< Habacuc 1 >

1 Révélation que vit Habacuc, le prophète.
Saƙon da annabi Habakkuk ya karɓa.
2 Yahvé, jusqu'à quand vais-je crier, et tu n'écouteras pas? Je crie vers toi « Violence! » et tu ne sauveras pas?
Har yaushe, ya Ubangiji, zan yi kukan neman taimako, amma ka ƙi ji? Ina kuka a gare ka saboda zalunci amma ba ka ce ufam ba.
3 Pourquoi me montres-tu l'iniquité, et regardes-tu la perversité? Car la destruction et la violence sont devant moi. Il y a des querelles, et la dispute s'élève.
Me ya sa ka bari ina ta kallon rashin gaskiya? Me ya sa kake barin abin da ba daidai ba? Hallaka da tashin hankali suna a gabana; ga rashin jituwa da faɗa ko’ina.
4 C'est pourquoi la loi est paralysée, et la justice ne prévaut jamais; car les méchants entourent les justes; c'est pourquoi la justice sort pervertie.
Saboda haka ba a bin doka, shari’a kuma ba ta aiki. Mugaye sun kewaye masu adalci don a hana gaskiya tă yi aiki.
5 « Regardez parmi les nations, observez, et soyez étonnés; car je fais en vos jours une œuvre que vous ne croirez pas, même si on vous la raconte.
“Ka dubi al’ummai, ka gani, ka sha mamaki. Ga shi zan yi wani abu a kwanakinka, wanda ko ma an faɗa maka ba za ka gaskata ba.
6 Car voici, je fais surgir les Chaldéens, cette nation âpre et hâtive qui marche sur toute la largeur de la terre, pour posséder des demeures qui ne sont pas à elle.
Zan tā da Babiloniyawa, waɗannan marasa hankali da kuma marasa tausayi; masu gajeren haƙuri, waɗanda suke ratsa ko’ina a duniya don su ƙwace wuraren zaman da ba nasu ba.
7 Ils sont craints et redoutés. Leur jugement et leur dignité viennent d'eux-mêmes.
Suna da bantsoro da firgitarwa; dokoki da ƙa’idodinsu ne kawai suka sani.
8 Leurs chevaux sont plus rapides que les léopards, Et plus féroces que les loups du soir. Leurs cavaliers avancent fièrement. Oui, leurs cavaliers viennent de loin. Ils volent comme l'aigle qui se précipite pour dévorer.
Dawakansu sun fi damisoshi sauri, sun fi kyarketan yamma zafin rai. Mahayansu suna zuwa a guje; mahayansu daga nesa suka fito. Suna firiya kamar ungulu mai sauka da gaggawa don yă ci mushe;
9 Ils viennent tous pour la violence. Leurs hordes sont tournées vers l'avant. Ils rassemblent les prisonniers comme du sable.
duk sukan zo da nufin tā-da-na-zaune-tsaye. Ana jin tsoronsu tun ma kafin su iso suna tattara bayi kamar yashi.
10 Ils se moquent des rois, Et les princes sont pour eux une dérision. Ils se moquent de toute forteresse, car ils construisent une rampe de terre et la prennent.
Sukan yi wa sarakuna ba’a su kuma rena masu mulki. Sukan yi wa dukan birane masu mafaka dariya; sukan tara ƙasa su hau, su cinye abokan gābansu da yaƙi.
11 Puis ils passent comme le vent et s'en vont. Ils sont vraiment coupables, eux dont la force est leur dieu. »
Sa’an nan su wuce da sauri kamar iska, mutane ne masu laifi, waɗanda ƙarfinsu shi ne allahnsu.”
12 N'es-tu pas de toute éternité, Yahvé mon Dieu, mon Saint? Nous ne mourrons pas. Yahvé, tu les as établis pour juger. Toi, Rocher, tu l'as établi pour punir.
Ya Ubangiji, ba tun fil azal kake ba? Ya Allahna, Mai Tsarkina, ba za mu mutu ba. Ya Ubangiji ka sanya su su tabbatar da hukunci; Ya Dutse, ka naɗa su don su yi hukunci.
13 Toi qui as des yeux plus purs que ceux qui voient le mal, et qui ne peux regarder la perversité, pourquoi tolères-tu les perfides et te tais-tu quand le méchant engloutit celui qui est plus juste que lui,
Idanunka masu tsarki ne da suka fi gaban duban mugunta; ba ka amince da abin da ke ba daidai ba. To, don me ka ƙyale munafukai suna cin karensu ba babbaka? Me ya sa kake shiru sa’ad da mugaye suke haɗiye adalai da suka fi su adalci?
14 et rend les hommes semblables aux poissons de la mer, aux reptiles qui n'ont pas de maître sur eux?
Ka mai da maza kamar kifin teku, kamar halittun tekun da ba su da shugaba.
15 Il les prend tous avec l'hameçon. Il les attrape dans son filet et les recueille dans sa gibecière. C'est pourquoi il se réjouit et se réjouit.
Mugu abokin gāba yakan kama su duka da ƙugiya, yă jawo su waje da abin kamun kifinsa, yă tattara su cikin ragarsa, ta haka yakan yi murna da farin ciki.
16 C'est pourquoi il sacrifie à son filet et brûle de l'encens à sa drague, parce que grâce à eux sa vie est luxueuse et sa nourriture est bonne.
Saboda haka yakan yi hadaya wa abin kamun kifinsa yă kuma ƙona turare wa ragarsa, domin ta wurin abin kamun kifinsa ne yake yin rayuwar jin daɗi yă kuma zaɓi irin abincin da yake so.
17 Videra-t-il donc continuellement son filet, Et tuera-t-il les nations sans pitié?
Zai ci gaba da juye abin kamun kifinsu ke nan, suna hallaka al’ummai ba tausayi?

< Habacuc 1 >