< Genèse 9 >

1 Dieu bénit Noé et ses fils, et leur dit: Soyez féconds, multipliez, et remplissez la terre.
Sa’an nan Allah ya sa wa Nuhu da’ya’yansa maza albarka, yana ce musu, “Ku haifi’ya’ya, ku ƙaru, ku kuma cika duniya.
2 La crainte de vous et la peur de vous seront sur tous les animaux de la terre et sur tous les oiseaux du ciel. Tout ce qui se meut sur la terre, et tous les poissons de la mer, sont livrés entre tes mains.
Dukan namun jeji da dukan tsuntsayen sama da kowace halitta mai rarrafe a ƙasa, da dukan kifayen teku, za su riƙa jin tsoronku, suna fargaba. An sa su a cikin hannuwanku.
3 Tout ce qui se déplace et qui vit te servira de nourriture. Comme je t'ai donné l'herbe verte, je t'ai tout donné.
Kome da yake da rai wanda yake tafiya, zai zama abincinku. Kamar yadda na ba ku kowane irin ganye, haka na ba ku kome da kome.
4 Mais la chair avec sa vie, c'est-à-dire son sang, vous n'en mangerez pas.
“Akwai abu ɗaya da ba za ku ci ba, wato, nama wanda jininsa yake cikinsa tukuna.
5 Je demanderai compte du sang de votre vie. Je l'exigerai de la part de tout animal. De la main de l'homme, même de la main du frère de l'homme, je demanderai la vie de l'homme.
Game da jinin ranka kuwa lalle zan bukaci lissafi. Zan bukaci lissafi daga kowane dabba. kuma daga kowane mutum, shi ma zan bukaci lissafi game da ran ɗan’uwansa.
6 Si quelqu'un verse le sang de l'homme, son sang sera versé par l'homme, car Dieu a créé l'homme à son image.
“Duk wanda ya zub da jinin mutum, ta hannun mutum za a zub da jininsa; gama a cikin siffar Allah ne, Allah ya yi mutum.
7 Soyez féconds et multipliez. Augmentez en abondance sur la terre, et multipliez en elle. »
Amma ku, ku yi ta haihuwa, ku ƙaru; ku yaɗu a duniya, ku yi yawa a bisanta.”
8 Dieu parla à Noé et à ses fils avec lui, et dit:
Sai Allah ya ce wa Nuhu da’ya’yansa,
9 « Quant à moi, voici que j'établis mon alliance avec toi, et avec ta descendance après toi,
“Yanzu na kafa alkawarina da ku da zuriyarku a bayanku,
10 et avec tous les êtres vivants qui sont avec toi: les oiseaux, le bétail, et tous les animaux de la terre avec toi, de tous ceux qui sortent du navire, tous les animaux de la terre.
da kowace halitta mai rai wadda ta kasance tare da kai; wato, tsuntsaye da dabbobin gida da kuma dukan namun jeji, duk dai iyakar abin da ya fita daga jirgin; wato, kowane mai rai na duniya.
11 J'établirai mon alliance avec vous: Toute chair ne sera plus exterminée par les eaux du déluge. Il n'y aura plus jamais de déluge pour détruire la terre. »
Na kafa alkawarina da ku, ba za a ƙara hallaka dukan rayuka da ambaliyar ruwa ba; ba za a ƙara yin ambaliya don a hallaka duniya ba.”
12 Dieu dit: « Voici le signe de l'alliance que j'établis entre moi et vous, et tous les êtres vivants qui sont avec vous, pour des générations perpétuelles:
Allah ya kuma ce, “Wannan ita ce alamar alkawarin da na yi tsakanina da ku, da kowace halitta tare da ku; alkawari na dukan zamanai masu zuwa.
13 Je place mon arc-en-ciel dans la nuée, et il sera le signe d'une alliance entre moi et la terre.
Na sa bakan gizona cikin gizagizai, shi ne kuwa zai zama alamar alkawari tsakanina da duniya.
