< Jérémie 35 >
1 La parole qui fut adressée à Jérémie de la part de Yahvé, au temps de Jojakim, fils de Josias, roi de Juda, en ces termes:
Ga maganar da ta zo wa Irmiya daga wurin Ubangiji a lokacin mulkin Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda.
2 « Va à la maison des Rechabites, parle-leur, fais-les entrer dans la maison de Yahvé, dans l'une des chambres, et donne-leur du vin à boire. »
“Ka tafi wurin iyalin Rekabawa ka gayyace su su zo a ɗaya daga cikin ɗakunan da suke gefe a gidan Ubangiji ka kuma ba su ruwan inabi su sha.”
3 Je pris Jaazania, fils de Jérémie, fils de Habazzinia, avec ses frères, tous ses fils, et toute la maison des Récabites;
Sai na tafi don in kawo Ya’azaniya ɗan Irmiya, ɗan Habazziniya, da’yan’uwansa da kuma dukan’ya’yansa maza, dukan iyalin Rekabawa.
4 et je les fis entrer dans la maison de l'Éternel, dans la chambre des fils de Hanan, fils d'Igdalia, homme de Dieu, qui était près de la chambre des princes, au-dessus de la chambre de Maaséja, fils de Schallum, gardien du seuil.
Na kawo su cikin gidan Ubangiji, a cikin ɗakin’ya’yan Hanan ɗan Igdaliya maza mutumin Allah. Ɗakin ne kusa da ɗakin fadawa, wanda yake bisa na Ma’asehiya ɗan Shallum mai tsaron ƙofa.
5 Je plaçai devant les fils de la maison des Récabites des coupes pleines de vin et des gobelets, et je leur dis: « Buvez du vin! »
Sai na ajiye ƙwarya cike da ruwan inabi da waɗansu kwaf a gaban iyalin Rekabawan na kuma ce musu, “Ku sha ruwan inabin.”
6 Mais ils dirent: « Nous ne boirons pas de vin, car Jonadab, fils de Rechab, notre père, nous a donné cet ordre: « Vous ne boirez pas de vin, ni vous ni vos enfants, à jamais.
Amma sai suka amsa suka ce, “Ba ma shan ruwan inabi, domin kakanmu Yehonadab ɗan Rekab ya umarce mu cewa, ‘Ko ku, ko zuriyarku kada ku sha ruwan inabi.
7 Vous ne construirez pas de maison, vous ne sèmerez pas de graines, vous ne planterez pas de vigne et vous n'en aurez pas; mais tous vos jours, vous habiterez sous des tentes, afin de vivre longtemps dans le pays où vous vivez en nomades.
Haka kuma ba za ku gina gidaje, ku dasa iri ko ku nome gonakin inabi ba; kada ku kasance da wani daga cikin waɗannan abubuwa, amma dole kullum ku zauna a tentuna. Ta haka za ku yi dogon rai a cikin ƙasar baƙuncinku.’
8 Nous avons obéi à la voix de Jonadab, fils de Rechab, notre père, dans tout ce qu'il nous a ordonné, de ne pas boire de vin toute notre vie, ni nous, ni nos femmes, ni nos fils, ni nos filles,
Mun yi biyayya da kome da kakanmu Yehonadab ɗan Rekab ya umarce mu. Mu ko matanmu ko’ya’yanmu maza da mata ba mu taɓa shan ruwan inabi ba
9 et de ne pas nous construire de maisons pour y habiter. Nous n'avons ni vigne, ni champ, ni semence;
ba mu kuma gina gidaje mu zauna a ciki ba ko mu yi gonakin inabi, gonaki ko hatsi ba.
10 mais nous avons habité sous des tentes, et nous avons obéi et fait tout ce que Jonadab, notre père, nous avait ordonné.
Mun yi rayuwarmu a cikin tentuna mun kuma yi biyayya ƙwarai da kowane abin da kakanmu Yehonadab ya umarce mu.
11 Mais lorsque Nabuchodonosor, roi de Babylone, est monté dans le pays, nous avons dit: « Venez! Allons à Jérusalem, par crainte de l'armée des Chaldéens et par crainte de l'armée des Syriens; ainsi nous habiterons à Jérusalem.'"
