< Jérémie 27 >

1 Au commencement du règne de Jojakim, fils de Josias, roi de Juda, cette parole fut adressée à Jérémie de la part de Yahvé, en ces termes:
A farkon sarautar Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda, wannan magana ta zo wa Irmiya daga Ubangiji.
2 Yahvé me dit: « Fais des liens et des barres, et mets-les sur ton cou.
Ga abin da Ubangiji ya ce mini, “Ka yi karkiyar itace da maɗaurai ka ɗaura a wuyanka.
3 Puis envoie-les au roi d'Édom, au roi de Moab, au roi des enfants d'Ammon, au roi de Tyr et au roi de Sidon, par la main des messagers qui viennent à Jérusalem auprès de Sédécias, roi de Juda.
Sa’an nan ka aika da saƙo zuwa wurin sarakunan Edom, Mowab, Ammon, Taya da Sidon ta bakin jakadu waɗanda suka zo Urushalima wurin Zedekiya sarkin Yahuda.
4 Donne-leur l'ordre de dire à leurs maîtres: « L'Éternel des armées, le Dieu d'Israël, dit: « Vous direz à vos maîtres:
Ka ba su saƙo wa iyayengijinsu su ce, ‘Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila, yana cewa, “Ku faɗa wa iyayengijinku wannan.
5 J'ai fait la terre, les hommes et les animaux qui sont à la surface de la terre par ma grande puissance et par mon bras étendu. Je la donne à qui me semble bon.
Da ikon mai ƙarfi da kuma hannuna da na miƙa na yi duniya da mutanenta da kuma dabbobin da suke ciki, na ba da ita ga duk wanda na ga dama.
6 Maintenant, j'ai livré toutes ces terres entre les mains de Nabuchodonosor, roi de Babylone, mon serviteur. Je lui ai aussi donné les animaux des champs pour qu'ils le servent.
Yanzu zan ba da dukan ƙasashenku ga bawana Nebukadnezzar sarkin Babilon; zan sa namun jeji ma su bauta masa.
7 Toutes les nations le serviront, lui, son fils et le fils de son fils, jusqu'à ce que vienne le temps de son propre pays. Alors, de nombreuses nations et de grands rois feront de lui leur serviteur.
Dukan al’ummai za su bauta masa da ɗansa da kuma jikansa har sai har lokacin ƙasarsa ya kai; sa’an nan al’ummai masu yawa da kuma manyan sarakuna za su kasance a ƙarƙashinsa.
8 ""« Il arrivera que je punirai la nation et le royaume qui ne serviront pas le même Nabuchodonosor, roi de Babylone, et qui ne mettront pas leur cou sous le joug du roi de Babylone, dit Yahvé, par l'épée, la famine et la peste, jusqu'à ce que je les aie consumés par sa main »".
“‘“Amma fa, duk al’umma ko mulkin da bai bauta wa Nebukadnezzar sarkin Babilon ba bai kuwa rusunar da wuyarsa ga karkiyarsa ba, zan hukunta wannan al’umma da takobi, yunwa da annoba, in ji Ubangiji, har sai na hallaka ta ta wurin hannunsa.
9 Mais toi, n'écoute pas tes prophètes, ni tes devins, ni tes songes, ni tes devins, ni tes sorciers, qui te disent: « Tu ne serviras pas le roi de Babylone »;
Saboda haka kada ku saurari annabawanku, masu dubanku, masu fassarar mafarkanku, bokayenku ko masu maitancinku waɗanda suke ce muku, ‘Ba za ku bauta wa sarkin Babilon ba.’
10 car ils te prophétisent le mensonge, pour t'éloigner de ton pays, afin que je te chasse et que tu périsses.
Suna muku annabcin ƙaryar ne kawai da za tă kau da ku daga ƙasarku; zan kore ku za ku kuwa hallaka.
11 Mais la nation qui mettra son cou sous le joug du roi de Babylone et qui le servira, je la laisserai dans son pays, dit Yahvé, elle le cultivera et y habitera.
Amma duk al’ummar da ta rusuna da wuyarta a ƙarƙashin karkiyar sarkin Babilon ta kuma bauta masa, zan bar al’ummar ta zauna a ƙasarta ta noma ta, ta kuma zauna a can, in ji Ubangiji.”’”
12 Je parlai à Sédécias, roi de Juda, selon toutes ces paroles, et je dis: « Placez votre cou sous le joug du roi de Babylone, servez-le, lui et son peuple, et vivez.
