< Isaïe 51 >

1 « Écoutez-moi, vous qui poursuivez la justice, vous qui cherchez Yahvé. Regardez la roche dans laquelle vous avez été taillé, et à la carrière d'où vous avez été extrait.
“Ku kasa kunne gare ni, ku da kuna neman adalci kuke kuma neman Ubangiji. Dubi dutse daga inda aka yanke ku da kuma mahaƙar duwatsu inda aka fafe ku;
2 Regarde vers Abraham, ton père, et à Sarah qui t'a porté; car quand il n'était qu'un, je l'ai appelé, Je l'ai béni, et l'a rendu nombreux.
dubi Ibrahim, mahaifinku, da Saratu, wadda ta haife ku. Sa’ad da na kira shi kaɗai ne, na kuma albarkace shi na kuma mai da shi da yawa.
3 Car Yahvé a réconforté Sion. Il a réconforté toutes ses ruines, et a fait de son désert un Eden, et son désert comme le jardin de Yahvé. La joie et l'allégresse se trouveront en eux, l'action de grâce, et la voix de la mélodie.
Tabbatacce Ubangiji zai ta’azantar da Sihiyona zai kuma duba da tausayi a kan dukan kufanta; zai sa hamadanta ta zama kamar Eden, ƙeƙasasshiyar ƙasarta kamar lambun Ubangiji. Za a sami farin ciki da murna a cikinta, godiya da ƙarar rerawa.
4 « Écoutez-moi, mon peuple; et écoute-moi, ma nation, car une loi sortira de moi, et j'établirai ma justice comme une lumière pour les peuples.
“Ku kasa kunne gare ni, mutanena; ku ji ni, al’ummata. Doka za tă fito daga gare ni; shari’ata za tă zama haske ga al’ummai.
5 Ma justice est proche. Mon salut s'est éteint, et mes bras jugeront les peuples. Les îles vont m'attendre, et ils feront confiance à mon bras.
Adalcina na zuwa da sauri, cetona yana a kan hanya, hannuna kuma zai kawo adalci ga al’ummai. Tsibirai za su dube ni su kuma jira da sa zuciya don hannuna.
6 Levez vos yeux vers les cieux, et regarder la terre en dessous; car les cieux s'évanouiront comme de la fumée, et la terre s'usera comme un vêtement. Ses habitants mourront de la même façon, mais mon salut sera éternel, et ma justice ne sera pas abolie.
Ku daga idanunku zuwa sammai ku dubi duniya a ƙasa; sammai za su ɓace kamar hayaƙi, duniya za tă shuɗe kamar riga mazaunanta kuma su mutu kamar ƙudaje. Amma cetona zai dawwama har abada, adalcina ba zai taɓa kāsa ba.
7 « Écoutez-moi, vous qui connaissez la justice, le peuple dans le cœur duquel se trouve ma loi. Ne craignez pas les reproches des hommes, et ne vous laissez pas démonter par leurs insultes.
“Ku ji ni, ku da kuka san abin da yake daidai, ku mutanen da kuke da dokata a zukatanku. Kada ku ji tsoron ba’ar da mutane suke yi ko ku firgita saboda zargin da suke yi.
8 Car la teigne les dévorera comme un vêtement, et le ver les mangera comme de la laine; mais ma justice sera éternelle, et mon salut à toutes les générations. »
Gama asu za su cinye su kamar riga; tsutsotsi za su cinye su kamar ulu. Amma adalcina zai dawwama har abada, cetona har dukan zamanai.”
9 Réveille-toi, réveille-toi, revêts-toi de force, bras de Yahvé! Réveillé, comme dans les jours d'autrefois, les générations des temps anciens. N'est-ce pas vous qui avez coupé Rahab en morceaux, qui a percé le monstre?
Ka tashi, ka tashi! Ka yafa wa kanka ƙarfi, Ya hannun Ubangiji; ka farka, kamar a kwanakin da suka wuce, kamar a zamanai na dā. Ba kai ba ne wanda ya yayyanka Rahab gunduwa-gunduwa, wanda ya soki dodon ruwan nan?
10 N'est-ce pas toi qui as asséché la mer, les eaux de la grande profondeur; qui a fait des profondeurs de la mer un passage pour les rachetés?
Ba kai ba ne ka busar da teku, ka busar da ruwan zurfafa masu girma, wanda ya yi hanya a cikin zurfafan teku saboda fansassu su ƙetare?
11 Les rachetés par Yahvé reviendront, et venez en chantant à Sion. Une joie éternelle sera sur leurs têtes. Ils obtiendront l'allégresse et la joie. Le chagrin et les soupirs s'en iront.
Waɗanda Ubangiji ya fansar za su dawo. Za su shiga Sihiyona da waƙoƙi; madawwamin farin ciki zai rufe kansu da rawani. Murna da farin ciki zai cika su, baƙin ciki da nishi zai ɓace.
