< Habacuc 2 >
1 Je me tiendrai à ma garde et je me placerai sur les remparts, et je regarderai pour voir ce qu'il me dira, et ce que je répondrai au sujet de ma plainte.
Zan tsaya wurin tsarona in kuma zauna a kan katanga; zan jira in ga abin da zai ce mini, da kuma wace amsa zan bayar ga wannan kuka.
2 Yahvé me répondit: « Écris la vision, et mets-la en évidence sur des tablettes, afin que celui qui court puisse la lire.
Sa’an nan Ubangiji ya amsa ya ce, “Ka rubuta wannan ru’uya ka bayyana ta a fili a kan alluna don mai shela yă ruga da ita, yă kai.
3 Car la vision est encore pour le temps fixé, et elle se hâte vers la fin, et ne se démentira pas. Même si elle prend du temps, attendez-la, car elle viendra sûrement. Elle ne tardera pas.
Gama ru’uyar tana jiran ƙayyadadden lokaci; tana zancen ƙarshe kuma ba za tă zama ƙarya ba. Ko da ka ga kamar tana jinkiri, ka jira ta; lalle za tă zo, ba za tă makara ba.
4 Voici, son âme s'enfle d'orgueil. Il n'est pas droit en lui, mais le juste vivra par sa foi.
“Duba, abokin gāba ya cika da ɗaga kai; sha’awarsa ba daidai ba ce, amma mai adalci zai rayu ta wurin bangaskiyarsa,
5 Oui, de plus, le vin est perfide: un homme arrogant qui ne reste pas chez lui, qui élargit son désir comme le séjour des morts; il est comme la mort et ne peut être satisfait, mais il rassemble à lui toutes les nations et entasse à lui tous les peuples. (Sheol )
ba shakka, ruwan inabi ya yaudare shi; yana fariya kuma ba ya hutu. Domin shi mai haɗama ne kamar kabari kuma kamar mutuwa, ba ya ƙoshi; yakan tattara dukan al’ummai wa kansa yana kuma kama dukan mutane su zama kamammu. (Sheol )
6 Tous ne prendront-ils pas contre lui une parabole et un proverbe de raillerie, et ne diront-ils pas: « Malheur à celui qui augmente ce qui ne lui appartient pas, et qui s'enrichit par l'extorsion! ». Jusqu'à quand? »
“Dukansu ba za su yi masa tsiya, suna yin masa ba’a da dariya ba, suna cewa, “‘Kaito ga wannan wanda ya tara wa kansa kayan sata ya kuma wadatar da kansa da kayan ƙwace! Har yaushe wannan abu zai ci gaba?’
7 Tes débiteurs ne vont-ils pas se lever soudainement, réveiller ceux qui te font trembler, et tu seras leur victime?
Masu binka bashi ba za su taso maka nan da nan ba? Ba za su farka su sa ka fargaba ba? Ta haka ka zama ganima a gare su.
8 Parce que tu as pillé de nombreuses nations, tout le reste des peuples te pillera à cause du sang des hommes, des violences faites au pays, à la ville et à tous ceux qui l'habitent.
Domin ka washe al’ummai masu yawa, mutanen da suka rage za su washe ka. Domin ka zub da jinin mutane; ka hallaka ƙasashe, da birane, da kuma kowa da yake cikinsu.
9 Malheur à celui qui obtient un mauvais gain pour sa maison, afin de placer son nid en haut, afin d'être délivré de la main du malheur!
“Kaito ga wanda ya gina masarautarsa da ƙazamar riba don yă kafa sheƙarsa can bisa, don yă tsere wa zama kango!
10 Tu as conçu la honte de ta maison en exterminant de nombreux peuples, et tu as péché contre ton âme.
Ka ƙulla lalacin mutane masu yawa, ta haka ka kunyatar da gidanka ka kuma hallaka ranka.
11 Car la pierre criera de la muraille, et la poutre de la charpente y répondra.
Duwatsun katanga za su yi kuka, ginshiƙan katako kuma za su amsa.
12 Malheur à celui qui bâtit une ville par le sang, et qui affermit une cité par l'iniquité!
“Kaiton mutumin da ya gina birni da jinin da ya zubar ya kuma kafa gari ta wurin mugun aiki!
13 Voici, n'est-ce pas de la part de l'Éternel des armées que les peuples travaillent pour le feu, et que les nations se fatiguent pour la vanité?
Ba Ubangiji Maɗaukaki ne ya ƙudura cewa wahalar mutane ta zama mai kawai don wuta ba, cewa al’ummai su gajiyar da kansu a banza ba?
14 Car la terre sera remplie de la connaissance de la gloire de l'Éternel, comme les eaux couvrent la mer.
Gama duniya za tă cika da sanin ɗaukakar Ubangiji, yadda ruwaye suka rufe teku.
15 « Malheur à celui qui donne à boire à son prochain, en versant votre vin brûlant jusqu'à ce qu'ils soient ivres, afin que vous puissiez contempler leurs corps nus!
“Kaito wanda ya ba wa maƙwabtansa abin sha, yana ta zubawa daga salkan ruwan inabi har sai sun bugu, don dai yă ga tsiraicinsu.
16 Vous êtes remplis de honte, et non de gloire. Vous aussi, vous boirez et serez exposés! La coupe de la main droite de Yahvé se retournera contre vous, et l'opprobre couvrira votre gloire.
Za ka cika da kunya a maimakon ɗaukaka. Yanzu lokacinka ne! Kai ma ka sha, a kuma tone asirinka! Gama kwaf na hannun daman Ubangiji yana zuwa kewaye da kai, abin kunya kuma zai rufe darajarka.
17 Car la violence faite au Liban vous accablera, et la destruction des animaux vous terrifiera, à cause du sang des hommes et de la violence faite au pays, à chaque ville et à ceux qui y habitent.
Ɓarnar da ka yi wa Lebanon zai komo kanka, kuma hallakar dabbobin da ka yi zai sa dabbobi su tsorata ka. Gama ka zub da jinin mutum; ka hallaka ƙasashe, da birane, da kuma kowa da yake cikinsu.
18 « Quelle valeur a l'image gravée, pour que son créateur l'ait gravée; l'image fondue, pour que celui qui en façonne la forme s'y fie, pour fabriquer des idoles muettes?
“Ina amfanin gunki da mutum ne ya sassaƙa? Ko siffar da take koyar da ƙarya? Gama wanda ya yi shi yana dogara ne ga halittarsa; ya yi gumakan da ba sa magana.
19 Malheur à celui qui dit au bois: « Réveille-toi! » ou à la pierre muette: « Lève-toi! ». Est-ce là un enseignement? Voici, elle est recouverte d'or et d'argent, et il n'y a en elle aucun souffle.
Kaito wanda ya ce da katako, ‘Rayu!’ Ko kuwa dutse marar rai, ‘Farka!’ Zai iya bishewa ne? An dalaye shi da zinariya da azurfa; ba numfashi a cikinsa.”
20 Mais Yahvé est dans son temple saint. Que toute la terre se taise devant lui! »
Amma Ubangiji yana a cikin haikalinsa mai tsarki; bari dukan duniya tă yi shiru a gabansa.