< Genèse 47 >

1 Joseph entra et fit un rapport à Pharaon, en disant: « Mon père et mes frères, avec leurs brebis, leurs bœufs et tout ce qui leur appartient, sont sortis du pays de Canaan; et voici, ils sont dans le pays de Gosen. »
Yusuf ya tafi yă faɗa wa Fir’auna, “Mahaifina da’yan’uwana, tare da garkunansu da shanunsu da kome da suke da shi, sun zo daga ƙasar Kan’ana, suna kuwa a Goshen yanzu.”
2 Il prit cinq hommes parmi ses frères, et les présenta à Pharaon.
Sai ya zaɓi mutum biyar daga cikin’yan’uwansa, ya gabatar da su a gaban Fir’auna.
3 Pharaon dit à ses frères: « Quelle est votre profession? » Ils dirent à Pharaon: « Tes serviteurs sont des bergers, nous et nos pères. »
Fir’auna ya tambayi’yan’uwan, “Mece ce sana’arku?” Suka amsa wa Fir’auna suka ce, “Bayinka makiyaya ne, kamar yadda kakanninmu suke.”
4 Ils dirent aussi à Pharaon: « Nous sommes venus vivre comme des étrangers dans le pays, car il n'y a pas de pâturage pour les troupeaux de tes serviteurs. Car la famine sévit dans le pays de Canaan. Laisse donc tes serviteurs habiter dans le pays de Gosen. »
Suka kuma ce masa, “Mun zo, mu zauna a nan na ɗan lokaci, gama yunwa ta yi tsanani a Kan’ana, dabbobin bayinka kuma ba su da wurin kiwo. Saboda haka yanzu, muna roƙonka, bari bayinka su zauna a Goshen.”
5 Pharaon parla à Joseph, et dit: Ton père et tes frères sont venus vers toi.
Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Mahaifinka da’yan’uwanka sun zo maka,
6 Le pays d'Égypte est devant toi. Fais habiter ton père et tes frères dans le meilleur du pays. Qu'ils habitent dans le pays de Gosen. Si tu connais parmi eux des hommes capables, confie-leur la garde de mon bétail. »
ƙasar Masar kuma tana gabanka, ka zaunar da mahaifinka da’yan’uwanka a sashe mafi kyau na ƙasar, bari su zauna a Goshen. Idan kuma ka ga waɗansu a cikinsu da suka fi dacewa, sai ka sa su lura mini da shanuna.”
7 Joseph fit venir Jacob, son père, et le plaça devant Pharaon; et Jacob bénit Pharaon.
Sa’an nan Yusuf ya shigar da Yaƙub mahaifinsa, ya gabatar da shi a gaban Fir’auna. Bayan Yaƙub ya albarkaci Fir’auna,
8 Pharaon dit à Jacob: « Quel âge as-tu? »
sai Fir’auna ya tambaye shi, “Shekarunka nawa da haihuwa?”
9 Jacob dit à Pharaon: « Les années de mon pèlerinage sont de cent trente ans. Les jours des années de ma vie ont été peu nombreux et mauvais. Ils n'ont pas atteint les jours des années de la vie de mes pères, aux jours de leur pèlerinage. »
Yaƙub kuwa ya ce wa Fir’auna, “Shekarun hijirata, shekaru ɗari da talatin ne. Shekaruna kaɗan ne cike da wahala, ba za a kuwa daidaita su da shekarun hijirar kakannina ba.”
10 Jacob bénit Pharaon, et sortit de la présence de Pharaon.
Sai Yaƙub ya albarkaci Fir’auna, ya yi masa bankwana, sa’an nan ya fita.
11 Joseph plaça son père et ses frères, et leur donna une possession au pays d'Égypte, dans le meilleur du pays, au pays de Ramsès, comme Pharaon l'avait ordonné.
Ta haka Yusuf ya zaunar da mahaifinsa da’yan’uwansa a Masar, ya ba su mallaka a sashe mafi kyau na ƙasar, a yankin nan na Rameses, kamar yadda Fir’auna ya umarta.
