< Isaïe 10 >

1 Malheur à ceux qui décrètent des ordonnances injustes, Et aux rédacteurs qui écrivent des ordonnances oppressives
Kaiton waɗanda suke kafa dokokin rashin gaskiya, waɗanda suke ba da ƙa’idodin danniya,
2 pour priver de justice les indigents, Et pour dépouiller de leurs droits les pauvres de mon peuple, Afin que les veuves soient leur butin, Et qu'ils fassent de l'orphelin leur proie!
don su hana matalauta hakkinsu su kuma ƙi yin shari’ar gaskiya a kan waɗanda suke zaluntar mutanena, suna ƙwace wa gwauraye dukiyarsu suna kuma yi wa marayu ƙwace.
3 Que ferez-vous au jour du châtiment, au jour de la désolation qui viendra de loin? Vers qui fuiras-tu pour demander du secours? Où laisserez-vous vos richesses?
Me za ku yi a ranan nan ta hukunci, sa’ad da masifa ta zo daga nesa? Ga wa za ku tafi don neman taimako? Ina za ku bar dukiyarku?
4 Ils ne se prosterneront que sous les prisonniers, et tomberont sous les morts. Pour autant, sa colère n'est pas détournée, mais sa main est encore tendue.
Babu abin da zai rage sai cizon haƙora a cikin kamammu ko mutuwa cikin waɗanda aka kashe. Duk da haka, fushinsa bai huce ba, hannunsa har yanzu yana a miƙe.
5 Hélas Assyrien, la verge de ma colère, le bâton dans la main duquel est ma fureur!
“Kaiton Assuriya, sandar fushina, a hannun da kulkin fushina yake!
6 Je l'envoie contre une nation profane, et contre le peuple qui m'irrite, je lui donne l'ordre de prendre le pillage et le butin, et de les fouler comme la boue des rues.
Na aike shi gāba da al’umma marar sanin Allah, na tura shi gāba da mutanen da suka ba ni fushi, don yă kwashe ganima yă kuma yi wason ganima, yă tattake su kamar laka a tituna.
7 Mais ce n'est pas ce qu'il veut, et ce n'est pas ce que son cœur pense; mais il a dans le cœur de détruire, et d'exterminer non pas quelques nations.
Amma ba abin da ya yi niyya ke nan ba, ba abin da yake da shi a zuciya ba; manufarsa shi ne yă hallaka, yă kuma kawo ƙarshen al’ummai da yawa.
8 Car il dit: « Tous mes princes ne sont-ils pas des rois?
Ya ce, ‘Dukan shugabannin yaƙina ba sarakuna ba ne?’
9 Calno n'est-elle pas comme Carménich? Hamath n`est-elle pas comme Arpad? Samarie n'est-elle pas comme Damas? »
‘Kalno bai kasance kamar Karkemish ba? Hamat bai zama kamar Arfad Samariya kuma kamar Damaskus ba?
10 Comme ma main a trouvé les royaumes des idoles, dont les images gravées dépassaient celles de Jérusalem et de Samarie,
Yadda hannuna ya ƙwace mulkokin gumaka, mulkokin da siffofinsu suka fi na Urushalima da Samariya,
11 ne ferai-je pas, comme j'ai fait à Samarie et à ses idoles, à Jérusalem et à ses idoles?
ba zan yi da Urushalima da siffofinta yadda na yi da Samariya da gumakanta ba?’”
12 C'est pourquoi, lorsque l'Éternel aura accompli toute son œuvre sur la montagne de Sion et sur Jérusalem, je punirai le fruit du cœur orgueilleux et volontaire du roi d'Assyrie, et l'insolence de ses regards arrogants.
Sa’ad da Ubangiji ya gama dukan aikinsa gāba da Dutsen Sihiyona da Urushalima, zai ce, “Zan hukunta sarkin Assuriya saboda fariya na gangancin zuciyarsa da kuma kallon reni na idanunsa.
13 Car il a dit: « C'est par la force de ma main que j'ai agi, et par ma sagesse, car j'ai de l'intelligence. J'ai fait disparaître les limites des peuples, et j'ai dérobé leurs trésors. Comme un vaillant homme, j'ai abattu leurs chefs.
Gama ya ce, “‘Ta wurin ƙarfin hannuna ne na aikata wannan, da kuma ta wurin hikimata, gama ina da fahimi. Na kau da iyakokin ƙasashe, na washe dukiyarsu; a matsayina na mai iko, na mamaye sarakunansu.
14 Ma main a trouvé les richesses des peuples comme un nid, et comme on recueille des œufs abandonnés, j'ai recueilli toute la terre. Il n'y en a pas un qui ait remué l'aile, qui ait ouvert la bouche, ou qui ait gazouillé. »
Kamar yadda mutum yakan miƙa hannu cikin sheƙar tsuntsu haka hannuna ya je ya washe dukiyar al’ummai; kamar yadda mutane sukan tattara ƙwai, haka na tattara dukan ƙasashe; ba tsuntsun da ya kakkaɓe fikafiki, ko yă buɗe baki don yă yi kuka.’”
15 La hache se vante-t-elle de celui qui coupe? La scie doit-elle s'élever au-dessus de celui qui la scie? Comme si une verge devait élever ceux qui la soulèvent, ou comme si un bâton devait élever quelqu'un qui n'est pas du bois.
Gatari ya taɓa fin wanda yake amfani da shi girma, ko zarto yă yi wa wanda yake amfani da shi taƙama? Sanda za tă girgiza mutumin da yake riƙe da ita, ko kuwa kulki yă jijjiga mutumin da yake riƙe da katako!
16 C'est pourquoi l'Éternel, l'Éternel des armées, enverra parmi ses gros la maigreur, et sous sa gloire s'allumera une ardeur comme celle d'un feu.
