< Isaïe 26 >

1 En ce jour-là, on chantera ce cantique dans le pays de Juda: « Nous avons une ville forte. Dieu destine le salut aux murs et aux remparts.
A wannan rana za a rera wannan waƙa a ƙasar Yahuda. Muna da birni mai ƙarfi; Allah yake ceton katanga da kuma kagarunta.
2 Ouvrez les portes, pour que la nation juste puisse entrer: celui qui garde la foi.
A buɗe ƙofofi saboda al’umma mai adalci ta shiga, al’ummar da mai aminci.
3 Tu gardes dans une paix parfaite l'esprit de celui qui est ferme, parce qu'il a confiance en vous.
Za ka kiyaye shi da cikakken salama shi wanda ya kafa zuciyarsa gare ka, domin ya dogara a gare ka.
4 Faites confiance à Yahvé pour toujours; car en Yah, Yahvé, est un rocher éternel.
Ku dogara ga Ubangiji, gama shi Ubangiji, ne madawwamin Dutse.
5 Car il a fait tomber les habitants des hauteurs, de la ville haute. Il fait profil bas. Il la pose à ras du sol. Il l'apporte même à la poussière.
Yakan ƙasƙantar da waɗanda suke zama a bisa ya kawar da birni mai alfarma ƙasa; ya rusa ta har ƙasa ya jefar da ita cikin ƙura.
6 Le pied la foulera, même les pieds des pauvres et les pas des nécessiteux ».
Ƙafafu sukan tattake ta, ƙafafu waɗanda aka zalunta, wato, sawun matalauta.
7 La voie du juste est la droiture. Toi qui es droit, tu nivelles le chemin des justes.
Hanyar masu adalci sumul take; Ya Mai Aikata Gaskiya, ka sa hanyar masu adalci ta yi sumul.
8 Oui, dans la voie de tes jugements, Yahvé, nous t'avons attendu. Ton nom et ta renommée sont le désir de notre âme.
I, Ubangiji, cikin tafiya a hanyar dokokinka, muna sa zuciya gare ka; sunanka da tunani a kanka su ne marmarin zukatanmu.
9 De mon âme, je t'ai désiré pendant la nuit. Oui, avec mon esprit en moi, je vous chercherai sincèrement; car quand tes jugements sont sur la terre, les habitants du monde apprennent la justice.
Raina yana marmarinka da dare; da safe kuma raina yana son ganinka. Sa’ad da hukunce-hukuncenka suka sauko duniya, mutanen duniya kan koyi adalci.
10 Que l'on fasse grâce aux méchants, mais il n'apprendra pas la droiture. Dans le pays de la droiture, il agira mal, et ne verront pas la majesté de Yahvé.
Ko da yake akan nuna wa mugaye alheri, ba sa koyi adalci; har ma a ƙasar masu aikata gaskiya sukan ci gaba da aikata mugunta ba sa ganin girmar darajar Ubangiji.
11 Yahvé, ta main est levée, et ils ne voient pas; mais ils verront votre zèle pour le peuple et seront déçus. Oui, le feu consumera vos adversaires.
Ya Ubangiji an ɗaga hannunka sama, amma ba sa ganinsa. Bari su ga himmarka don mutanenka su kuma sha kunya; bari wutar da aka ajiye don abokan gābanka ta cinye su.
12 Yahvé, tu ordonneras la paix pour nous, car tu as aussi fait tout notre travail pour nous.
Ubangiji ka kafa salama dominmu; duk abin da muka iya yi kai ne ka yi mana.
13 Yahvé notre Dieu, d'autres seigneurs que toi ont dominé sur nous, mais nous ne reconnaîtrons que votre nom.
Ya Ubangiji, Allahnmu, waɗansu iyayengiji ban da kai sun yi mulki a kanmu, amma sunanka kaɗai muka girmama.
14 Les morts ne vivront pas. Les esprits défunts ne s'élèveront pas. C'est pourquoi vous les avez visités et détruits, et a fait périr toute mémoire d'eux.
Yanzu duk sun mutu, ba za su ƙara rayuwa ba; waɗannan ruhohin da suka rasu ba za su tashi ba. Ka hukunta su ka kuma kawo su ga hallaka; ka sa ba za a ƙara tunawa da su ba.
15 Tu as multiplié la nation, ô Yahvé. Vous avez augmenté la nation! Vous êtes glorifié! Tu as élargi toutes les frontières du pays.
Ka fadada al’umma, ya Ubangiji; ka fadada al’umma. Ka samo wa kanka ɗaukaka; ka fadada dukan iyakokin ƙasar.
16 Yahvé, c'est dans la détresse qu'ils t'ont visité. Ils ont versé une prière lorsque ton châtiment s'est abattu sur eux.
Ubangiji, sun zo gare ka a cikin damuwarsu; sa’ad da ka hore su, da ƙyar suna iya yin addu’a.
17 Comme une femme enceinte, qui approche du moment de l'accouchement, est en souffrance et crie dans ses douleurs, ainsi nous avons été devant toi, Yahvé.
Kamar mace mai ciki da take gab da haihuwa takan yi ta murɗawa tana kuka saboda zafi, haka muka kasance a gabanka, ya Ubangiji.
18 Nous avons été avec l'enfant. Nous avons souffert. Nous n'avons donné naissance, semble-t-il, qu'à du vent. Nous n'avons opéré aucune délivrance sur la terre; les habitants du monde ne sont pas non plus tombés.
Muna da ciki, mun yi ta murɗewa saboda zafi, amma mun haifi iska. Ba mu kawo ceto ga duniya ba; ba mu haifi mutanen duniya ba.
19 Vos morts vivront. Leurs corps morts se lèveront. Réveillez-vous et chantez, vous qui habitez dans la poussière; car ta rosée est comme la rosée des herbes, et la terre chassera les esprits des défunts.
Amma matattunka za su rayu; jikunansu za su tashi. Ku da kuke zama a ƙura, ku farka ku kuma yi sowa don farin ciki. Raɓarka kamar raɓar safiya ce; duniya za tă haifi matattunta.
20 Venez, mon peuple, entrez dans vos chambres, et fermez vos portes derrière vous. Cachez-vous pendant un petit moment, jusqu'à ce que l'indignation soit passée.
Ku tafi, mutanena, ku shiga ɗakunanku ku kuma kulle ƙofofi; ku ɓoye kanku na ɗan lokaci sai ya huce fushinsa.
21 Car voici que Yahvé sort de son lieu pour punir les habitants de la terre à cause de leur iniquité. La terre aussi dévoilera son sang, et ne couvrira plus ses morts.
Duba, Ubangiji yana fitowa daga mazauninsa don yă hukunta mutanen duniya saboda zunubansu. Duniya za tă bayyana zub da jinin da aka yi a kanta; ba za tă ƙara ɓoye waɗanda aka kashe a cikinta ba.

< Isaïe 26 >