14 Quand je ferai venir une nuée sur la terre, pour qu'on voie l'arc-en-ciel dans la nuée,
Duk sa’ad da na kawo gizagizai a bisa duniya, bakan gizo kuma ya bayyana a ciki gizagizan,
15 je me souviendrai de mon alliance, qui est entre moi et vous, et tout être vivant de toute chair, et les eaux ne deviendront plus un déluge pour détruire toute chair.
zan tuna da alkawari tsakanina da ku da kuma dukan halittu masu rai na kowane iri. Ruwa ba zai sāke yin ambaliyar da za tă hallaka dukan masu rai ba.
16 L'arc-en-ciel sera dans la nuée. Je le regarderai, afin de me souvenir de l'alliance éternelle entre Dieu et tous les êtres vivants de toute chair qui sont sur la terre. »
Duk sa’ad da bakan gizo ya bayyana cikin gizagizan, zan gan shi in kuma tuna da madawwamin alkawari tsakanin Allah da dukan halittu masu rai, na kowane iri a duniya.”
17 Dieu dit à Noé: « Voici le gage de l'alliance que j'ai établie entre moi et toute chair qui est sur la terre. »
Saboda haka Allah ya ce wa Nuhu, “Wannan ita ce alamar alkawarin da na kafa tsakanina da dukan masu rai a duniya.”
18 Les fils de Noé qui sortirent du navire furent Sem, Cham et Japhet. Cham est le père de Canaan.
’Ya’yan Nuhu maza, waɗanda suka fito daga cikin jirgi, su ne, Shem, Ham da Yafet. (Ham shi ne mahaifin Kan’ana.)
19 Ces trois-là étaient les fils de Noé, et c'est à partir d'eux que toute la terre a été peuplée.
Waɗannan su ne’ya’yan Nuhu maza uku, daga gare su ne kuma duniya za tă cika da mutane.
20 Noé se mit à cultiver la terre et planta une vigne.
Nuhu, mutumin ƙasa, shi ne farko da ya fara yin gonar inabi.
21 Il but du vin et s'enivra. Il se découvrit dans sa tente.
Sa’ad da ya sha ruwan inabin ya kuwa bugu, sai ya kwanta tsirara cikin tentinsa.
22 Cham, le père de Canaan, vit la nudité de son père, et le dit à ses deux frères au dehors.
Ham, mahaifin Kan’ana ya ga tsiraici mahaifinsa, ya kuma faɗa wa’yan’uwansa biyu a waje.
23 Sem et Japhet prirent un vêtement, le posèrent sur leurs deux épaules, entrèrent à reculons et couvrirent la nudité de leur père. Ils entrèrent à reculons et couvrirent la nudité de leur père. Ils avaient le visage tourné vers l'arrière, et ils ne virent pas la nudité de leur père.
Amma Shem da Yafet suka ɗauki mayafi, suka shimfiɗa a kafaɗarsu, sa’an nan suka shiga suna tafiya da baya har zuwa inda mahaifinsu yake kwance, suka rufe tsiraicinsa. Suka kau da fuskokinsu domin kada su ga tsiraicin mahaifinsu.
24 Noé se réveilla de son vin, et il sut ce que son plus jeune fils lui avait fait.
Sa’ad da Nuhu ya farka daga buguwarsa ya kuma gane abin da ƙarami ɗansa ya yi,
25 Il dit, « Canaan est maudite. Il sera le serviteur des serviteurs de ses frères. »
sai ya ce, “Kan’ana la’ananne ne, zai zama bawa mafi ƙanƙanta ga’yan’uwansa.”
26 Il a dit, « Béni soit Yahvé, le Dieu de Sem. Que Canaan soit son serviteur.
Ya kuma ce, “Albarka ta tabbata ga Ubangiji Allah na Shem! Bari Kan’ana yă zama bawan Shem.
27 Que Dieu agrandisse Japhet. Qu'il habite dans les tentes de Sem. Que Canaan soit son serviteur. »
Allah yă ƙara fāɗin ƙasar Yafet; bari Yafet yă zauna a tentunan Shem, bari kuma Kan’ana yă zama bawansa.”
28 Noé vécut trois cent cinquante ans après le déluge.
Bayan ambaliyar, Nuhu ya yi shekaru 350.
29 Tous les jours de Noé furent de neuf cent cinquante ans, puis il mourut.
Gaba ɗaya dai, Nuhu ya yi shekara 950, sa’an nan ya mutu.

< Genèse 9 >