< Genèse 42 >

1 Jacob vit qu'il y avait du blé en Égypte, et il dit à ses fils: « Pourquoi vous regardez-vous les uns les autres? »
Sa’ad da Yaƙub ya sami labari cewa akwai hatsi a Masar, sai ya ce wa’ya’yansa maza, “Don me kuke duban juna kawai?”
2 Il répondit: « Voici, j'ai appris qu'il y a du blé en Égypte. Descendez-y et achetez-en pour nous, afin que nous vivions et que nous ne mourions pas. »
Ya ci gaba, “Na ji cewa akwai hatsi a Masar. Ku gangara can ku sayo mana, domin mu rayu kada mu mutu.”
3 Les dix frères de Joseph descendirent pour acheter du blé en Égypte.
Sai goma daga cikin’yan’uwan Yusuf suka gangara don su saya hatsi daga Masar.
4 Mais Jacob n'envoya pas Benjamin, le frère de Joseph, avec ses frères, car il dit: « De peur qu'il ne lui arrive du mal. »
Amma Yaƙub bai aiki Benyamin, ɗan’uwan Yusuf tare da sauran ba, gama yana tsoro kada wani abu yă faru da shi.
5 Les fils d'Israël vinrent acheter parmi ceux qui étaient venus, car la famine sévissait au pays de Canaan.
Sai’ya’yan Yaƙub suka isa Masar tare da sauran mutanen don sayen abinci, gama yunwar ta kai yankin Kan’ana ma.
6 Joseph était le gouverneur du pays. C'est lui qui vendit à tous les habitants du pays. Les frères de Joseph vinrent, et ils se prosternèrent devant lui, le visage contre terre.
To, Yusuf ne gwamnar ƙasar wanda yake sayar da hatsi ga dukan mutanenta. Saboda haka sa’ad da’yan’uwan Yusuf suka isa, sai suka rusuna masa har ƙasa da fuskokinsu.
7 Joseph vit ses frères et les reconnut, mais il se comporta comme un étranger avec eux et leur parla durement. Il leur dit: « D'où venez-vous? » Ils ont dit: « Du pays de Canaan, pour acheter de la nourriture. »
Nan da nan da Yusuf ya ga’yan’uwansa, sai ya gane su, amma ya yi kamar baƙo, ya kuma yi musu magana da tsawa. Ya tambaya, “Daga ina kuka fito?” Suka amsa, “Daga ƙasar Kan’ana, don mu saya abinci.”
8 Joseph reconnut ses frères, mais ils ne le reconnurent pas.
Ko da yake Yusuf ya gane’yan’uwansa, su ba su gane shi ba.
9 Joseph se souvint des rêves qu'il avait eus à leur sujet, et il leur dit: « Vous êtes des espions! Vous êtes venus voir la nudité du pays. »
Sa’an nan ya tuna da mafarkansa game da su, ya kuma ce musu, “Ku’yan leƙen asiri ne! Kun zo don ku leƙi asirin ƙasar ku ga inda ba ta da tsaro.”
10 Ils lui dirent: « Non, mon seigneur, mais tes serviteurs sont venus pour acheter de la nourriture.
Suka amsa suka ce, “A’a, ranka yă daɗe, bayinka sun zo don saya abinci ne.
11 Nous sommes tous fils d'un seul homme, nous sommes des hommes honnêtes. Tes serviteurs ne sont pas des espions. »
Mu duka’ya’yan mutum ɗaya maza ne. Bayinka mutane ne masu gaskiya, ba’yan leƙen asiri ba ne.”
12 Il leur dit: « Non, mais vous êtes venus pour voir la nudité du pays! »
Ya ce musu “Sam! Kun zo ne ku ga inda ƙasarmu babu tsaro.”
13 Ils dirent: « Nous, tes serviteurs, sommes douze frères, fils d'un seul homme au pays de Canaan; et voici que le plus jeune est aujourd'hui avec notre père, et l'autre n'est plus. »
Amma suka amsa suka ce, “Bayinka dā su goma sha biyu ne,’yan’uwa,’ya’yan mutum guda maza, wanda yake zama a ƙasar Kan’ana. Ƙaraminmu yanzu yana tare da mahaifinmu, ɗayan kuma ya rasu.”
14 Joseph leur dit: « C'est comme je vous l'ai dit, en disant: « Vous êtes des espions ».
Yusuf ya ce musu, “Daidai ne yadda na faɗa muku. Ku’yan leƙen asiri ne!
15 Par ceci, vous serez mis à l'épreuve. Par la vie de Pharaon, vous ne sortirez pas d'ici, à moins que votre plus jeune frère ne vienne ici.
Ga kuwa yadda za a gwada ku. Muddin Fir’auna yana a raye, ba za ku bar wannan wuri ba sai ƙaramin ɗan’uwanku ya zo nan.
16 Envoie l'un d'entre vous, qu'il aille chercher ton frère, et tu seras lié, afin que tes paroles soient mises à l'épreuve et qu'on sache s'il y a de la vérité en toi, ou si, par la vie de Pharaon, tu es un espion. »
Ku aiki ɗaya daga cikinku yă kawo ɗan’uwanku; za a sa sauranku a kurkuku, saboda a gwada maganarku a ga ko gaskiya ce kuke faɗi. In ba haka ba, to, da ran Fir’auna, ku’yan leƙen asiri ne!”
17 Il les mit tous ensemble en détention pendant trois jours.
Ya kuwa sa su duka a kurkuku na kwana uku.
18 Le troisième jour, Joseph leur dit: « Faites cela, et vivez, car je crains Dieu.
A rana ta uku, Yusuf ya ce musu, “Ku yi wannan za ku kuwa rayu, gama ina tsoron Allah.
