< Jérémie 17 >

1 « Le péché de Juda est écrit avec une plume de fer, et avec la pointe d'un diamant. Elle est gravée sur la tablette de leur cœur, et sur les cornes de vos autels.
“An rubuta zunubin Yahuda da alƙalamin ƙarfe, an rubuta da tsinin dutse, a kan allunan zukatansu da kuma a kan ƙahonin bagadansu.
2 Même leurs enfants se souviennent de leurs autels et leurs mâts d'Ashérah près des arbres verts sur les hautes collines.
Har’ya’yansu ma sun tuna bagadansu da ginshiƙan Asheransu kusa da itatuwa masu duhuwa da kuma a kan tuddai masu tsayi.
3 Ma montagne dans le champ, Je donnerai vos biens et tous vos trésors en pillage, et tes hauts lieux, à cause du péché, dans tout ton territoire.
Dutsena a ƙasar da dukiyarku na ƙasar da dukan arzikinku za a ba da su ganima, tare da masujadanku na kan tuddai, saboda zunubi ko’ina a ƙasarku.
4 Vous, même de vous-mêmes, vous abandonnerez l'héritage que je vous ai donné. Je vous ferai servir vos ennemis dans un pays que vous ne connaissez pas, car tu as allumé dans ma colère un feu qui brûlera à jamais. »
Saboda laifinku za ku rasa gādon da na ba ku. Zan bautar da ku ga abokan gābanku a ƙasar da ba ku sani ba, domin kun husata ni, zai kuwa ci har abada.”
5 Yahvé dit: « Maudit soit l'homme qui se confie en l'homme, s'appuie sur la force de la chair, et dont le cœur s'éloigne de Yahvé.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “La’ananne ne mutumin da yake dogara ga mutum, wanda ya dogara ga jiki don ƙarfi wanda kuma zuciyarsa ta juya wa Ubangiji baya.
6 Car il sera comme un buisson dans le désert, et ne verront pas quand le bien arrive, mais habitera les lieux desséchés du désert, une terre salée inhabitée.
Zai zama kamar ɗan kurmi a ƙasar da take kango; ba za su ga arziki sa’ad da ya zo ba. Za su zauna a busassun wuraren hamada, a cikin ƙasar gishiri inda ba kowa.
7 « Heureux l'homme qui se confie en Yahvé, et dont la confiance est en Yahvé.
“Amma mai albarka ne mutumin da yake dogara ga Ubangiji, wanda ƙarfin halinsa yana daga Ubangiji.
8 Car il sera comme un arbre planté près des eaux, qui étend ses racines près de la rivière, et n'aura pas peur quand la chaleur viendra, mais sa feuille sera verte, et ne sera pas inquiété l'année de la sécheresse. Il ne cessera pas de donner des fruits.
Za su zama kamar itacen da aka dasa kusa da ruwa wanda ya miƙa saiwoyinsa zuwa cikin rafi. Ba ya jin tsoro sa’ad da zafi ya zo; ganyayensa kullum kore suke. Ba shi da damuwa a shekarar fări ba ya taɓa fasa ba da’ya’ya.”
9 Le cœur est trompeur par-dessus tout. et il est extrêmement corrompu. Qui peut le savoir?
Zuciya ta fi kome ruɗu ta fi ƙarfin warkewa. Wa zai iya gane ta?
10 « Moi, Yahvé, je sonde l'esprit. J'essaie le cœur, de rendre à chacun selon ses voies, selon le fruit de ses actions. »
“Ni Ubangiji nakan bincike zuciya in gwada tunani, don in sāka wa kowane mutum bisa ga halinsa, bisa ga ayyukansa.”
11 Comme la perdrix qui s'assied sur des œufs qu'elle n'a pas pondus, ainsi est celui qui obtient des richesses, et non par droit. Au milieu de ses jours, ils le quitteront. A sa fin, il sera un imbécile.
Kamar makwarwar da ta kwanta a kan ƙwan da ba ita ta zuba ba haka yake da mutumin da ya sami arziki a hanyar da ba daidai ba. A tsakiyar rayuwarsa za su rabu da shi, a ƙarshe kuma zai zama wawa.
12 Un trône glorieux, placé en haut dès le commencement, est le lieu de notre sanctuaire.
Kursiyi mai daraja, da aka ɗaukaka tun daga farko, shi ne wuri mai tsarkinmu.
13 Yahvé, l'espoir d'Israël, tous ceux qui t'abandonnent seront déçus. Ceux qui s'éloignent de moi seront inscrits sur la terre, parce qu'ils ont abandonné Yahvé, la source d'eau vive.
Ya Ubangiji, sa zuciyar Isra’ila, duk waɗanda suka rabu da kai za su sha kunya. Waɗanda suka juya maka baya za a rubuta su a ƙura domin sun yashe Ubangiji, maɓulɓular ruwan rai.
14 Guéris-moi, Yahvé, et je serai guéri. Sauve-moi, et je serai sauvé; car tu es ma louange.
Ka warkar da ni, ya Ubangiji, zan kuwa warke; ka cece ni zan kuwa cetu, gama kai ne nake yabo.
15 Voici, ils me demandent, « Où est la parole de Yahvé? Qu'il s'accomplisse maintenant. »
Sun riƙa ce mini, “Ina maganar Ubangiji take? Bari tă cika yanzu!”
