< Isaïe 23 >

1 Le fardeau de Tyr. Hurlez, navires de Tarsis! Car elle est dévastée, il n'y a plus de maison, plus d'entrée. C'est du pays de Kittim qu'il leur est révélé.
Abin da Allah ya faɗa game da Taya. Ku yi kuka mai zafi, ya jiragen ruwan Tarshish! Gama an hallaka Taya aka kuma bar su babu gida ko tasha. Daga ƙasar Saifurus magana ta zo musu.
2 Soyez tranquilles, habitants de la côte, vous que les marchands de Sidon, qui passent par la mer, ont rassasiés.
Ku yi shiru, ku mutanen tsibiri da ku’yan kasuwan Sidon waɗanda masu ciniki a teku suka azurta.
3 Sur les grandes eaux, la semence du Shihor, la récolte du Nil, était son revenu. Elle était le marché des nations.
A manyan ruwaye hatsin Shihor suka iso; girbin Nilu ne kuɗin shiga na Taya ta kuma zama kasuwar al’ummai.
4 Honte à toi, Sidon! Car la mer a parlé, la forteresse de la mer, en disant: « Je n'ai pas enfanté, je n'ai pas accouché, je n'ai pas nourri de jeunes gens, je n'ai pas élevé de vierges. »
Ki ji kunya, ya ke Sidon, da ke kuma, kagarar teku, gama teku ya yi magana ya ce, “Ban taɓa naƙuda ba balle in haifi’ya’ya; ban taɓa goyon’ya’ya maza ba balle in reno’ya’ya mata.”
5 Quand la nouvelle arrivera en Égypte, elle sera dans l'angoisse à la nouvelle de Tyr.
Sa’ad da magana ta kai Masar, za su razana da jin labari daga Taya.
6 Passez à Tarsis! Gémissez, habitants de la côte!
Ku haye zuwa Tarshish; ku yi kuka mai zafi, ku mutanen tsibiri.
7 Est-ce là votre ville joyeuse, Dont l'antiquité est ancienne, Et dont les pieds l'ont portée au loin pour voyager?
Wannan ce birnin murnanku, birnin nan na tun dā wadda ƙafafunta suka kai ta zama a ƙasashe masu nesa?
8 Qui a projeté cela contre Tyr, la dispensatrice de couronnes, dont les marchands sont des princes, dont les négociants sont les hommes d'honneur de la terre?
Wane ne ya ƙulla wannan a kan Taya ita da take ba da rawanin sarauta, wadda’yan kasuwanta sarakuna ne, wadda masu cinikinta sanannu ne a duniya?
9 L'Éternel des armées l'a projeté, pour souiller l'orgueil de toute gloire, pour mépriser tous les hommes d'honneur de la terre.
Ubangiji Maɗaukaki ya ƙulla shi, don yă kawo ƙarshen girman kan dukan darajarta ya kuma ƙasƙantar da dukan waɗanda suke sanannu a duniya.
10 Passe par ton pays comme le Nil, fille de Tarsis. Il n'y a plus de frein.
Ki nome ƙasarki har zuwa wajen Nilu, Ya Diyar Tarshish, gama ba ki da tashan jirgin ruwa kuma.
11 Il a étendu sa main sur la mer. Il a fait trembler les royaumes. Yahvé a ordonné la destruction des forteresses de Canaan.
Ubangiji ya miƙa hannunsa a bisa teku ya kuma sa mulkokinsa suka yi rawar jiki. Ya ba da umarni game da Funisiya cewa a hallaka kagararta.
12 Il a dit: « Tu ne te réjouiras plus, vierge opprimée, fille de Sidon. Lève-toi, passe à Kittim. Là aussi tu n'auras pas de repos. »
Ya ce, “Ba za ki ƙara yin murna ba, Ya ke Budurwa Diyar Sidon, yanzu da kike ragargajiya! “Tashi, ki ƙetare zuwa Saifurus; a can ɗin ma ba za ki huta ba.”
13 Voici le pays des Chaldéens. Ce peuple n'existait pas. Les Assyriens l'ont fondé pour ceux qui habitent dans le désert. Ils ont érigé leurs tours. Ils ont renversé ses palais. Ils en ont fait une ruine.
Dubi ƙasar Babiloniyawa, wannan mutanen da yanzu ba su da wani amfani! Assuriyawa sun mai da ita wurin zaman halittun hamada; sun gina hasumiyoyin kwanto, suka ragargaza kagararta ƙaf suka mai da ita kango.
14 Hurlez, navires de Tarsis, car votre forteresse est détruite!
Ku yi kuka mai zafi, ku jiragen ruwan Tarshish; an rurrushe kagararku!
15 En ce jour-là, Tyr sera oubliée pendant soixante-dix ans, selon les jours d'un seul roi. Au bout de soixante-dix ans, il en sera pour Tyr comme dans le chant de la prostituée.
A wannan lokaci za a manta da Taya har shekaru saba’in, tsawon rayuwar sarki. Amma a ƙarshen waɗannan shekaru saba’in, zai zama wa Taya kamar yadda yake a waƙar karuwa cewa,
16 Prends une harpe, parcours la ville, prostituée oubliée. Fais des mélodies douces. Chantez beaucoup de chansons, afin qu'on se souvienne de vous.
“Ɗauki garaya, ki ratsa birni, Ya ke karuwar da aka manta da ita; kaɗa garaya da kyau, ki rera waƙoƙi masu yawa, saboda a tuna da ke.”
17 Au bout de soixante-dix ans, l'Éternel visitera Tyr. Elle retournera à son salaire et se prostituera avec tous les royaumes du monde sur la surface de la terre.
A ƙarshen shekaru saba’in, Ubangiji zai magance Taya. Za tă koma ga aikinta na karuwanci za tă kuma yi kasuwancinta da dukan mulkokin duniya.
18 Sa marchandise et son salaire seront saints pour Yahvé. On n'en fera ni des trésors ni des réserves, car sa marchandise sera pour ceux qui habitent devant Yahvé, pour manger à leur faim et pour se vêtir durablement.
Duk da haka za a keɓe ribarta da kuɗin shigarta wa Ubangiji; ba za a yi ajiyarsu ko a ɓoye su. Ribarta za tă tafi ga waɗanda suke yi wa Ubangiji sujada, don su sami yalwataccen abinci da tufafi masu kyau.

< Isaïe 23 >