Saboda haka Ubangiji Maɗaukaki, zai aukar da cuta mai kisa a kan ƙosassu jarumawa; a ƙarƙashin sansaninsa zai ƙuna wuta kamar harshen wuta.
17 La lumière d'Israël sera comme un feu, et son Saint comme une flamme; et il brûlera et dévorera ses épines et ses ronces en un seul jour.
Hasken Isra’ila zai zo kamar wuta, Mai Tsarkinsu zai zama kamar wuta; a rana guda zai ƙone yă kuma cinye ƙayayyuwa da sarƙaƙƙiyarsa.
18 Il consumera la gloire de sa forêt et de son champ fertile, l'âme et le corps. Ce sera comme lorsqu'un porte-étendard s'évanouit.
Darajar jejinsa da gonakinsa masu dausayi za a hallaka su ɗungum, kamar yadda ciwo yakan kashe mutum.
19 Le reste des arbres de sa forêt sera peu nombreux, au point qu'un enfant pourrait écrire leur nombre.
Sauran itatuwan jejinsa kuma za su ragu ko ɗan ƙaramin yaro ma zai iya ƙidaya su.
20 En ce jour-là, le reste d'Israël et les réchappés de la maison de Jacob ne s'appuieront plus sur celui qui les frappait, mais ils s'appuieront sur Yahvé, le Saint d'Israël, dans la vérité.
A wannan rana raguwar Isra’ila, waɗanda suka ragu na gidan Yaƙub, ba za su ƙara dogara ga wanda ya kusa hallaka su ba amma za su dogara ga Ubangiji, Mai Tsarkin nan na Isra’ila.
21 Un reste reviendra, le reste de Jacob, vers le Dieu puissant.
Raguwa za tă komo, raguwar Yaƙub za su komo ga Maɗaukaki Allah.
22 Car si ton peuple, Israël, est comme le sable de la mer, un reste seulement reviendra. Une destruction est prévue, débordante de justice.
Ko da yake mutanenka, ya Isra’ila, sun zama kamar yashin bakin teku, raguwa ce kurum za tă komo. A ƙaddara hallaka, mai mamayewa da mai adalci.
23 Car l'Éternel, le Yahvé des armées, fera une destruction complète, et déterminée, sur toute la terre.
Ubangiji Maɗaukaki, zai sa hallakar da aka ƙaddara a kan dukan ƙasa ta faru.
24 C'est pourquoi l'Éternel, le Yahvé des armées, dit: « Mon peuple qui habite Sion, ne craignez pas l'Assyrien, même s'il vous frappe de sa verge et qu'il lève son bâton contre vous, comme l'Égypte.
Saboda haka, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ya mutanena masu zama a Sihiyona, kada ku ji tsoron Assuriyawa, waɗanda suka dūke ku da sanda suka kuma ɗaga kulki a kanku, kamar yadda Masar ta yi.
25 Car encore un tout petit moment, et l'indignation contre vous s'accomplira, et ma colère se portera sur sa destruction. »
Ba da daɗewa ba fushina a kanku zai zo ga ƙarshe hasalata kuma za tă koma ga hallakarsu.”
26 Yahvé des armées suscitera contre lui un fléau, comme lors du massacre de Madian au rocher d'Oreb. Sa verge sera au-dessus de la mer, et il la lèvera comme il l'a fait contre l'Égypte.
Ubangiji Maɗaukaki zai bulale su da tsumagiya, kamar sa’ad da ya bugi Midiyan a dutsen Oreb; zai kuma ɗaga sandarsa a bisa ruwaye, yadda ya yi a Masar.
27 En ce jour-là, son fardeau disparaîtra de ton épaule, et son joug de ton cou, et le joug sera détruit à cause de l'huile d'onction.
A wannan rana zai ɗauke nauyi daga kafaɗarku, nauyinsu daga wuyanku; za a karye karkiya domin kun yi ƙiba ƙwarai.
28 Il est arrivé à Aiath. Il passe par Migron. A Michmash, il range ses bagages.
Sun shiga Ayiyat; sun bi ta Migron; sun adana tanade-tanade a Mikmash.
29 Ils ont franchi le col. Ils se logent à Guéba. Rama tremble. Gibéa de Saül s'est enfuie.
Suka ƙetare ta hanya, suka kuma ce, “Za mu kwana a Geba.” Rama ta firgita; Gibeya ta Shawulu ta gudu.
30 Crie de ta voix, fille de Gallim! Écoute, Laisha! Pauvre Anathoth!
Ki yi ihu, ya Diyar Gallim! Ki saurara, ya Layisha! Kayya, Anatot abin tausayi!
31 Madmena est une fugitive. Les habitants de Guébim fuient pour se mettre en sûreté.
Madmena tana gudu; mutanen Gebim sun ɓuya.
32 Aujourd'hui même, il s'arrête à Nob. Il serre la main à la montagne de la fille de Sion, à la colline de Jérusalem.
A wannan rana za su dakata a Nob; za su jijjiga ƙarfinsu a dutsen Diyar Sihiyona, a tudun Urushalima.
33 Voici que le Seigneur, l'Éternel des armées, fauche les rameaux avec terreur. Les grands seront abattus, et les grands seront abaissés.
Duba, Ubangiji Maɗaukaki, zai ragargaza rassa da iko mai girma. Za a sassare itatuwa masu ganyaye, za a yanke dogayen itatuwa har ƙasa.
34 Ilabattra avec le fer les fourrés de la forêt, et le Liban tombera sous les coups du Puissant.
Zai sassare itatuwan jeji da gatari har ƙasa; Lebanon zai fāɗi a gaban Mai Iko.

< Isaïe 10 >