16 Quant à moi, je ne me suis pas empressé d'être un berger après vous. Je n'ai pas désiré le jour malheureux. Tu sais. Ce qui est sorti de mes lèvres était devant ton visage.
Ban gudu zaman mai yin maka kiwo ba; ka sani ban marmarin ranan nan ta masifa ba. Abin da ya fito daga leɓunana kuwa, a bayyane suke gare ka.
17 Ne sois pas une terreur pour moi. Tu es mon refuge au jour du malheur.
Kada ka zama mini abin razana; kai ne mafakata a ranar masifa.
18 Que ceux qui me persécutent soient déçus, mais ne me laisse pas être déçu. Qu'ils soient consternés, mais ne me laissez pas être consterné. Faites venir sur eux le jour du malheur, et les détruire doublement.
Bari masu tsananta mini su sha kunya, amma ka kiyaye ni daga shan kunya; bari su tsorata, amma ka kiyaye ni da razana. Ka kawo musu ranar masifa; ka hallaka su da hallaka riɓi biyu.
19 Yahvé m'a dit ceci: « Va te tenir à la porte des enfants du peuple, par laquelle les rois de Juda entrent et par laquelle ils sortent, et à toutes les portes de Jérusalem.
Ga abin da Ubangiji ya ce mini, “Ka je ka tsaya a ƙofar mutane, inda sarakunan Yahuda sukan shiga su fita; ka tsaya kuma a dukan sauran ƙofofin Urushalima.
20 Dis-leur: « Écoutez la parole de Yahvé, rois de Juda, tout Juda et tous les habitants de Jérusalem, qui entrez par ces portes:
Ka ce musu, ‘Ku ji maganar Ubangiji, ku sarakunan Yahuda, da dukan mutanen Yahuda da dukan mazaunan Urushalima waɗanda suke bi ta waɗannan ƙofofi.
21 Yahvé dit: « Prenez garde, ne portez pas de fardeau le jour du sabbat, et ne le faites pas entrer par les portes de Jérusalem.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, ku yi hankali kada ku ɗauki kaya a ranar Asabbaci ko ku shigar da shi ta ƙofofin Urushalima.
22 Ne portez pas de fardeau hors de vos maisons le jour du sabbat. Ne faites pas d'ouvrage, mais sanctifiez le jour du sabbat, comme je l'ai ordonné à vos pères.
Kada ku fitar da kayan gidajenku ko ku yi wani aiki a ranar Asabbaci mai tsarki, yadda na umarci kakanni-kakanninku.
23 Mais ils n'ont pas écouté. Ils n'ont pas prêté l'oreille, mais ils ont raidi leur cou, afin de ne pas entendre et de ne pas recevoir d'instruction.
Duk da haka ba su saurara ba, ba su kuwa mai da hankali ba; suka taurare ba su kuwa saurara ko su karɓi horo ba.
24 Si vous m'écoutez attentivement, dit l'Éternel, vous ne ferez entrer aucun fardeau par les portes de cette ville le jour du sabbat, vous sanctifierez le jour du sabbat et vous ne ferez aucun ouvrage.
Amma in kuka yi hankali kuka yi mini biyayya, in ji Ubangiji, ba ku kuwa shigar da kaya ta ƙofofi a ranar Asabbaci ba, amma kuka kiyaye ranar Asabbaci da tsarki ba tare da yin wani aiki a cikinta ba,
25 Alors entreront par les portes de cette ville des rois et des princes assis sur le trône de David, montés sur des chars et sur des chevaux, eux et leurs princes, les hommes de Juda et les habitants de Jérusalem, et cette ville subsistera à jamais.
sa’an nan sarakuna da suke zama a kursiyin Dawuda za su shiga ta ƙofofin wannan birni tare da fadawansu. Su da fadawansu za su shiga a kan kekunan yaƙi da kuma a kan dawakai, mutanen Yahuda suna musu rakiya tare da waɗanda suke zaune a Urushalima, wannan birni kuwa za tă kasance da mazauna har abada.
26 Ils viendront des villes de Juda et des environs de Jérusalem, du pays de Benjamin, de la plaine, de la montagne et du Midi, apportant des holocaustes, des sacrifices, des offrandes, de l'encens et des sacrifices d'action de grâces à la maison de l'Éternel.
Mutane za su zo daga garuruwan Yahuda da ƙauyukan kewaye da Urushalima, daga iyakar Benyamin da gindin tuddan yamma, daga ƙasar tudu da kuma Negeb, suna kawo hadayun ƙonawa da hadayun gari, sadakokin turare da na godiya zuwa gidan Ubangiji.
27 Mais si vous ne m'écoutez pas pour sanctifier le jour du sabbat, pour ne pas porter de fardeau et entrer aux portes de Jérusalem le jour du sabbat, j'allumerai un feu dans ses portes, et il dévorera les palais de Jérusalem. Il ne s'éteindra pas. »'"
Amma in ba ku yi mini biyayya ba, ba ku kiyaye ranar Asabbaci da tsarki ba, kuka ɗauki wani kaya yayinda kuke shiga ƙofofin Urushalima a ranar Asabbaci, to, sai in cinna wa ƙofofin Urushalima wutar da ba a iya kashewa, tă cinye kagaranta.’”

< Jérémie 17 >