< Isaïe 59 >
1 Voici, la main de Yahvé n'est pas raccourcie au point de ne pas pouvoir sauver; ni son oreille émoussée, qu'elle ne puisse entendre.
Tabbatacce hannun Ubangiji bai kāsa yin ceto ba, kunnensa kuma bai kurmance da zai kāsa ji ba.
2 Mais tes iniquités t'ont séparé de ton Dieu, et vos péchés vous ont caché sa face, pour qu'il n'entende pas.
Amma laifofinku sun raba ku da Allahnku; zunubanku sun ɓoye fuskarsa daga gare ku, saboda kada yă ji.
3 Car vos mains sont souillées de sang, et tes doigts avec l'iniquité. Tes lèvres ont dit des mensonges. Ta langue murmure la méchanceté.
Gama hannuwanku sun ƙazantu da jini, yatsotsinku kuma da alhaki. Leɓunanku suna faɗin ƙarairayi, harshenku kuma yana raɗar mugayen abubuwa.
4 Personne n'intente un procès en justice, et personne ne plaide en vérité. Ils font confiance à la vanité et dire des mensonges. Ils conçoivent des méfaits et donnent naissance à l'iniquité.
Babu wani mai ce a yi adalci; babu wani mai nema a dubi al’amarinsa da mutunci. Sun dogara a gardandamin banza suna ƙarairayi; suna ɗaukar cikin ɓarna, su haifi mugunta.
5 Ils font éclore des œufs de loups et tisser la toile d'araignée. Celui qui mange de leurs œufs meurt; et ce qui est écrasé se transforme en vipère.
Suna ƙyanƙyashe ƙwan kāsā su kuma saƙa yanar gizo-gizo. Duk wanda ya ci ƙwansu zai mutu, kuma sa’ad da ƙwan ya fashe, zai ƙyanƙyashe kububuwa.
6 Leurs toiles ne deviendront pas des vêtements. Ils ne se couvriront pas de leurs œuvres. Leurs œuvres sont des œuvres d'iniquité, et les actes de violence sont entre leurs mains.
Yanar gizo-gizonsu ba amfani don tufa; ba za su iya rufuwa da abin da suka yi ba. Ayyukansu mugaye ne, ayyukan tā da hargitsi kuma suna a hannuwansu.
7 Leurs pieds courent vers le mal, et ils se dépêchent de verser du sang innocent. Leurs pensées sont des pensées d'iniquité. La désolation et la destruction sont sur leur chemin.
Ƙafafunsu sukan gaggauta zuwa aikata zunubi; suna da saurin zub da jini. Tunaninsu mugaye ne; lalaci da hallaka sun shata hanyoyinsu.
8 Ils ne connaissent pas le chemin de la paix; et il n'y a pas de justice dans leurs manières. Ils se sont tracés des chemins tortueux; celui qui y entre ne connaît pas la paix.
Ba su san hanyar salama ba; babu adalci a hanyoyinsu. Sun mai da su karkatattun hanyoyi; babu wanda zai yi tafiya a kansu ya sami salama.
9 C'est pourquoi la justice est loin de nous, et la justice ne nous rattrape pas. Nous cherchons la lumière, mais nous voyons les ténèbres; pour la clarté, mais nous marchons dans l'obscurité.
Saboda haka gaskiya ta yi nisa da mu, adalci kuma ba ya kaiwa gare mu. Muna neman haske, sai ga duhu; muna neman haske, sai muka yi ta tafiya cikin baƙin inuwa.
10 Nous tâtonnons vers le mur comme des aveugles. Oui, nous tâtonnons comme ceux qui n'ont pas d'yeux. Nous trébuchons à midi comme si c'était le crépuscule. Parmi ceux qui sont forts, nous sommes comme des hommes morts.
Kamar makafi, sai lallubar bango muke yi, muna lallubawar hanyarmu kamar marasa idanu. Da tsakar rana muna tuntuɓe sai ka ce wuri ya fara duhu; cikin ƙarfafa, mun zama kamar matattu.
11 Nous rugissons tous comme des ours et gémissent tristement comme des colombes. Nous cherchons la justice, mais il n'y en a pas, pour le salut, mais il est loin de nous.
