< Isaïe 14 >

1 Car Yahvé aura pitié de Jacob, il choisira encore Israël et le fixera dans son pays. L'étranger se joindra à eux, et ils s'uniront à la maison de Jacob.
Ubangiji zai yi wa Yaƙub jinƙai; zai sāke zaɓi Isra’ila yă kuma zaunar da su a ƙasarsu. Baƙi ma za su zo su zauna tare da su su haɗa kai da gidan Yaƙub.
2 Les peuples les prendront, et les amèneront dans leur lieu. La maison d'Israël les possédera dans le pays de Yahvé comme serviteurs et comme servantes. Ils emmèneront en captivité ceux dont ils étaient captifs, et ils domineront sur leurs oppresseurs.
Al’ummai za su ɗauke su su kuma kawo wurin da yake nasu. Gidan Isra’ila kuwa za tă mallaki al’ummai a matsayin bayi maza da mata a ƙasar Ubangiji. Za su mai da waɗanda suka kama su su zama kamammu su kuma yi mulki a kan waɗanda suka taɓa danne su.
3 Le jour où Yahvé vous donnera le repos de vos peines, de votre détresse et du dur service auquel vous avez été astreints,
A ranar da Ubangiji ya hutashe ku daga wahala da azaba da muguwar bauta,
4 vous reprendrez cette parabole contre le roi de Babylone, et vous direz: « Comme l'oppresseur a disparu! La ville d'or a disparu! »
za ku yi wa sarkin Babilon wannan ba’a. Mai danniya ya zo ga ƙarshe! Dubi yadda fushinsa ya ƙare!
5 Yahvé a brisé le bâton des méchants, le sceptre des dominateurs,
Ubangiji ya karye sandar mugaye, sandan mulkin masu mulki,
6 qui frappaient sans cesse les peuples dans la colère, qui dominaient les nations avec fureur, par une persécution que personne ne retenait.
wanda cikin fushi ya kashe mutane da bugu marar ƙarewa, kuma cikin fushi ya mamaye al’ummai da fushi ba ƙaƙƙautawa.
7 Toute la terre est en repos, elle est tranquille. On éclate en chants.
Dukan ƙasashe suna hutawa suna kuma cikin salama; sun ɓarke da waƙa.
8 Oui, les cyprès se réjouissent avec toi, avec les cèdres du Liban, en disant: « Depuis que tu es humilié, aucun bûcheron ne s'est dressé contre nous. »
Har itatuwan fir ma da kuma al’ul na Lebanon suna murna a kanka suna cewa, “Yanzu da aka ƙasƙantar da kai, babu wani mai yankan katakon da ya zo yă yanka mu.”
9 Le séjour des morts d'en bas s'est déplacé pour toi, afin de te rencontrer à ton arrivée. Il réveille pour toi les esprits défunts, tous les princes de la terre. Il a fait lever de leurs trônes tous les rois des nations. (Sheol h7585)
Kabari a ƙarƙashi duk ya shirya don yă sadu da kai a zuwanka; yana tā da ruhohin da suka rasu don su gaishe ka, dukan waɗanda sun taɓa zama shugabanni a duniya; ya sa suka tashi daga kujerun sarauta, dukan waɗanda suke sarakuna a kan al’ummai. (Sheol h7585)
10 Tous répondront et te demanderont: « Es-tu devenu aussi faible que nous? Es-tu devenu comme nous? »
Duk za su amsa, za su ce maka, “Ashe kai ma raunana ne, kamar mu; ka zama kamar mu.”
11 Ton faste est descendu au séjour des morts, avec le son de tes instruments à cordes. Les asticots se répandent sous toi, et les vers te couvrent. (Sheol h7585)
An yi ƙasa da dukan alfarmarka zuwa kabari, tare da surutan garayunka; tsutsotsi sun bazu a ƙarƙashinka tsutsotsi kuma suka rufe ka. (Sheol h7585)
12 Comme tu es tombé du ciel, resplendissant, fils de l'aurore! Comme tu es tombé à terre, toi qui as humilié les nations!
Yaya aka yi ka fāɗo daga sama Ya tauraron safiya, ɗan hasken asuba! An fyaɗa ka da ƙasa, kai da ka taɓa ƙasƙantar da al’ummai!
13 Tu disais en ton cœur: « Je monterai au ciel! J'élèverai mon trône au-dessus des étoiles de Dieu! Je m'assiérai sur la montagne de l'assemblée, à l'extrême nord!
Ka yi tunani a ranka ka ce, “Zan hau zuwa sama; zan ɗaga kursiyina sama da taurarin Allah; zan zauna a kursiyi a kan dutsen taro, a can ƙurewar saman dutse mai tsarki.
14 Je monterai au-dessus des hauteurs des nuages. Je me rendrai semblable au Très-Haut! »
Zan haura can bisa gizagizai; zan mai da kaina kamar Mafi Ɗaukaka.”
15 Mais on te fera descendre au séjour des morts, au fond de la fosse. (Sheol h7585)
Amma ga shi an gangara da kai zuwa kabari, zuwa zurfafan rami. (Sheol h7585)
16 Ceux qui te verront te regarderont fixement. Ils te considéreront en disant: « Est-ce là l'homme qui a fait trembler la terre, qui a ébranlé les royaumes,
Waɗanda suka gan ka sun zura maka ido, suna tunani abin da zai same ka. “Wannan mutumin ne ya girgiza duniya ya kuma sa mulkoki suka razana,
17 qui a rendu le monde comme un désert et a renversé ses villes, qui n'a pas relâché ses prisonniers dans leur maison? ».
mutumin da ya mai da duniya ta zama hamada, wanda ya tumɓuke biranenta bai kuma bar kamammunsa suka tafi ba?”
