< Isaïe 64 >

1 Oh que tu déchirerais les cieux, que vous descendiez, que les montagnes puissent trembler en ta présence...
Da ma za ka tsage sammai ka sauko, ai, da duwatsu za su yi rawar jiki a gabanka!
2 comme lorsque le feu enflamme les broussailles, et le feu fait bouillir l'eau. Faites connaître votre nom à vos adversaires, pour que les nations tremblent en ta présence!
Kamar sa’ad da wuta takan ci rassa ta sa ruwa ya tafasa, ka sauko ka sanar da sunanka ga abokan gābanka ka kuma sa al’ummai su yi rawan jiki a gabanka!
3 Quand tu as fait des choses géniales que nous n'avions pas cherché, tu es descendu, et les montagnes ont tremblé en ta présence.
Gama sa’ad da ka aikata abubuwan bantsoron da ba mu sa tsammani ba, ka sauko, duwatsu kuma suka yi rawar jiki a gabanka.
4 Car depuis toujours, les hommes n'ont pas entendu, ni perçue par l'oreille, et l'œil n'a pas vu d'autre Dieu que toi, qui travaille pour lui qui l'attend.
Tun fil azal babu wanda ya taɓa ji, babu kunnen da ya gane, babu idon da ya ga wani Allah in ban da kai, wanda ya aikata waɗannan al’amura a madadin waɗanda suke sa zuciya a gare shi.
5 Tu rencontres celui qui se réjouit et qui pratique la justice, ceux qui se souviennent de toi dans tes voies. Voici, tu t'es mis en colère, et nous avons péché. Nous sommes dans le péché depuis longtemps. Serons-nous sauvés?
Kakan taimaki waɗanda suke murnan yin abin da yake daidai, waɗanda sukan tuna da hanyoyinka. Amma sa’ad da muka ci gaba da yin zunubi, kakan yi fushi. Ta yaya za mu sami ceto ke nan?
6 Car nous sommes tous devenus comme un impur, et toute notre justice est comme un vêtement souillé. Nous nous fanons tous comme une feuille; et nos iniquités, comme le vent, nous emportent.
Dukanmu mun zama kamar wanda yake marar tsabta, kuma dukan ayyukanmu masu adalci sun zama kamar ƙazaman tsummoki; duk mun zama kamar busasshen ganye, kamar iska haka zunubanmu sukan share mu.
7 Il n'y a personne qui invoque ton nom, qui s'agite pour s'emparer de vous; car tu nous as caché ta face, et nous ont consumés par nos iniquités.
Babu wanda yake kira bisa sunanka ko ya yi ƙoƙarin riƙe ka; gama ka ɓoye fuskarka daga gare mu ka kuma sa muka lalace saboda zunubanmu.
8 Mais maintenant, Yahvé, tu es notre Père. Nous sommes l'argile et vous êtes notre potier. Nous sommes tous l'œuvre de ta main.
Duk da haka, Ubangiji, kai ne Ubanmu. Mu yumɓu ne, kai kuma mai ginin tukwane; dukanmu aikin hannunka ne.
9 Ne sois pas furieux, Yahvé. Ne te souviens pas à jamais de l'iniquité. Regardez et voyez, nous vous en supplions, nous sommes tous votre peuple.
Kada ka yi fushi fiye da kima, ya Ubangiji; kada ka tuna da zunubanmu har abada. Da ma ka dube mu, muna roƙonka, gama dukanmu mutanenka ne.
10 Vos villes saintes sont devenues un désert. Sion est devenue un désert, Jérusalem une désolation.
Biranenka masu tsarki sun zama hamada; har Sihiyona ma ta zama hamada; Urushalima ta zama kango.
11 Notre sainte et belle maison où nos pères t'ont loué est brûlé par le feu. Tous nos endroits agréables sont détruits.
Haikalinmu mai tsarki da kuma mai daraja, inda kakanninmu suka yabe ka, an ƙone da wuta, kuma dukan abubuwan da muke ƙauna sun lalace.
12 Te retiendras-tu pour ces choses, Yahvé? Allez-vous garder le silence et nous punir très sévèrement?
Bayan dukan wannan, ya Ubangiji, ba za ka yi wani abu ba? Za ka yi shiru ka hore mu fiye da kima?

< Isaïe 64 >