
11 Lorsque l'armée des Chaldéens se fut retirée de Jérusalem par crainte de l'armée de Pharaon,
Bayan sojojin Babiloniyawa suka janye daga Urushalima saboda sojojin Fir’auna,
12 Jérémie sortit de Jérusalem pour aller au pays de Benjamin, afin d'y recevoir sa part, au milieu du peuple.
sai Irmiya ya bar birnin don yă je yankin Benyamin ya sami rabon mallaka a cikin mutane a can.
13 Lorsqu'il fut à la porte de Benjamin, il y avait là un chef de la garde, nommé Irija, fils de Shelemia, fils de Hanania, qui saisit Jérémie, le prophète, en disant: « Tu passes aux Chaldéens! »
Amma sa’ad da ya kai Ƙofar Benyamin, sai hafsa mai tsaro, wanda ake kira Iriya ɗan Shelemiya, ɗan Hananiya, ya kama shi ya kuma ce, “Kana gudu daga Babiloniyawa ne!”
14 Jérémie dit alors: « C'est faux! Je ne fais pas défection aux Chaldéens. » Mais il ne l'écouta pas; alors Irija se saisit de Jérémie, et l'amena aux princes.
Sai Irmiya ya ce, “Ba gaskiya ba ce, ba na gudu daga Babiloniyawa.” Amma Iriya bai saurare shi ba; a maimako, ya kama Irmiya ya kawo shi wurin fadawa.
15 Les princes s'irritèrent contre Jérémie, le frappèrent et le mirent en prison dans la maison de Jonathan, le scribe, car ils avaient fait de cette maison une prison.
Suka yi fushi da Irmiya suka sa aka yi masa dūka aka kuma jefa shi cikin kurkuku a gidan Yonatan magatakarda, gama an mai da gidansa ya zama kurkuku.
16 Lorsque Jérémie fut entré dans le cachot et dans les cellules, et que Jérémie y fut resté plusieurs jours,
Aka sa Irmiya a can cikin kurkuku, inda ya kasance kwanaki masu yawa.
17 le roi Sédécias l'envoya chercher et le fit sortir. Le roi l'interrogea secrètement dans sa maison: « Y a-t-il une parole de Yahvé? » Jérémie a dit: « Il y en a un. » Il a aussi dit: « Vous serez livrés aux mains du roi de Babylone. »
Sa’an nan Sarki Zedekiya ya aika a kawo shi aka kuma kawo shi fada, inda ya tambaye shi a kaɗaice ya ce, “Akwai wata magana daga Ubangiji?” Irmiya ya amsa ya ce, “I, za a ba da kai ga sarkin Babilon.”
18 Jérémie dit au roi Sédécias: « En quoi ai-je péché contre toi, contre tes serviteurs ou contre ce peuple, pour que tu me mettes en prison?
Sai Irmiya ya ce wa Sarki Zedekiya, “Wane laifi na yi maka ko fadawanka ko kuwa wannan mutane, da ka sa aka jefa ni cikin kurkuku?
19 Où sont maintenant tes prophètes qui t'ont prophétisé en disant: Le roi de Babylone ne viendra pas contre toi ni contre ce pays?
Ina annabawanka waɗanda suka yi maka annabci suna cewa, ‘Sarkin Babilon ba zai yaƙe ka ko wannan ƙasa ba’?
20 Écoute maintenant, mon seigneur le roi, et permets que ma supplique soit présentée devant toi, afin que tu ne me fasses pas retourner dans la maison de Jonathan, le scribe, de peur que je n'y meure. »
Amma yanzu, ranka yă daɗe, sarkina, ka saurara. Bari in kawo kukata a gabanka. Kada ka mai da ni gidan Yonatan magatakarda, in ba haka zan mutu a can.”
21 Alors le roi Sédécias donna ses ordres, et on enferma Jérémie dans la cour des gardes. On lui donna chaque jour une miche de pain de la rue des boulangers, jusqu'à ce qu'il n'y ait plus de pain dans la ville. Jérémie resta ainsi dans la cour des gardes.
Sarki Zedekiya ya yi umarni a ajiye Irmiya a sansanin matsara a kuma ba shi burodi daga titin masu gashin burodi kowace rana sai duka burodi a birnin ya ƙare. Saboda haka Irmiya ya zauna a sansanin matsara.

< Jérémie 37 >