18 Tous les rois des nations dorment dans la gloire, chacun dans sa maison.
Dukan sarakunan duniya suna kwance a mace, kowa a kabarinsa.
19 Mais toi, tu es rejeté de ton sépulcre comme un rameau abominable, tu es revêtu des morts que l'épée transperce, qui descendent vers les pierres de la fosse, comme un cadavre foulé aux pieds.
Amma an jefar da kabarinka kamar reshen da aka ƙi; an rufe ka da waɗanda aka kashe, tare da waɗanda aka soke da takobi, waɗanda suka gangara zuwa duwatsun rami. Kamar gawar da aka tattake da ƙafa,
20 Tu ne les rejoindras pas dans la sépulture, car tu as détruit ton pays. Tu as tué ton peuple. La descendance des méchants ne sera pas nommée à jamais.
ba za a haɗa ka tare da su a jana’iza ba, gama ka hallaka ƙasarka ka kuma kashe mutanenka. Ba za a ƙara ambaci zuriyarka masu aikata mugunta ba.
21 Préparez l'abattage de ses enfants à cause de l'iniquité de leurs pères, afin qu'ils ne se lèvent pas pour posséder la terre, et remplir de villes la surface du monde.
A shirya wuri don a yayyanka’ya’yansa maza saboda zunuban kakanninsu; kada a reno su su gāji ƙasar su cika duniya da biranensu.
22 « Je me lèverai contre eux », dit Yahvé des armées, « et j'exterminerai de Babylone le nom et le reste, le fils et le fils du fils », dit Yahvé.
“Zan yi gāba da su,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan kau da sunan Babilon da waɗanda suka rage da rai a cikinta,’ya’yanta da zuriyarta,” in ji Ubangiji.
23 « J'en ferai aussi un territoire pour le porc-épic, et des mares d'eau. Je la balaierai avec le balai de la destruction », dit Yahvé des armées.
“Zan mai da ita wuri domin mujiyoyi da kuma fadama; zan share ta da tsintsiyar hallaka,” Ni Ubangiji Maɗaukaki na faɗa.
24 L'Éternel des armées l'a juré, en disant: Il arrivera ce que j'ai pensé, et ce que j'ai voulu, ce qui arrivera.
Ubangiji Maɗaukaki ya rantse, “Tabbatacce, kamar yadda na riga na shirya, haka zai kasance, kuma kamar yadda na nufa, haka zai zama.
25 Je briserai l'Assyrien dans mon pays, et je le foulerai aux pieds sur mes montagnes. Alors son joug les quittera, et son fardeau quittera leurs épaules.
Zan ragargazar da Assuriya a cikin ƙasata; a kan duwatsuna zan tattake shi. Za a ɗauke nauyin da ya sa wa mutanena, a kuma ɗauke nauyinsa daga kafaɗunsu.”
26 Tel est le plan qui est arrêté pour toute la terre. C'est la main qui s'étend sur toutes les nations.
Wannan shi ne shirin da na yi domin dukan duniya; wannan shi ne hannun da aka miƙa a bisa dukan al’ummai ke nan.
27 Car l'Éternel des armées a fait un plan, et qui pourra l'arrêter? Sa main est étendue, et qui pourra la faire reculer? ».
Gama Ubangiji Maɗaukaki ya ƙudura ya yi wannan, wa kuwa zai hana shi? Ya riga ya miƙa hannunsa, wa zai komar da shi?
28 Cette charge était l'année de la mort du roi Achaz.
Wannan abin da Allah ya yi magana ya zo ne a shekarar da Sarki Ahaz ya mutu.
29 Ne te réjouis pas, Philistie, toi toute, parce que la verge qui te frappait est brisée; car de la racine du serpent sortira une vipère, et son fruit sera un serpent volant ardent.
Kada ku yi farin ciki, dukanku Filistiyawa, cewa sandar da ta buge ku ta karye; daga saiwar wannan maciji wani mugun maciji mai dafi zai taso,’ya’yansa za su zama wani maciji masu dafi mai tashi sama.
30 Les premiers-nés des pauvres mangeront, et les indigents se coucheront en sécurité; mais je tuerai ta racine par la famine, et ton reste sera tué.
Mafi talauci na matalauta zai sami wurin kiwo, mabukata kuma za su kwana lafiya. Amma zan hallakar da saiwarka da matsananciyar yunwa; za tă kashe naka da suka rage da rai.
31 Hurle, porte! Pleure, ville! Tu es fondue, Philistia, toi toute entière; car la fumée sort du nord, et il n'y a pas de traînard dans ses rangs.
Ki yi ihu, ya ke ƙofa! Yi kururuwa, ya ke birni! Ku razana, dukanku Filistiyawa! Ƙunshin hayaƙi yana tasowa daga arewa, kuma babu matsorata a cikin sojojinsa.
32 Que répondront-ils aux messagers de la nation? Que Yahvé a fondé Sion, et qu'en elle se réfugieront les malheureux de son peuple.
Wace amsa ce za a bayar wa jakadun wannan al’umma? “Ubangiji ya kafa Sihiyona, kuma a cikinta mutanensa masu shan azaba za su sami mafaka.”

< Isaïe 14 >