< Isaïe 22 >
1 Le fardeau de la vallée de la vision. Qu'est-ce qui vous afflige maintenant, pour que vous soyez tous montés sur les toits?
Abin da Allah ya faɗa game da Kwarin Wahayi. Mene ne ya dame ku a yanzu, da dukanku kuka hau kan rufin gidaje.
2 Toi qui es pleine de cris, ville tumultueuse, ville joyeuse, tes morts ne sont pas tués par l'épée, ils ne sont pas morts dans la bataille.
Ya kai gari cike da hayaniya, Ya ke birnin tashin hankali da alkarya mai murna? Mutanenki ba su mutu ta wurin takobi ba, ba kuwa za su mutu a yaƙi ba.
3 Tous tes chefs se sont enfuis ensemble, Ils ont été liés par les archers. Ils ont été liés par les archers. Tous ceux que tu as trouvés ont été liés ensemble. Ils se sont enfuis au loin.
Dukan shugabanninki sun gudu gaba ɗaya; an kama su ba tare da an yi amfani da baka ba. Dukanku da aka kama an kwashe ku ɗaurarru gaba ɗaya, kun gudu tun abokin gāba yana da nisa.
4 C`est pourquoi j`ai dit: Détournez de moi les regards. Je vais pleurer amèrement. Ne cherche pas à me consoler de la destruction de la fille de mon peuple.
Saboda haka na ce, “Ƙyale ni kurum; bari in yi kuka mai zafi. Kada ka yi ƙoƙarin ta’azantar da ni a kan hallakar mutanena.”
5 Car c'est un jour de confusion, de piétinement et de trouble de la part de l'Éternel, le Yahvé des armées, dans la vallée de la vision, un effondrement des murs et un cri vers les montagnes. »
Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, yana da ranar giggicewa da tattakewa da banrazana a cikin Kwarin Wahayi, ranar ragargazawar katanga da ta yin kuka ga duwatsu.
6 Elam portait son carquois, avec des chars d'hommes et des cavaliers; et Kir découvrait le bouclier.
Elam ya ɗauki kwari da baka, tare da mahayan kekunan yaƙinta da dawakai; Kir ta buɗe garkuwoyi.
7 Tes plus belles vallées étaient pleines de chars, Et les cavaliers se rangeaient en bataille à la porte.
Kwarurukanku mafi kyau sun cika da kekunan yaƙi, an kuma tsai da mahayan dawakai a ƙofofin birni.
8 Il enleva la couverture de Juda, et tu regardas en ce jour-là les armures dans la maison de la forêt.
An rurrushe kāriyar Yahuda, a ranan nan kuwa kun yi la’akari da makamai a cikin Fadan Kurmi;
9 Tu as vu les brèches de la ville de David, elles étaient nombreuses, et tu as recueilli les eaux de l'étang inférieur.
kuka ga cewa Birnin Dawuda tana da wuraren kāriya masu yawa da suka tsattsage; kuka tattara ruwa a Tafkin Ƙasa.
10 Tu as compté les maisons de Jérusalem, et tu as abattu les maisons pour fortifier la muraille.
Kuka ƙirga gine-gine a Urushalima kuka kuma rurrushe gidaje don ku ƙarfafa katanga.
11 Tu as aussi fait un réservoir entre les deux murs pour l'eau de l'ancienne piscine. Mais tu n'as pas regardé celui qui avait fait cela, et tu n'as pas eu de respect pour celui qui l'avait prévu depuis longtemps.
Kuka gina matarar ruwa tsakanin katanga biyu saboda ruwan Tsohon Tafki, amma ba ku yi la’akari da Wannan da ya yi su ba, ko ku kula da Wannan da ya shirya shi tuntuni.
12 En ce jour-là, l'Éternel, le Yahvé des armées, a appelé aux pleurs, au deuil, à la calvitie et à l'habillement de sacs;
Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki ya kira ku a wannan rana don ku yi kuka ku yi ihu, don ku aske gashinku ku kuma sa tsummoki.
13 et voici, c'est la joie et l'allégresse, on tue du bétail et on tue des moutons, on mange de la viande et on boit du vin: « Mangeons et buvons, car demain nous mourrons. »
Amma duba, sai ga shi kuna farin ciki kuna kuma murna, kuna yankan shanu kuna kashe tumaki, kuna cin nama kuna kuma shan ruwan inabi! Kuna cewa, “Bari mu ci mu kuma sha, gama gobe za mu mutu!”
