< Isaïe 19 >
1 Le fardeau de l'Égypte. « Voici que Yahvé monte sur une nuée rapide, et il vient en Égypte. Les idoles de l'Égypte trembleront en sa présence, et le cœur de l'Égypte se fondra en lui.
Abin da Allah ya faɗa game da Masar, Duba, Ubangiji yana a kan girgije a sukwane yana kuwa zuwa Masar. Gumakan Masar sun firgita a gabansa, zukatan Masarawa sun karai.
2 J'exciterai les Égyptiens contre les Égyptiens, et ils se battront chacun contre son frère, chacun contre son voisin, ville contre ville, et royaume contre royaume.
“Zan tā da hargitsi tsakanin mutumin Masar da mutumin Masar, ɗan’uwa zai yi gāba da ɗan’uwa maƙwabci ya yi gāba da maƙwabci, birni ya yi gāba da birni, mulki ya yi gāba da mulki.
3 L'esprit des Égyptiens s'affaiblira au dedans d'eux. Je détruirai leur conseil. Ils chercheront les idoles, les enchanteurs, ceux qui ont des esprits familiers, et les magiciens.
Masarawa za su karai, zan kuma sa shirye-shiryensu su zama banza; za su nemi shawarar gumaka da kuma ruhohin matattu, za su nemi shawarar mabiya da na masu duba.
4 Je livrerai les Égyptiens entre les mains d'un seigneur cruel. Un roi féroce dominera sur eux, dit le Seigneur, Yahvé des Armées.
Zan ba da Masarawa ga ikon azzalumi shugaba, mugun sarki kuma zai yi mulki a kansu,” in ji mai girma, Ubangiji Maɗaukaki.
5 Les eaux de la mer disparaîtront, et le fleuve sera épuisé et desséché.
Ruwayen kogi za su ƙafe, bakin kogi zai shanye yă kuma bushe.
6 Les fleuves deviendront infects. Les ruisseaux d'Égypte diminueront et se dessécheront. Les roseaux et les drapeaux se dessécheront.
Wuriyoyi za su yi wari; rafuffukan Masar za su yi ta raguwa har su ƙafe. Iwa da jema za su bushe,
7 Les prairies sur le Nil, sur le bord du Nil, et tous les champs ensemencés sur le Nil, se dessèchent, sont chassés, et ne sont plus.
haka ma tsire-tsire kusa da Nilu, a bakin kogi. Kowane abin da aka shuka a gefen Nilu zai bushe, iska ta kwashe su ƙaf.
8 Les pêcheurs se lamenteront, et tous ceux qui pêchent dans le Nil se lamenteront, et ceux qui étendent les filets sur les eaux se languiront.
Masu kamun kifi za su yi nishi su kuma yi makoki, dukan waɗanda suke jefan ƙugiyoyi a Nilu; waɗanda suke jefan abin kamun kifi a ruwa abin kamun kifin za su zama marasa amfani.
9 Et ceux qui travaillent le lin peigné, et ceux qui tissent des étoffes blanches, seront confus.
Waɗanda suke aiki da kaɗin auduga za su karai, masu yin lilin mai kyau za su fid da zuciya.
10 Les piliers seront brisés en morceaux. Tous ceux qui travaillent à gages auront l'âme affligée.
Masu aikin tufafi ransu zai ɓace, kuma dukan masu samun albashi za su damu.
11 Les princes de Tsoan sont complètement stupides. Le conseil des plus sages conseillers de Pharaon est devenu stupide. Comment peux-tu dire à Pharaon: « Je suis le fils des sages, le fils des anciens rois »?
Shugabannin Zowan ba kome ba ne, wawaye ke kawai; mashawarta masu hikima na Fir’auna suna ba da shawarwari marasa amfani. Yaya za ka ce wa Fir’auna, “Ni ɗaya ne cikin masu hikima, almajirin sarakuna na dā can”?
12 Où sont donc tes sages? Qu'ils te le disent maintenant, et qu'ils sachent ce que l'Éternel des armées a décidé pour l'Égypte.
Ina masu hikima suke yanzu? Bari su nuna maka su kuma sanar da abin da Ubangiji Maɗaukaki ya shirya a kan Masar.
13 Les princes de Tsoan sont devenus des insensés. Les princes de Memphis ont été trompés. Ils ont égaré l'Égypte, eux qui sont la pierre angulaire de ses tribus.
Shugabannin Zowan sun zama wawaye, an ruɗe shugabannin Memfis dutsen kan kusurwa na mutanenta su sa Masar ta kauce.