12 Joseph fournit du pain à son père, à ses frères et à toute la famille de son père, selon la taille de leurs familles.
Yusuf ya kuma tanada wa mahaifinsa da kuma’yan’uwansa da dukan gidan mahaifinsa, abinci bisa ga yawan’ya’yansu.
13 Il n'y avait pas de pain dans tout le pays, car la famine était très forte, de sorte que le pays d'Égypte et le pays de Canaan s'éteignirent à cause de la famine.
A yanzu, a cikin ƙasar duka, ba abinci, gama yunwa ta yi tsanani ƙwarai, har ƙasar Masar da ƙasar Kan’ana suka shiga matsananciyar wahala!
14 Joseph rassembla tout l'argent qui se trouvait dans le pays d'Égypte et dans le pays de Canaan, pour le blé qu'on achetait, et il apporta l'argent dans la maison de Pharaon.
Yusuf ya tattara dukan kuɗaɗen da suke a Masar da Kan’ana don biyan hatsin da suke saya, ya kuwa kawo su a fadan Fir’auna.
15 Lorsque tout l'argent fut dépensé dans le pays d'Égypte et dans le pays de Canaan, tous les Égyptiens vinrent trouver Joseph et dirent: « Donne-nous du pain, car pourquoi mourrions-nous en ta présence? Car notre argent manque. »
Sa’ad da kuɗin mutanen Masar da Kan’ana suka ƙare, dukan Masar ta zo wurin Yusuf ta ce, “Ka ba mu abinci. Me zai sa mu mutu a idanunka? Kuɗinmu duk sun ƙare.”
16 Joseph dit: « Donne-moi ton bétail, et je te donnerai de la nourriture pour ton bétail, si ton argent a disparu. »
Yusuf ya ce, “To, ku kawo dabbobinku, zan sayar muku da abinci a madadin dabbobinku, tun da kuɗinku ya ƙare.”
17 Ils amenèrent leur bétail à Joseph, qui leur donna du pain en échange des chevaux, des troupeaux, des bœufs et des ânes, et il les nourrit de pain en échange de tout leur bétail pour cette année-là.
Saboda haka suka kawo dabbobinsu wa Yusuf, ya kuma ba su abinci a madadin dawakai, tumaki da awaki, shanu da jakunansu. Ya kuwa ba su abinci a madadin dabbobinsu, a wannan shekara.
18 Lorsque cette année fut terminée, ils vinrent le trouver la deuxième année et lui dirent: « Nous ne cacherons pas à mon seigneur que tout notre argent est dépensé, et que les troupeaux de bétail appartiennent à mon seigneur. Il ne reste plus aux yeux de mon seigneur que nos corps et nos terres.
Sa’ad da wannan shekara ta ƙare, sai suka zo wurinsa a shekara ta biye suka ce, “Ba za mu ɓoye maka ba ranka yă daɗe, kuɗinmu sun ƙare, dabbobinmu kuma sun zama naka. Ranka yă daɗe, in ban da jikunanmu da gonakinmu, ba abin da ya rage mana.
19 Pourquoi mourrions-nous sous tes yeux, nous et nos terres? Achète-nous du pain, nous et nos terres, et nous serons, nous et nos terres, les serviteurs de Pharaon. Donne-nous de la semence, afin que nous vivions et ne mourions pas, et que le pays ne soit pas dévasté. »
Kada ka bar mu mu mutu, ka yi wata dabara! Kada ka bari mu rasa gonakinmu. Ka musaye mu da abinci, mu da gonakinmu. Mu kuwa za mu zama bayin Fir’auna. Ka ba mu iri don mu rayu, kada mu mutu, don kuma kada gonakin ƙasarmu su zama kango.”
20 Joseph acheta tout le pays d'Égypte pour Pharaon, car chacun des Égyptiens vendit son champ, car la famine les frappait, et le pays devint la propriété de Pharaon.
Ta haka Yusuf ya saya wa Fir’auna ƙasar Masar duka, gama Masarawa duka sun sayar da gonakinsu, saboda yunwa ta tsananta musu. Ƙasar ta zama mallakar Fir’auna.
21 Quant au peuple, il le déplaça dans les villes, d'un bout à l'autre de la frontière de l'Égypte.
Yusuf kuwa ya mai da mutanen bayi, daga wannan iyakar Masar zuwa wancan.