12 « C'est moi, moi aussi, qui vous réconforte. Qui es-tu, pour avoir peur de l'homme qui va mourir, et du fils de l'homme qui sera réduit à l'état d'herbe?
“Ni kaɗai ne na ta’azantar da ku. Wane ne ku da kuke tsoron mutane masu mutuwa,’ya’yan mutane waɗanda suke ciyawa ne kawai,
13 As-tu oublié Yahvé, ton créateur? qui a étendu les cieux, et a posé les fondations de la terre? Vivez-vous dans la peur continuellement toute la journée à cause de la fureur de l'oppresseur, quand il se prépare à détruire? Où est la fureur de l'oppresseur?
har da kuka manta da Ubangiji Mahaliccinku, wanda ya shimfiɗa sammai ya kuma kafa harsashen duniya, har kuna zama da tsoro kowace rana saboda fushin masu zalunci, waɗanda sun ƙudura sai sun hallaka? Gama ina fushin mai zalunci?
14 L'exilé captif sera rapidement libéré. Il ne mourra pas et ne descendra pas dans la fosse. Son pain ne manquera pas.
Ba da daɗewa za a’yantar da’yan kurkuku; ba za su mutu a kurkuku ba, ba kuwa za su rasa abinci ba.
15 Car je suis Yahvé ton Dieu, qui remue la mer. pour que ses vagues rugissent. Yahvé des Armées est son nom.
Gama ni ne Ubangiji Allahnku, wanda ya dama teku domin raƙumansa su yi ruri, Ubangiji Maɗaukaki ne sunansa.
16 J'ai mis mes paroles dans ta bouche et je t'ai couvert de l'ombre de ma main, pour que je puisse planter les cieux, et poser les fondations de la terre, et dis à Sion: « Tu es mon peuple. »
Na sa maganata a bakinka na kuma rufe ka da inuwar hannuna, Na shimfiɗa sammai, na kafa harsashen duniya, na kuma ce wa Sihiyona, ‘Ku mutanena ne.’”
17 Réveillez-vous, réveillez-vous! Debout, Jérusalem, vous qui avez bu de la main de Yahvé la coupe de sa colère. Vous avez bu le bol de la coupe de l'étourdissement, et l'a vidée.
Ki farka, ki farka! Ki tashi, ya Urushalima, ke da kika sha daga hannun Ubangiji kwaf na fushinsa, ke da kika shanye har ƙasar kwaf kwaf da ya sa mutane suna tangaɗi.
18 Il n'y a personne pour la guider parmi tous les fils qu'elle a mis au monde; et il n'y a personne qui la prenne par la main parmi tous les fils qu'elle a élevés.
Cikin dukan’ya’yan da ta haifa; cikin dukan’ya’yan da ta yi reno babu wani da zai kama hannunta.
19 Ces deux choses vous sont arrivées. qui sera en deuil avec vous? la désolation et la destruction, et la famine et l'épée. Comment puis-je te réconforter?
Waɗannan masifu riɓi biyu sun auko miki, wa zai ta’azantar da ke? Lalaci da hallaka, yunwa da takobi, wa zai ƙarfafa ki?
20 Tes fils se sont évanouis. Ils se trouvent à la tête de toutes les rues, comme une antilope dans un filet. Ils sont pleins de la colère de Yahvé, la réprimande de votre Dieu.
’Ya’yanki sun sume; sun kwanta kusurwar kowane titi, kamar barewar da aka kama da tarko. Sun cika da fushin Ubangiji da kuma tsawatawar Allahnki.
21 C'est pourquoi, maintenant, écoutez ceci, vous qui êtes affligés, et ivres, mais pas avec du vin:
Saboda haka ki ji wannan, ke mai wahala, wadda ta bugu, amma ba da ruwan inabi.
22 Ton Seigneur Yahvé, votre Dieu qui plaide la cause de son peuple, dit, « Voici que j'ai retiré de ta main la coupe de l'étourdissement, même le bol de la coupe de ma colère. Vous ne le boirez plus.
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, Allahnki, wanda ya kāre mutanensa, “Duba, na ƙwace daga hannunki kwaf da ya sa ki tangaɗi; daga wannan kwaf, kwaf na fushina, ba za ki ƙara sha ba.
23 Je le mettrai dans la main de ceux qui vous affligent, qui ont dit à ton âme: « Incline-toi, pour que nous puissions marcher sur toi ». et vous avez posé votre dos sur le sol, comme une rue pour ceux qui la traversent. »
Zan sa shi a hannuwan masu gwada miki azaba, waɗanda suke ce miki, ‘Fāɗi rubda ciki don mu iya taka a kanki.’ Kika kuma mai da bayanki kamar ƙasa, kamar titin da ake takawa a kai.”

< Isaïe 51 >