< Isaïe 30 >

1 Malheur aux enfants rebelles, dit l'Éternel, qui prennent conseil, mais non de moi, et qui s'allient, mais non avec mon esprit, pour ajouter le péché au péché;
“Kaiton’ya’ya masu tayarwa,” in ji Ubangiji, “ga waɗanda suke ƙulle-ƙullen da ba nawa ba, suna yin yarjejjeniya, amma ba ta Ruhuna ba, suna jibga zunubi a kan zunubi;
2 qui se mettent en route pour descendre en Égypte sans demander mon avis, pour se fortifier dans la force de Pharaon, et pour se réfugier à l'ombre de l'Égypte!
waɗanda suka gangara zuwa Masar ba tare da sun nemi shawarata; waɗanda suke neman taimakon kāriyar Fir’auna, don neman inuwar mafakar Masar.
3 C'est pourquoi la force de Pharaon sera votre honte, et le refuge à l'ombre de l'Égypte votre confusion.
Amma kāriyar Fir’auna za tă zama muku abin kunya, inuwar Masar za tă jawo muku kunya.
4 Car leurs princes sont à Tsoan, et leurs ambassadeurs sont venus à Hanès.
Ko da yake suna da shugabanni a Zowan kuma jakadunsu sun iso Hanes,
5 Ils seront tous honteux à cause d'un peuple qui ne peut leur servir, qui n'est ni un secours ni un avantage, mais une honte, et aussi un opprobre. »
kowa zai sha kunya saboda mutanen da ba su da amfani gare su, waɗanda ba sa taimako ko amfani, sai dai jawo kunya da da-na-sani.”
6 Le fardeau des animaux du Sud. Par le pays de la détresse et de l'angoisse, de la lionne et du lion, de la vipère et du serpent volant ardent, ils portent leurs richesses sur les épaules de jeunes ânes, et leurs trésors sur la bosse des chameaux, vers un peuple infréquentable.
Allah ya faɗa game da dabbobin Negeb cewa, Ta cikin ƙasa mai wahala da mai hatsari inda zakoki da zakanya, inda macizai masu dafi da macizai masu tashi sama suke, jakadu na ɗaukan arzikinsu a kan jakuna, dukiyarsu a kan raƙuma, zuwa ƙasan nan marar riba,
7 Car l'Égypte aide en vain et en pure perte; c'est pourquoi je l'ai appelée Rahab, qui reste assise.
zuwa Masar, wadda taimakonta marar amfani ne. Saboda haka na yi mata laƙabi Rahab Marar Yin Kome.
8 Maintenant, va, écris-le devant eux sur une tablette, et inscris-le dans un livre, afin que ce soit pour les temps à venir, pour toujours et à jamais.
Tafi yanzu, ka rubuta musu a kan allo, ka rubuta shi a kan littafi, cewa kwanaki suna zuwa zai zama madawwamin shaida.
9 Car c'est un peuple rebelle, des enfants menteurs, des enfants qui ne veulent pas écouter la loi de l'Éternel,
Waɗannan mutane masu tawaye,’ya’ya masu ruɗu,’ya’yan da ba sa niyya su saurara ga umarnan Ubangiji.
10 qui disent aux voyants: « Ne voyez pas! » et aux prophètes: « Ne nous prophétisez pas des choses justes. Dites-nous des choses agréables. Prophétisez des tromperies.
Sukan ce wa masu gani, “Kada ku ƙara ganin wahayi!” Ga annabawa kuwa sukan ce, “Kada ku ƙara ba mu wahayin abin da yake daidai! Faɗa mana abubuwan da muke so mu ji ne kawai, ku yi annabcin abin da zai ruɗe mu.
11 Sortez du chemin. Détournez-vous du chemin. Faites que le Saint d'Israël cesse d'être devant nous ».
Ku bar wannan hanya, ku tashi daga wannan hanya, ku kuma daina kalubalantarmu da Mai Tsarkin nan na Isra’ila!”
12 C'est pourquoi le Saint d'Israël dit: « Parce que vous méprisez cette parole, et que vous vous confiez à l'oppression et à la perversité, et que vous vous appuyez sur elle,
Saboda haka, ga abin da Mai Tsarkin nan na Isra’ila yake cewa, “Saboda haka kun ƙi wannan saƙo, kuka dogara ga aikin kama-karya kuka kuma dogara ga yin ruɗu,
13 cette iniquité sera pour vous comme une brèche prête à s'écrouler, gonflée dans une haute muraille, dont la rupture survient soudainement en un instant.
wannan zunubi zai zama muku kamar bango mai tsayi, tsagagge da yake kuma fāɗuwa, da zai rushe nan da nan, ba tsammani.