Muna gurnani kamar beyar; muna ta ƙugi kamar kurciyoyi. Muna ta neman adalci amma ina; mun nemi fansa, amma yana can da nisa.
12 Car nos transgressions se sont multipliées devant toi, et nos péchés témoignent contre nous; car nos transgressions sont avec nous, et quant à nos iniquités, nous les connaissons:
Gama laifofinmu suna da yawa a gabanka, zunubanmu kuma suna ba da shaida gāba da mu. Laifofinmu kullum suna a gabanmu, muna kuma sane da laifofinmu,
13 transgressant et reniant Yahvé, et se détourner de notre Dieu, parlant d'oppression et de révolte, en concevant et en prononçant du cœur des paroles mensongères.
tawaye da mūsun Ubangiji, mun juye bayanmu ga Allahnmu, zugawa a yi zalunci da tayarwa, faɗin ƙarairayi da zukatanmu suka shirya.
14 La justice se détourne à reculons, et la droiture se tient loin; car la vérité est tombée dans la rue, et la droiture ne peut pas entrer.
Saboda haka aka kau da yin gaskiya adalci kuma ya tsaya can da nesa; gaskiya ta yi tuntuɓe a tituna, sahihanci ba zai shiga ba.
15 Oui, la vérité fait défaut; et celui qui s'éloigne du mal devient une proie. Yahvé l'a vu, et il était mécontent qu'il n'y ait pas de justice.
Gaskiya ta ɓace gaba ɗaya, kuma duk wanda ya guji mugunta zai zama ganima. Ubangiji ya duba bai kuwa ji daɗi cewa babu adalci ba.
16 Il vit qu'il n'y avait pas d'homme, et s'est étonné qu'il n'y ait pas d'intercesseur. C'est donc son propre bras qui lui a apporté le salut; et sa justice l'a soutenu.
Ya ga cewa babu wani, ya yi mamaki cewa babu wanda zai shiga tsakani; saboda haka hannunsa ya aikata masa ceto, adalcinsa kuma ya raya shi.
17 Il s'est revêtu de la justice comme d'une cuirasse, et un casque de salut sur sa tête. Il a mis des vêtements de vengeance pour se vêtir, et était revêtu de zèle comme d'un manteau.
Ya yafa sulke a matsayin rigar ƙirji, da hulan kwanon ceto a kansa; ya sa rigunan ɗaukar fansa ya kuma nannaɗe kansa da kishi kamar a cikin alkyabba.
18 Selon leurs actes, il remboursera le cas échéant: la colère de ses adversaires, la rétribution de ses ennemis. Il rendra aux îles leur dû.
Bisa ga abin da suka yi, haka za a sāka fushi a kan abokan gābansa ramuwa kuma a kan maƙiyansa; zai sāka wa tsibirai abin da ya dace da su.
19 Ainsi, ils craindront le nom de Yahvé depuis l'occident, et sa gloire dès le lever du soleil; car il viendra comme un torrent impétueux, que le souffle de Yahvé conduit.
Daga yamma, mutane za su ji tsoron Ubangiji, daga mafitar rana kuma, za su girmama ɗaukakarsa. Gama zai zo kamar rigyawa mai tsananin gudu cewa numfashin Ubangiji zai tafi tare da shi.
20 « Un rédempteur viendra à Sion, et à ceux qui se détournent de la désobéissance en Jacob, dit Yahvé.
“Mai fansa zai zo Sihiyona, zuwa waɗanda suke cikin Yaƙub da suka tuba daga zunubansu,” in ji Ubangiji.
21 « Quant à moi, voici mon alliance avec eux, dit Yahvé. « Mon Esprit qui est sur toi et mes paroles que j'ai mises dans ta bouche ne sortiront pas de ta bouche, ni de la bouche de ta descendance, ni de la bouche de la descendance de ta descendance, dit Yahvé, dès maintenant et pour toujours. »
“Game da ni dai, ga alkawarina da su,” in ji Ubangiji. “Ruhuna, wanda yake a kanka, da kuma maganata da na sa a bakinka ba za tă rabu da bakinka ba, ko daga bakunan’ya’yanka ba, ko kuwa daga bakunan zuriyarsu ba daga wannan lokaci zuwa gaba da kuma har abada,” in ji Ubangiji.