< Isaïe 25 >
1 Yahvé, tu es mon Dieu. Je t'exalte! Je louerai ton nom, car tu as fait des choses merveilleuses, des choses prévues depuis longtemps, en toute fidélité et vérité.
Ya Ubangiji, kai ne Allahna; zan ɗaukaka ka in kuma yabi sunanka, gama cikin cikakken aminci ka yi abubuwa masu banmamaki, abubuwan da aka shirya tun da.
2 Car tu as fait d'une ville un monceau, d'une ville fortifiée une ruine, d'un palais d'étrangers une ville qui n'existe plus. Elle ne sera jamais bâtie.
Ka mai da birnin tsibin tarkace, ka lalatar da gari mai katanga, birnin baƙi mai ƙarfi, ta ɓace; ba za a ƙara gina ta ba.
3 C'est pourquoi un peuple fort te glorifiera. Une ville de nations puissantes te craindra.
Saboda haka mutane masu ƙarfi za su girmama ka; biranen mugayen al’ummai za su ji tsoronka.
4 Car tu as été un refuge pour le pauvre, une forteresse pour l'indigent dans sa détresse, un abri contre la tempête, une ombre contre la chaleur, quand le souffle des redoutables est comme une tempête contre la muraille.
Kai ka zama mafakar matalauta, mafaka don mabukata cikin damuwa, wurin ɓuya daga hadari, inuwa kuma daga zafin rana. Gama numfashin mugaye yana kamar da hadari mai bugun bango
5 Comme la chaleur d'un lieu sec, tu feras tomber le bruit des étrangers; comme la chaleur à l'ombre d'un nuage, tu feras tomber le chant des redoutables.
kuma kamar zafin hamada. Ka kwantar da hayaniyar baƙi; kamar yadda inuwar girgije kan rage zafin rana, haka ake kwantar da waƙar mugaye.
6 Dans cette montagne, l'Éternel des armées fera à tous les peuples un festin de viandes de choix, un festin de vins de choix, de viandes de choix pleines de mœlle, de vins de choix bien raffinés.
A kan wannan dutse Ubangiji Maɗaukaki zai shirya bikin abinci mai kyau don dukan mutane, liyafar ajiyayyen ruwan inabi da nama mafi kyau da ruwan inabi mafi kyau.
7 Il détruira dans cette montagne la surface de la couverture qui recouvre tous les peuples, et le voile qui s'étend sur toutes les nations.
A wannan dutse zai kawar da baƙin cikin da ya lulluɓe dukan mutane, ƙyallen da ya rufe dukan al’ummai;
8 Il a englouti la mort pour toujours! Le Seigneur Yahvé essuiera les larmes de tous les visages. Il enlèvera l'opprobre de son peuple de toute la terre, car Yahvé l'a dit.
zai haɗiye mutuwa har abada. Ubangiji Mai Iko Duka zai share hawaye daga dukan fuskoki; zai kawar da kunyar mutanensa daga dukan duniya. Ubangiji ne ya faɗa.
9 En ce jour-là, on dira: « Voici notre Dieu! Nous l'avons attendu, et il nous a sauvés! C'est Yahvé! Nous l'avons attendu. Nous nous réjouirons et nous nous réjouirons de son salut! »
A wannan rana za su ce, “Tabbatacce wannan shi ne Allah; mun dogara a gare shi, ya kuma cece mu. Wannan shi ne Ubangiji, mun dogara a gare shi; bari mu yi murna mu kuma yi farin ciki a cikin cetonsa.”
10 Car la main de Yahvé s'arrêtera sur cette montagne. Moab sera foulé à sa place, comme on foule la paille dans l'eau du fumier.
Hannun Ubangiji zai zauna a kan wannan dutse; amma za a tattake Mowab a ƙarƙashinsa kamar yadda ake tattaka kara a cikin taki.
11 Il étendra ses mains au milieu d'elle, comme celui qui nage étend ses mains pour nager, mais son orgueil sera humilié avec l'art de ses mains.
Za su buɗe hannuwansa a cikinsa, yadda mai iyo kan buɗe hannuwansa don yă yi iyo. Allah ya ƙasƙantar da girmankansu duk da wayon hannuwansu.
12 Il a abattu la haute forteresse de tes murs, il l'a abaissée, il l'a ramenée à terre, jusqu'à la poussière.
Zai rurrushe manyan katangar kagaru ya kuma ƙasƙantar da su; zai rushe su har ƙasa, su zama ƙura.