14 Il la brisera comme on brise le vase d'un potier, il la brisera en morceaux sans ménagement, de sorte qu'il ne se trouvera pas parmi les morceaux brisés un morceau assez bon pour prendre du feu dans le foyer, ou pour puiser de l'eau dans la citerne. »
Zai rushe kucu-kucu kamar tukunyar yumɓu, ya ragargaje ƙaf har cikin gutsattsarinsa ba za a sami ko ɗan katanga don ɗiba garwashin wuta ko a ɗiba ruwa daga tanki ba.”
15 Car ainsi parle le Seigneur Yahvé, le Saint d'Israël: « Vous serez sauvés dans le retour et le repos. Votre force sera dans le calme et dans la confiance. » Vous avez refusé,
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka, Mai Tsarkin nan na Isra’ila ya faɗa, “Cikin tuba da hutu ne kaɗai cetonku yake, cikin shiru da dogara gare ni ne za ku sami ƙarfinku, amma ba za ku sami ko ɗaya a cikinsu ba.
16 mais vous avez dit: « Non, car nous fuirons à cheval »; donc vous fuirez; et « Nous monterons sur le rapide »; donc ceux qui vous poursuivront seront rapides.
Kun ce, ‘A’a, za mu gudu a kan dawakai.’ Saboda haka za ku gudu! Kun ce, ‘Za mu hau dawakai masu sauri mu gudu.’ Saboda haka masu fafararku za su fi ku gudu!
17 Mille fuiront à la menace d'un seul. A la menace de cinq, vous fuirez jusqu'à ce qu'il vous reste comme un phare au sommet d'une montagne, et comme une bannière sur une colline.
Dubu za su gudu don barazanar mutum guda; da jin barazanar mutane biyar dukanku za ku yi ta gudu sai an bar ku kamar sandar tuta a kan dutse, kamar tuta a kan tudu.”
18 C'est pourquoi Yahvé attendra, pour vous faire grâce, et il sera exalté, pour avoir pitié de vous, car Yahvé est un Dieu de justice. Heureux tous ceux qui espèrent en lui.
Duk da haka Ubangiji yana marmari ya yi muku alheri; ya tashi don yă nuna muku jinƙai. Gama Ubangiji Allah ne mai aikata gaskiya. Masu albarka ne dukanku waɗanda suke dogara gare shi!
19 Car le peuple habitera en Sion, à Jérusalem. Vous ne pleurerez plus. A la voix de ton cri, il te fera grâce. Quand il t'entendra, il te répondra.
Ya mutanen Sihiyona, waɗanda suke zama a Urushalima, ba za ku ƙara kuka ba. Zai zama mai alheri sa’ad da kuka yi kukan neman taimako! Da zarar ya ji, zai amsa muku.
20 Même si le Seigneur te donne le pain de l'adversité et l'eau de l'affliction, tes maîtres ne seront plus cachés, mais tes yeux verront tes maîtres;
Ko da yake Ubangiji yakan ba da abincin azaba da ruwan wahala, ba za a ƙara ɓoye malamanku ba; da idanunku za ku gan su.
21 et quand tu te tourneras à droite, et quand tu te tourneras à gauche, tes oreilles entendront une voix derrière toi, disant: « Voici le chemin. Marchez-y. »
Ko kun juye dama ko hagu, kunnuwanku za su ji murya a bayanku tana cewa, “Ga hanya; ku yi tafiya a kai.”
22 Tu souilleras le recouvrement de tes images gravées en argent, et le placage de tes images fondues en or. Tu les jetteras comme une chose impure. Tu lui diras: « Va-t'en! »
Sa’an nan za ku ƙazantar da gumakanku da kuka dalaye da zinariya; za ku zubar da su kamar rigar al’adar mace ku kuma ce musu, “Ku ɓace mana da gani!”
23 Il donnera la pluie pour ta semence, avec laquelle tu ensemenceras le sol; et le pain du produit du sol sera riche et abondant. En ce jour-là, votre bétail paîtra dans de vastes pâturages.