14 L'Éternel des armées se révéla à mes oreilles: « Cette iniquité ne te sera pas pardonnée avant ta mort, dit le Seigneur, l'Éternel des armées.
Ubangiji Maɗaukaki ya bayyana wannan a kunnena cewa, “Har ranar mutuwarka ba za a yi kafarar wannan zunubi ba,” in ji mai girma Ubangiji Maɗaukaki.
15 Le Seigneur, l'Éternel des armées, dit: « Va, va trouver ce trésorier, jusqu'à Shebna, qui est à la tête de la maison, et dis:
Ga abin da Ubangiji, Ubangiji Maɗaukaki, ya faɗa, “Je, ka faɗa wa wannan mai hidima, Shebna, sarkin fada.
16 'Que fais-tu ici? Qui t'a fait venir ici, pour que tu te creuses un tombeau ici?'. Il s'est creusé un tombeau en haut, il s'est taillé une habitation dans le roc! »
Mene ne kake yi a nan kuma wa ya ba ka izini ka haƙa kabari wa kanka a nan, kana fafe kabarinka a bisa kana sassaƙa wurin hutunka a dutse?
17 Voici que Yahvé vous vaincra et vous précipitera violemment. Oui, il te saisira fermement.
“Ka yi hankali, Ubangiji yana shirin ya kama ka da ƙarfi ya kuma ɗauke ka, ya kai mai ƙarfi.
18 Il te fera tourner en rond et te jettera comme une balle dans un grand pays. C'est là que tu mourras, c'est là que seront les chars de ta gloire, toi qui es la honte de la maison de ton seigneur.
Zai dunƙule ka kamar ƙwallo ya jefa ka a cikin ƙasa mai girma. A can za ka mutu a can kuma kekunan yaƙinka masu daraja za su kasance, abin kunya kake ga gidan maigidanka!
19 Je te chasserai de ta charge. Tu seras abattu de ton poste.
Zan tumɓuke ka daga makaminka, za a kuma kore ka daga matsayinka.
20 En ce jour-là, j'appellerai mon serviteur Éliakim, fils de Hilkija,
“A wannan rana zan kira bawana, Eliyakim ɗan Hilkiya.
21 je le revêtirai de ta robe, et je le fortifierai avec ta ceinture. Je remettrai entre ses mains ton gouvernement, et il sera un père pour les habitants de Jérusalem et pour la maison de Juda.
Zan rufe shi da rigarka in kuma yi masa ɗamara in miƙa masa ikonka. Zai zama mahaifi ga waɗanda suke zama a Urushalima da kuma gidan Yahuda.
22 Je poserai sur son épaule la clé de la maison de David. Il ouvrira, et personne ne fermera. Il fermera, et personne n'ouvrira.
Zan sa mabuɗin gidan Dawuda a kafaɗarsa; abin da ya buɗe ba mai rufewa, kuma abin da ya rufe ba mai buɗewa.
23 Je le fixerai comme un clou dans un lieu sûr. Il sera un trône de gloire pour la maison de son père.
Zan kafa shi kamar turke a tsayayyen wuri; zai zama mazaunin daraja domin gidan mahaifinsa.
24 On accrochera sur lui toute la gloire de la maison de son père, la descendance et la postérité, tous les petits objets, depuis les tasses jusqu'à toutes les cruches.
Dukan ɗaukakar iyalinsa za tă rataya a kansa daga’ya’yansa da zuriyarsa har zuwa dukan ƙananan kayan aikinsa, wato, daga kwanoni har zuwa tuluna.
25 « En ce jour-là, dit Yahvé des armées, le clou qui était fixé dans un lieu sûr cédera. Il sera abattu et tombera. Le fardeau qu'il portait sera coupé, car Yahvé l'a dit. »
“A ranan nan, in ji Ubangiji Maɗaukaki, turken da aka kafa a tsayayyen wuri zai sumɓule; za a sare shi ya fāɗi, za a kuma datse nauyin da yake rataya a kansa.” Ni Ubangiji na faɗa.