< Aggée 1 >

1 La deuxième année du roi Darius, le sixième mois, le premier jour du mois, la parole de Yahvé fut adressée par Aggée, le prophète, à Zorobabel, fils de Shealtiel, gouverneur de Juda, et à Josué, fils de Jotsadak, le grand prêtre, en ces termes:
A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus, a rana ta fari ga watan shida, maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai zuwa ga Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, gwamnan Yahuda, da kuma Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist.
2 « Voici ce que dit Yahvé des armées: Ce peuple dit: 'Le temps n'est pas encore venu, le temps de construire la maison de Yahvé'. »
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Waɗannan mutane sun ce, ‘Lokaci bai yi ba tukuna da za a gina gidan Ubangiji.’”
3 Et la parole de Yahvé vint par Aggée, le prophète, en ces termes:
Sa’an nan maganar Ubangiji ta zo ta wurin annabi Haggai cewa,
4 Est-ce le moment pour vous d'habiter dans vos maisons à pan coupé, tandis que cette maison est détruite?
“Ashe, lokaci ya yi da za ku zauna a ɗakunan da kuka yi da rufin katako, amma haikalin nan yana zaman kufai?”
5 Voici donc ce que dit l'Éternel des armées: « Considérez vos voies.
To, ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
6 Vous avez beaucoup semé, et vous rapportez peu. Vous mangez, mais vous n'avez pas assez. Vous buvez, mais vous n'êtes pas rassasiés. Vous vous habillez, mais personne n'a chaud; et celui qui gagne un salaire le gagne pour le mettre dans un sac troué.''
Kun shuka da yawa, amma kun girbe kaɗan. Kun ci, amma ba ku ƙoshi ba. Kun sha, amma ba ku kashe ƙishirwa ba. Kun sa tufafi, amma ba ku ji ɗumi ba. Kuna karɓar albashi, ya zama sai ka ce kuna zuba a hudajjen aljihu.”
7 Voici ce que dit l'Éternel des armées: « Considère tes voies.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, “Ku lura da al’amuranku.
8 Monte sur la montagne, apporte du bois, et construis la maison. J'y prendrai plaisir, et je serai glorifié, dit l'Éternel.
Ku haura zuwa kan duwatsu ku sauko da katakai don ku gina gidan, don ni ma in ji daɗinsa, in kuma sami ɗaukaka,” in ji Ubangiji.
9 Tu as cherché beaucoup, et voici qu'il n'y a eu que peu de choses; et quand tu l'as rapportée à la maison, je l'ai soufflée. Pourquoi? dit l'Éternel des armées, à cause de ma maison qui gît, tandis que chacun de vous est occupé de sa propre maison.
“Ga shi, kukan sa rai za ku sami da yawa, amma sai ku ga kun sami kaɗan. Ɗan kaɗan ɗin ma da kukan kawo gida, nakan hura shi yă tafi. Me ya sa yake faruwa haka?” In ji Ubangiji Maɗaukaki. “Saboda gidana da yake zaman kango, yayinda kowannenku yana faman gina gidansa.
10 C'est pourquoi, à cause de vous, les cieux retiennent la rosée, et la terre retient ses fruits.
Shi ya sa, saboda ku sammai sun ƙi saukar da raɓa, ƙasa kuma ta ƙi ba da amfani.
11 J'ai appelé la sécheresse sur la terre, sur les montagnes, sur le blé, sur le vin nouveau, sur l'huile, sur ce que produit le sol, sur les hommes, sur le bétail, et sur tout le travail des mains. »
Na kawo fări a ƙasar, da a kan duwatsu, da a kan hatsi, da a kan dukan abin da yake tsirowa daga ƙasa, da a kan mutane, da a kan dabbobi da kuma a kan wahalar hannuwanku.”
12 Et Zorobabel, fils de Shealtiel, et Josué, fils de Jehozadak, le grand prêtre, et tout le reste du peuple, obéirent à la voix de Yahvé, leur Dieu, et aux paroles du prophète Aggée, comme Yahvé, leur Dieu, l'avait envoyé; et le peuple craignit Yahvé.
Sa’an nan sai Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, da Yoshuwa ɗan Yehozadak, wanda yake babban firist, da kuma dukan raguwar jama’ar suka yi biyayya da muryar Ubangiji Allahnsu da kuma saƙon annabi Haggai, domin Ubangiji Allahnsu ne ya aiko shi. Mutane kuwa suka ji tsoron Ubangiji.
13 Alors Aggée, le messager de Yahvé, transmit au peuple le message de Yahvé, en disant: « Je suis avec vous, dit Yahvé.
Sai Haggai, ɗan saƙon Ubangiji, ya ba da wannan saƙo na Ubangiji ga mutane cewa, “Ina tare da ku” in ji Ubangiji.
14 L'Éternel réveilla l'esprit de Zorobabel, fils de Schealthiel, gouverneur de Juda, l'esprit de Josué, fils de Jotsadak, le souverain sacrificateur, et l'esprit de tout le reste du peuple; et ils vinrent travailler à la maison de l'Éternel des armées, leur Dieu,
Saboda haka Ubangiji ya motsa zuciyar Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel, wanda yake gwamna a Yahuda, da kuma zuciyar Yoshuwa ɗan Yehozadak, babban firist, da kuma zukatan dukan raguwar jama’ar. Suka zo suka fara aiki a gidan Ubangiji Maɗaukaki, Allahnsu,
15 le vingt-quatrième jour du mois, le sixième mois, la seconde année du roi Darius.
a ranar ashirin da huɗu ga watan shida. A shekara ta biyu ta mulkin Sarki Dariyus,

< Aggée 1 >