22 Mais il n'acheta pas les terres des prêtres, car les prêtres avaient une part de Pharaon et mangeaient la part que Pharaon leur donnait. C'est pourquoi ils n'ont pas vendu leurs terres.
Amma bai sayi gonakin firistoci ba, gama suna karɓa rabo daga Fir’auna ne, suna kuma da isashen abinci daga rabon da Fir’auna yake ba su. Dalilin ke nan da ba su sayar da gonakinsu ba.
23 Joseph dit alors au peuple: « Voici que je vous ai achetés aujourd'hui, vous et vos terres, pour Pharaon. Voici de la semence pour vous, et vous ensemencerez la terre.
Yusuf ya ce wa mutane, “Yanzu da na saye ku da kuma gonakinku a yau wa Fir’auna, ga iri don ku shuka a gonaki.
24 Aux récoltes, vous donnerez un cinquième à Pharaon, et quatre parts vous appartiendront, pour la semence des champs, pour votre nourriture, pour celle de vos familles et pour celle de vos petits enfants. »
Amma sa’ad da hatsi suka nuna, za ku ba da kashi ɗaya bisa biyar ga Fir’auna. Sauran kashi huɗu bisa biyar kuma ku riƙe a matsayin iri don gonaki da kuma abinci wa kanku da gidajenku da kuma’ya’yanku.”
25 Ils dirent: « Tu nous as sauvé la vie! Que nous trouvions grâce aux yeux de mon seigneur, et nous serons les serviteurs de Pharaon. »
Suka ce, “Ka ceci rayukanmu, in ya gamshe ka, ranka yă daɗe, za mu zama bayin Fir’auna.”
26 Joseph fit une loi sur le pays d'Égypte, jusqu'à ce jour, pour que Pharaon ait le cinquième. Seule la terre des prêtres ne devint pas la propriété de Pharaon.
Ta haka Yusuf ya kafa wannan ya zama doka game da ƙasa a Masar, har yă zuwa yau cewa kashi ɗaya bisa biyar na amfani gona ya zama na Fir’auna. Gonakin firistoci ne kaɗai ba su zama na Fir’auna ba.
27 Israël habita au pays d'Égypte, dans le pays de Gosen; ils y acquirent des biens, furent féconds et multiplièrent beaucoup.
To, Isra’ilawa suka zauna a Masar a yankin Goshen. Suka mallaki filaye a can, suka riɓaɓɓanya suka ƙaru ƙwarai.
28 Jacob vécut dix-sept ans au pays d'Égypte. Les jours de Jacob, les années de sa vie, furent donc de cent quarante-sept ans.
Yaƙub ya yi zama a Masar shekaru goma sha bakwai, yawan shekarunsa duka sun zama ɗari da arba’in da bakwai.
29 Le temps où Israël devait mourir approchait. Il appela son fils Joseph et lui dit: « Si j'ai trouvé grâce à tes yeux, mets ta main sous ma cuisse et traite-moi avec bonté et sincérité. Ne m'enterre pas en Égypte,
Sa’ad da lokaci ya gabato da Isra’ila zai mutu, sai ya kira ɗansa Yusuf, ya ce masa, “Ka yi mini wannan alheri, ka sa hannunka ƙarƙashin cinyar ƙafata, ka yi mini alkawari saboda ina roƙonka kaɗa ka bizne ni a Masar,
30 mais quand je dormirai avec mes pères, tu me transporteras hors d'Égypte et tu m'enterreras dans leur sépulture. » Joseph a dit: « Je ferai ce que vous avez dit. »
amma sa’ad da na huta da kakannina, ka ɗauke ni, ka fid da ni daga Masar, ka binne ni a inda aka binne su.” Yusuf ya ce, “Zan yi yadda ka faɗa.”
31 Israël dit: « Jure-le-moi », et il le lui jura. Puis Israël se prosterna sur la tête du lit.
Yaƙub ya ce, “Ka rantse mini.” Sai Yusuf ya rantse masa, Isra’ila kuwa ya yi godiya ga Allah yayinda ya jingina a kan sandansa.

< Genèse 47 >