Zai kuma aiko muku da ruwan sama don shuki a ƙasa, kuma abincin da zai fito daga gona zai zama mai albarka da kuma mai yawa. A wannan rana shanu za su yi kiwo a wadatacciyar makiyaya.
24 Les bœufs et les jeunes ânes qui labourent la terre mangeront un fourrage savoureux, qu'on aura vanné avec la pelle et la fourche.
Shanunku da jakunanku da suke huɗar gonakinku za su ci harawa mafi kyau, wanda an sheƙe shi da babban cokali mai yatsu da kuma babban cokali.
25 Il y aura des ruisseaux et des torrents d'eau sur toute haute montagne et sur toute colline élevée, au jour du grand carnage, quand les tours tomberont.
A ranar babban kisa, sa’ad da hasumiyoyi za su fāɗi, rafuffukan ruwa za su malalo a kan kowane dutse da kowane tudu mai tsawo.
26 Et la lumière de la lune sera comme la lumière du soleil, et la lumière du soleil sera sept fois plus brillante, comme la lumière de sept jours, le jour où l'Éternel pansera la fracture de son peuple et guérira la plaie dont il a été frappé.
Wata zai yi haske kamar rana, kuma hasken rana zai ma yi sau bakwai na haskenta, kamar hasken cikakku ranaku bakwai, sa’ad da Ubangiji zai ɗaura raunukan mutanensa ya kuma warkar da raunukan da ya yi musu.
27 Voici que le nom de Yahvé vient de loin, brûlant de sa colère, et dans une épaisse fumée montante. Ses lèvres sont pleines d'indignation. Sa langue est comme un feu dévorant.
Duba, Sunan Ubangiji yana zuwa daga nesa, tare da fushi mai ƙuna da kuma baƙin hayaƙi; leɓunansa sun cika da fushi, harshensa kuma wuta ce mai cinyewa.
28 Son souffle est comme un torrent débordant qui atteint jusqu'au cou, pour passer les nations au crible de la destruction. Une bride qui mène à la ruine sera dans les mâchoires des peuples.
Numfashinsa kamar raƙuman ruwa masu gudu yana tashi har zuwa wuya. Yakan tankaɗe al’ummai cikin lariyar hallaka; yakan sa a muƙamuƙan mutane linzamin da zai jagorance su su kauce.
29 Vous aurez un chant, comme la nuit où l'on célèbre une fête sainte, et une joie du cœur, comme lorsqu'on va avec une flûte pour venir à la montagne de Yahvé, au Rocher d'Israël.
Za ku kuma rera kamar a daren da kuke shagalin biki mai tsarki; zukatanku za su yi farin ciki kamar sa’ad da mutane sukan haura da busa zuwa dutsen Ubangiji, zuwa Dutse na Isra’ila.
30 Yahvé fera entendre sa voix glorieuse, il montrera la descente de son bras, avec l'indignation de sa colère et la flamme d'un feu dévorant, avec le souffle, la tempête et les grêlons.
Ubangiji zai sa mutane su ji muryarsa mai daraja ya kuma sa su ga hannunsa na saukowa tare da fushi mai ƙuna da kuma wuta mai cinyewa, gizagizai za su ɓarke, za a yi hadarin tsawa da ƙanƙara.
31 Car, par la voix de Yahvé, l'Assyrien sera consterné. Il le frappera de sa verge.
Muryar Ubangiji za tă firgita Assuriya da sandar mulkinsa zai kashe su.
32 Chaque coup de la verge du châtiment que Yahvé lui infligera sera accompagné du son des tambourins et des harpes. Il combattra avec eux dans les batailles, en brandissant des armes.
Kowane bugun da Ubangiji zai yi musu da bulalarsa na hukunci zai zama kiɗi ga ganguna da garaya, yayinda yake yaƙi da su da naushin hannunsa.
33 Car il y a longtemps que sa fournaise est prête. Oui, elle est préparée pour le roi. Il a fait son bûcher profond et large avec du feu et beaucoup de bois. Le souffle de Yahvé, comme un torrent de soufre, l'allume.
An riga an shirya wurin ƙonawa; an shirya shi saboda sarki. An haƙa ramin wutarsa da zurfi da kuma fāɗi, da isashen wuta da itacen wuta; numfashin Ubangiji, yana kamar kibiritu mai ƙuna, da aka sa masa wuta.

< Isaïe 30 >