Amma da Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kawo wa ƙasan nan hari, sai muka ce, ‘Ku zo, dole mu tafi Urushalima don mu tsira daga Babiloniyawa da kuma sojojin Arameyawa.’ Saboda haka ne muke a Urushalima.”
12 Alors la parole de Yahvé fut adressée à Jérémie, en ces mots:
Sai maganar Ubangiji ta zo wa Irmiya cewa,
13 Yahvé des armées, le Dieu d'Israël, dit: « Va dire aux hommes de Juda et aux habitants de Jérusalem: « Ne recevrez-vous pas l'instruction d'écouter mes paroles? » dit Yahvé.
“Ga abin da Ubangiji, Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa ka tafi ka faɗa wa mutanen Yahuda da kuma mutanen Urushalima cewa, ‘Ba za ku koyi darasi ku kuma yi biyayya da maganata ba?’ In ji Ubangiji.
14 « Les paroles de Jonadab, fils de Réchab, qui avait ordonné à ses fils de ne pas boire de vin, se sont accomplies; et jusqu'à ce jour, ils n'en boivent pas, car ils obéissent au commandement de leur père; mais moi, je vous ai parlé, je me suis levé de bonne heure et j'ai parlé, et vous ne m'avez pas écouté.
‘Yehonadab ɗan Rekab ya umarci’ya’yansa maza kada su sha ruwan inabi sun kuma kiyaye wannan umarni. Har yă zuwa yau ba sa shan ruwan inabi, domin sun yi biyayya da umarnin kakansu. Amma na yi muku magana sau da sau, duk da haka ba ku yi biyayya ba.
15 J'ai aussi envoyé vers vous tous mes serviteurs les prophètes, je me suis levé de bonne heure et je les ai envoyés, en disant: « Que chacun de vous revienne maintenant de sa mauvaise voie, qu'il corrige ses actions, et qu'il n'aille pas après d'autres dieux pour les servir. Vous habiterez alors dans le pays que j'ai donné à vous et à vos pères. » Mais vous n'avez pas prêté l'oreille et vous ne m'avez pas écouté.
Sau da sau na aika dukan bayina annabawa gare ku. Suka ce, “Kowannenku ya juyo daga mugayen hanyoyinsa ya sabunta ayyukansa; kada yă bi waɗansu alloli don yă bauta musu. Ta haka za ku zauna a cikin ƙasar da na ba ku da kuma kakanninku.” Amma ba ku saurara ba, ba ku kuwa ji ni ba.
16 Les fils de Jonadab, fils de Récab, ont exécuté le commandement que leur père leur avait donné, mais ce peuple ne m'a pas écouté.
Zuriyar Yehonadab ɗan Rekab sun yi biyayya da umarnin da kakansu ya ba su, amma waɗannan mutane ba su yi mini biyayya ba.’
17 « C'est pourquoi Yahvé, le Dieu des armées, le Dieu d'Israël, dit: « Voici que je vais faire venir sur Juda et sur tous les habitants de Jérusalem tous les malheurs que j'ai prononcés contre eux, parce que je leur ai parlé et qu'ils n'ont pas écouté, parce que je les ai appelés et qu'ils n'ont pas répondu. »"
“Saboda haka, ga abin da Ubangiji Allah Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Ku saurara! Zan kawo wa Yahuda da kuma kowane mutumin da yake zama a Urushalima kowace masifar da na ambata a kansu. Na yi musu magana, amma ba su saurara ba; na kira su, amma ba su amsa ba.’”
18 Jérémie dit à la maison des Rechabites: « L'Éternel des armées, le Dieu d'Israël, dit: « Parce que vous avez obéi au commandement de Jonadab, votre père, que vous avez observé toutes ses ordonnances et que vous avez fait tout ce qu'il vous a commandé,
Sai Irmiya ya ce wa iyalin Rekabawa, “Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Kun yi biyayya da umarnin kakanku Yehonadab kuka kuma kiyaye dukan umarnansa kuka yi kome bisa ga tsari.’
19 l'Éternel des armées, le Dieu d'Israël, dit: « Jonadab, fils de Rechab, ne manquera pas d'un homme pour se tenir devant moi à jamais ».
Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, ‘Yehonadab ɗan Rekab ba zai taɓa rasa mutumin da zai yi mini hidima ba.’”