Na ba da wannan saƙo guda ga Zedekiya sarkin Yahuda. Na ce, “Ka rusunar da wuyanka a ƙarƙashin sarkin Babilon; ka bauta masa da kuma mutanensa, za ka kuwa rayu.
13 Pourquoi mourrez-vous, vous et votre peuple, par l'épée, par la famine et par la peste, comme Yahvé l'a dit au sujet de la nation qui ne veut pas servir le roi de Babylone?
Me ya sa kai da mutanenka za ku mutu saboda takobi, yunwa da annoba waɗanda Ubangiji ya yi barazana wa duk al’ummar da ba za tă bauta wa sarkin Babilon ba?
14 N'écoutez pas les paroles des prophètes qui vous disent: « Vous ne servirez pas le roi de Babylone », car ils vous prophétisent le mensonge.
Kada ku saurari maganganun annabawa waɗanda suke ce muku, ‘Ba za ku bauta wa sarkin Babilon ba,’ gama annabcin ƙarya suke muku.
15 Car ce n'est pas moi qui les ai envoyés, dit Yahvé, mais ils prophétisent faussement en mon nom, afin que je vous chasse et que vous périssiez, vous et les prophètes qui vous prophétisent. »
‘Ban aike su ba,’ in ji Ubangiji. ‘Suna annabcin ƙarya ne da sunana. Saboda haka, zan kore ku za ku kuwa hallaka, da ku da kuma annabawan da suke muku annabci.’”
16 J'ai parlé aux prêtres et à tout ce peuple, en disant: « L'Éternel dit: N'écoutez pas les paroles de vos prophètes qui vous prophétisent en disant: « Voici que les ustensiles de la maison de l'Éternel vont bientôt être ramenés de Babylone », car ils vous prophétisent le mensonge.
Sai na ce wa firistoci da dukan waɗannan mutane, “Ga abin da Ubangiji yana cewa, kada ku saurari annabawan da suke cewa, ‘Ba daɗewa ba za a komo da kayan gidan Ubangiji daga Babilon.’ Suna muku annabcin ƙarya ne.
17 Ne les écoutez pas. Servez le roi de Babylone, et vivez. Pourquoi cette ville deviendrait-elle une désolation?
Kada ku saurare su. Ku bauta wa sarkin Babilon, za ku kuwa rayu. Don me wannan birni zai zama kufai?
18 Mais s'ils sont prophètes, et si la parole de l'Éternel est avec eux, qu'ils intercèdent maintenant auprès de l'Éternel des armées, afin que les objets qui restent dans la maison de l'Éternel, dans la maison du roi de Juda et à Jérusalem, n'aillent pas à Babylone.
In su annabawa ne da gaske suna kuma da maganar Ubangiji, bari su roƙi Ubangiji Maɗaukaki ya sa kada a kwashe kayayyakin da suka ragu a gidan Ubangiji da kuma a cikin fadar sarkin Yahuda da kuma cikin Urushalima a kai Babilon.
19 Car l'Éternel des armées dit, au sujet des colonnes, de la mer, des bases et du reste des ustensiles qui sont restés dans cette ville,
Gama ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa game da ginshiƙai, kwatarniya, da dakalai, da sauran kayayyaki da aka bar su a birnin nan,
20 et que Nebucadnetsar, roi de Babylone, n'a pas pris quand il emmena captif Jeconia, fils de Jehoïakim, roi de Juda, de Jérusalem à Babylone, et tous les nobles de Juda et de Jérusalem-
waɗanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya kwashe sa’ad da ya kame Yekoniya ɗan Yehohiyakim sarkin Yahuda zuwa zaman bauta daga Urushalima zuwa Babilon tare da dukan manyan mutanen Yahuda da Urushalima,
21 oui, Yahvé des armées, le Dieu d'Israël, dit au sujet des objets qui restent dans la maison de Yahvé, dans la maison du roi de Juda et à Jérusalem:
I, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki, Allah na Isra’ila yana cewa game da abubuwan da aka bari a gidan Ubangiji da kuma a cikin fadar sarkin Yahuda da Urushalima,
22 'Ils seront transportés à Babylone, et ils y resteront jusqu'au jour où je les visiterai, dit Yahvé; alors je les ferai remonter et je les rétablirai dans ce lieu'.'"
‘Za a kwashe su zuwa Babilon a can kuwa za su kasance sai ranar da na neme su,’ in ji Ubangiji. ‘Sa’an nan zan komo da su in maido da su wannan wuri.’”

< Jérémie 27 >