< Isaïe 3 >

1 Car voici, le Seigneur, Yahvé des armées, enlève à Jérusalem et à Juda le ravitaillement et le soutien, tout le stock de pain, et toute la réserve d'eau;
Yanzu ka duba fa, Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana shirin yă ɗauke kowane tanadi da taimako daga Urushalima da Yahuda dukan tanade-tanaden abinci da kuma dukan tanade-tanaden ruwa,
2 l'homme puissant, l'homme de guerre, le juge, le prophète, le devin, l'aîné,
jarumi, da soja, alƙali da annabi masu duba da dattijo,
3 le capitaine de cinquante, l'homme honorable, le conseiller, l'artisan qualifié, et l'astucieux enchanteur.
shugaban sojojin hamsin da mutum mai makami, mai ba da shawara, gwanin sarrafa abubuwa da mai gwanintan dabo.
4 Je donnerai des garçons pour être leurs princes, et les enfants domineront sur eux.
“Zan sa’yan yara su zama shugabanninsu;’yan yara kurum za su yi mulkinsu.”
5 Le peuple sera opprimé, chacun par un autre, et chacun par son voisin. L'enfant se comportera fièrement face au vieil homme, et les méchants contre les honorables.
Mutane za su zalunci juna mutum da mutum, maƙwabci da maƙwabci. Yara za su rena tsofaffi, ƙasƙantacce zai rena mai daraja.
6 En effet, un homme saisira son frère dans la maison de son père, en disant, « Tu as des vêtements, tu seras notre chef. et que cette ruine soit sous ta main. »
Mutum zai kama ɗaya daga cikin’yan’uwansa a gidan mahaifinsa ya ce, “Kana da abin sawa, ka zama shugabanmu; wannan kango kuma yă zama a ƙarƙashinka!”
7 En ce jour-là, il s'écriera: « Je ne veux pas être un guérisseur; car dans ma maison, il n'y a ni pain ni vêtement. Tu ne feras pas de moi le chef du peuple. »
Amma a ranan nan zai tā da murya ya ce, “Ba ni ba dai. Ba ni da abinci ko abin sawa a gidana; kada ka mai da ni shugaban mutane.”
8 Car Jérusalem est ruinée, et Juda est tombé; car leur langue et leurs actes sont contraires à Yahvé, pour provoquer les yeux de sa gloire.
Urushalima tana tangaɗi, Yahuda yana fāɗuwa; maganganunsu da ayyukansu suna gāba da Ubangiji, suna rena ɗaukakar kasancewarsa.
9 L'aspect de leur visage témoigne contre eux. Ils exhibent leur péché comme Sodome. Ils ne le cachent pas. Malheur à leur âme! Car ils ont attiré le désastre sur eux.
Fuskokinsu shaidu ne a kansu; suna nuna zunubinsu a fili kamar yadda Sodom ya yi; ba sa ma ɓoye shi. Kaitonsu! Sun jawo wa kansu masifa.
10 Dis aux justes que tout ira bien pour eux, car ils mangeront le fruit de leurs actes.
Ku faɗa wa masu adalci cewa kome zai zama musu da kyau, gama za su ji daɗin aikin da hannuwansu suka yi.
11 Malheur aux méchants! Le désastre est sur eux, car les actes de leurs mains leur seront rendus.
Kaiton masu mugunta! Masifa tana a kansu! Za a rama abin da hannuwansu suka yi.
12 Quant à mon peuple, les enfants sont ses oppresseurs, et les femmes les gouvernent. Mon peuple, ceux qui te dirigent te font errer, et détruire le chemin de vos sentiers.
Matasa suna zalunta mutanena, mata suna mulki a bisansu. Ya mutanena, jagorarinku suna ɓad da ku; suna karkatar da ku daga hanya.
13 Yahvé se lève pour contester, et se tient debout pour juger les peuples.
Ubangiji ya ɗauki mazauninsa a cikin ɗakin shari’a; ya tashi don yă shari’anta mutane.
14 L'Éternel entrera en jugement avec les anciens de son peuple. et leurs dirigeants: « C'est vous qui avez dévoré la vigne. Le butin des pauvres est dans vos maisons.
Ubangiji yana shari’a da dattawa da kuma shugabannin mutanensa, “Ku ne kuka lalace gonar inabina; ganimar talakawa suna a gidajenku.
15 Qu'est-ce que cela signifie que vous écrasez mon peuple, et broyer le visage du pauvre? » dit le Seigneur, Yahvé des Armées.
Ina dalilin da kuke marmatsa mutanena kuna gurgurje fuskokin talakawa?” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
16 Et Yahvé dit: « Parce que les filles de Sion sont arrogantes, et marchent avec le cou tendu et les yeux qui flirtent, en marchant dignement, des ornements qui tintent sur leurs pieds;
Ubangiji ya ce, “Matan Sihiyona suna da girman kai, suna tafiya da wuya a miƙe, da idanu masu yaudara, suna takawa ɗaya-ɗaya a hankali, da mundaye a ƙafafunsu, suna cas-cas.
17 C'est pourquoi l'Éternel fait venir des ulcères sur le sommet de la tête des femmes de Sion, et Yahvé rendra leur crâne chauve. »
Saboda haka Ubangiji zai kawo gyambuna a kawunan matan Sihiyona; Ubangiji zai sa a aske kawunansu, a bar su ƙwal.”
18 En ce jour-là, l'Éternel enlèvera la beauté de leurs bracelets de cheville, de leurs bandeaux, de leurs colliers en forme de croissant,
A wannan rana Ubangiji zai ƙwace abin da suke taƙama da shi, mundayensu, ɗankwalin kansu da abin wuyansu,
19 de leurs boucles d'oreilles, de leurs bracelets, de leurs voiles,
’yan kunnensu, kwandagansu da lulluɓinsu,
20 de leurs coiffures, de leurs chaînes de cheville, de leurs ceintures, de leurs flacons de parfum, de leurs breloques,
kitsonsu, sarƙar da suke sa wa damatsansu da ɗamararsu, kwalabai turare da layu,
21 de leurs chevalières, de leurs anneaux de nez,
da ƙawanen da suka sa a yatsotsinsu da hancinsu,
22 de leurs robes fines, de leurs capes, de leurs manteaux, de leurs bourses,
tufafi masu kyau, da manyan rigunansu, da mayafansu, da jakar kuɗinsu
23 de leurs miroirs à main, de leurs vêtements de lin fin, de leurs diadèmes et de leurs châles.
da madubi, da kuma tufafin lilin da adikai, da gyale.
24 Il arrivera qu'au lieu d'épices douces, il y aura de la pourriture; au lieu d'une ceinture, une corde; au lieu de cheveux bien attachés, la calvitie; au lieu d'une robe, un port de sac; et l'image de marque au lieu de la beauté.
A maimakon ƙanshi, wari ne za a ji; a maimakon abin ɗamara, igiya ce za a samu; a maimakon kyakkyawan gashi, sanƙo za su kasance da shi a kai; a maimakon tufafi masu kyau, za su sa tsummoki; a maimakon kyau, za su zama munana.
25 Tes hommes tomberont par l'épée, et votre puissance dans la guerre.
Mazanku za su mutu ta wurin takobi, jarumawanku za su mutu a yaƙi.
26 Ses portes se plaignent et se lamentent. Elle sera désolée et s'assiéra sur le sol.
Ƙofofin Sihiyona za su yi makoki su kuma yi kuka; za tă zama wofi, za tă zauna a ƙasa.

< Isaïe 3 >