< Isaïe 4 >

1 En ce jour-là, sept femmes saisiront un seul homme, en disant: « Nous mangerons notre propre pain, et nous porterons nos propres vêtements. Laisse-nous seulement être appelées par ton nom. Ôte notre opprobre. »
A wannan rana mata guda bakwai za su cafke namiji guda su ce, “Ma ciyar da kanmu mu kuma yi wa kanmu sutura; ka dai bari mu ce kai ne mijinmu. Ka ɗauke mana kunyar da za mu sha.”
2 En ce jour-là, le rameau de Yahvé sera beau et glorieux, et le fruit du pays sera la beauté et la gloire des survivants d'Israël.
A wannan rana Reshen Ubangiji zai zama kyakkyawa da kuma ɗaukaka, kuma amfanin ƙasar zai zama abin fariya da ɗaukakar waɗanda suka rayu a Isra’ila.
3 Il arrivera que celui qui restera en Sion et celui qui demeurera à Jérusalem seront appelés saints, tous ceux qui seront inscrits parmi les vivants de Jérusalem,
Waɗanda suka rage a Sihiyona, waɗanda suka rage a Urushalima, za a ce da su masu tsarki, wato, dukan waɗanda aka rubuta a cikin masu rai a Urushalima.
4 quand le Seigneur aura lavé les souillures des filles de Sion et purifié le sang de Jérusalem en son sein, par l'esprit de justice et par l'esprit de feu.
Ubangiji zai wanke duk wani ƙazantar matan Sihiyona; ya tsabtacce jinin da aka zubar daga Urushalima ta wurin ruhun hukunci da yake ƙuna kamar wuta.
5 Yahvé créera sur toute la demeure de la montagne de Sion et sur ses assemblées, une nuée et une fumée le jour, et l'éclat d'un feu ardent la nuit, car il y aura un dais sur toute la gloire.
Sa’an nan Ubangiji zai sa girgijen hayaƙi da rana da harshen wuta da dare a bisa dukan Dutsen Sihiyona da kuma bisa waɗanda suka tattaru a can; a bisa duka kuwa ɗaukakar za tă zama rumfa.
6 Il y aura un pavillon pour faire de l'ombre le jour contre la chaleur, et pour servir de refuge et d'abri contre la tempête et la pluie.
Za tă zama rumfa da inuwar da za tă tare zafin rana, da kuma mafaka da wurin ɓuya daga hadari da ruwan sama.

< Isaïe 4 >