14 L'Éternel a mêlé au milieu d'elle un esprit de perversité; ils ont égaré l'Égypte dans toutes ses œuvres, comme un homme ivre titube dans son vomissement.
Ubangiji ya sa zuba musu ruhun jiri; suka sa Masar ta yi tangaɗi cikin kome da take yi, kamar yadda mutumin da ya bugu yake tangaɗi cikin amansa.
15 Il n'y aura plus pour l'Égypte d'ouvrage que tête ou queue, branche de palmier ou jonc, puisse faire.
Babu abin da Masar za tă yi, kai ko wutsiya, reshen dabino ko iwa.
16 En ce jour-là, les Égyptiens seront comme des femmes. Ils trembleront et auront peur à cause de l'agitation de la main de l'Éternel des armées, qu'il secoue sur eux.
A wannan rana Masarawa za su zama kamar mata. Za su yi rawar jiki lokacin da Ubangiji Maɗaukaki ya ɗaga hannu a kansu.
17 Le pays de Juda deviendra une terreur pour l'Égypte. Tous ceux à qui on en parlera seront effrayés, à cause des projets de l'Éternel des armées, qu'il forme contre lui.
Ƙasar Yahuda kuma za kawo fargaba ga Masarawa; kowanne da Yahuda ya ambace zai firgita, saboda abin da Ubangiji Maɗaukaki yake shiri a kansu.
18 En ce jour-là, il y aura au pays d'Égypte cinq villes qui parleront la langue de Canaan et qui jureront devant l'Éternel des armées. L'une d'elles sera appelée « la ville de la destruction ».
A wannan rana birane biyar a Masar za su yi yaren Kan’ana su kuma miƙa kai cikin yarjejjeniya ga Ubangiji Maɗaukaki. Za a ce da ɗayansu Birnin Hallaka.
19 En ce jour-là, il y aura un autel à Yahvé au milieu du pays d'Égypte, et une colonne à Yahvé à sa frontière.
A wannan rana za a kasance da bagade ga Ubangiji a tsakiyar Masar, da kuma ginshiƙin dutse Ubangiji a iyakarta.
20 Ce sera un signe et un témoignage pour l'Éternel des armées dans le pays d'Égypte; car ils crieront à l'Éternel à cause des oppresseurs, et il leur enverra un sauveur et un défenseur, et il les délivrera.
Zai zama alama da kuma shaida ga Ubangiji Maɗaukaki a ƙasar Masar. Sa’ad da suka yi kuka ga Ubangiji saboda masu zaluntarsu, zai aiko musu mai ceto da mai kāriya, zai kuma cece su.
21 Yahvé sera connu de l'Égypte, et les Égyptiens connaîtront Yahvé en ce jour-là. Oui, ils se prosterneront avec des sacrifices et des offrandes, ils feront un vœu à Yahvé et l'accompliront.
Saboda haka Ubangiji zai sanar da kansa ga Masarawa, kuma a wannan rana za su yarda da Ubangiji. Za su yi masa sujada da hadayu da hadayun hatsi; za su yi alkawura ga Ubangiji su kuma kiyaye su.
22 Yahvé frappera l'Égypte, il la frappera et la guérira. Ils reviendront à Yahvé, qui sera imploré par eux et les guérira.
Ubangiji zai bugi Masar da annoba; zai buge su ya kuma warkar da su. Za su juyo wurin Ubangiji, zai amsa roƙonsu ya kuma warkar da su.
23 En ce jour-là, il y aura une route de l'Égypte vers l'Assyrie; l'Assyrien entrera en Égypte, et l'Égyptien en Assyrie; et les Égyptiens se prosterneront avec les Assyriens.
A wannan rana za a kasance da babban hanya daga Masar zuwa Assuriya. Assuriyawa za su tafi Masar, Masarawa kuma za su tafi Assuriya. Masarawa da Assuriyawa za su yi sujada tare.
24 En ce jour-là, Israël sera le troisième avec l'Égypte et avec l'Assyrie, une bénédiction sur la terre;
A wannan rana Isra’ila za tă zama na uku, tare da Masar da Assuriya, abin albarka ga duniya.
25 car l'Éternel des armées les a bénis, en disant: « Bénis soient l'Égypte, mon peuple, l'Assyrie, l'ouvrage de mes mains, et Israël, mon héritage. »
Ubangiji Maɗaukaki zai albarkace su, yana cewa, “Albarka ta tabbata ga Masar, mutanena, Assuriya aikin hannuna, da kuma Isra’ila gādona.”