19 Si vous êtes des hommes honnêtes, laissez donc l'un de vos frères être lié dans votre prison; mais vous, partez, portez du blé pour la famine de vos maisons.
In ku mutane masu gaskiya ne, ku bar ɗaya daga cikin’yan’uwanku yă zauna a kurkuku, yayinda sauranku su tafi, su kai hatsi don gidajenku da suke yunwa.
20 Amenez-moi votre plus jeune frère; ainsi vos paroles seront vérifiées, et vous ne mourrez pas. » Ils firent ainsi.
Amma dole ku kawo ƙaramin ɗan’uwanku gare ni, saboda a tabbatar da maganarku har ba za ku mutu ba.” Suka kuwa yi haka.
21 Ils se dirent les uns aux autres: « Nous sommes certainement coupables à l'égard de notre frère, en ce que nous avons vu la détresse de son âme, lorsqu'il nous suppliait, et que nous n'avons pas voulu l'écouter. C'est pourquoi cette détresse est venue sur nous. »
Sai suka ce wa juna, “Tabbatacce ana hukunta mu ne saboda ɗan’uwanmu. Mun ga yadda ya yi wahala sa’ad da ya roƙe mu saboda ransa, amma ba mu saurare shi ba, shi ya sa wannan wahala ta zo mana.”
22 Ruben leur répondit: « Ne vous ai-je pas dit: « Ne péchez pas contre l'enfant », et n'avez-vous pas voulu écouter? C'est pourquoi aussi, voici, son sang est requis. »
Ruben ya amsa, “Ban faɗa muku cewa kada ku ɗauki alhakin yaron nan ba, sai kuka ƙi ji, to, yau ga alhakin jininsa muke biya.”
23 Ils ne savaient pas que Joseph les comprenait, car il y avait un interprète entre eux.
Ba su san cewa Yusuf yana jin su ba, da yake yana amfani da mai fassara ne.
24 Il se détourna d`eux, et pleura. Puis il revint vers eux, leur parla, prit Siméon du milieu d'eux et le lia sous leurs yeux.
Sai ya juya daga gare su ya yi kuka, sa’an nan ya dawo ya yi musu magana kuma. Ya sa aka ɗauke Simeyon daga gare su, aka daure shi a idanunsu.
25 Puis Joseph donna l'ordre de remplir leurs sacs de blé, de remettre l'argent de chacun dans son sac, et de leur donner de la nourriture pour le chemin. C'est ainsi qu'il leur fut fait.
Yusuf ya yi umarni a cika buhunansu da hatsi, a kuma sa azurfan kowane mutum a cikin buhunsa, a kuma ba su kalaci don tafiyarsu. Bayan aka yi musu wannan,
26 Ils chargèrent leurs ânes de leur grain, et partirent de là.
suka jibga hatsinsu a kan jakuna, sai suka kama hanya.
27 Comme l'un d'eux ouvrait son sac pour donner à manger à son âne dans le lieu d'hébergement, il vit son argent. Voici, il était dans l'ouverture de son sac.
A wurin da suka tsaya don su kwana, ɗaya daga cikinsu ya buɗe buhunsa don yă ciyar da jakinsa, sai ya ga azurfansa a bakin buhunsa.
28 Il dit à ses frères: « Mon argent a été retrouvé! Voici qu'il est dans mon sac. » Leur cœur les abandonna, et ils se tournèrent en tremblant les uns vers les autres, en disant: « Qu'est-ce que Dieu nous a fait? »
Sai ya ce wa’yan’uwansa, “An mayar mini da azurfata. Ga shi a cikin buhuna.” Zuciyarsu ta karai, suka dubi juna suna rawan jiki, suka ce, “Mene ne wannan da Allah ya yi mana?”
29 Ils se rendirent auprès de Jacob, leur père, au pays de Canaan, et lui racontèrent tout ce qui leur était arrivé, en disant:
Sa’ad da suka zo wurin mahaifinsu Yaƙub a ƙasar Kan’ana, suka faɗa masa dukan abin da ya faru da su. Suka ce,
30 « Cet homme, le seigneur du pays, nous a parlé durement et nous a pris pour des espions du pays.
“Mutumin da yake shugaba a ƙasar ya yi mana matsananciyar magana, ya kuma ɗauke mu tamƙar’yan leƙen asirin ƙasa.
31 Nous lui avons répondu: « Nous sommes d'honnêtes hommes. Nous ne sommes point des espions.
Amma muka ce masa, ‘Mu masu gaskiya ne; mu ba’yan leƙen asiri ba ne.
32 Nous sommes douze frères, fils de notre père; l'un d'eux n'est plus, et le plus jeune est aujourd'hui avec notre père au pays de Canaan.
Dā mu’yan’uwa ne goma sha biyu,’ya’yan mahaifi guda maza. Ɗayanmu ya rasu, kuma ƙaramin yanzu yana tare da mahaifinmu a Kan’ana.’
33 L'homme, le seigneur du pays, nous dit: « Voici comment je saurai que vous êtes des hommes honnêtes: laissez-moi l'un de vos frères, prenez du blé pour la famine de vos maisons, et partez.
“Sai mutumin wanda yake shugaba a kan ƙasar ya ce mana, ‘Ga yadda zan san ko ku mutane masu gaskiya ne. Ku bar ɗaya daga cikin’yan’uwanku a nan tare da ni, ku ɗauki abinci domin gidajenku masu yunwa, ku tafi.
34 Amenez-moi votre plus jeune frère. Je saurai alors que vous n'êtes pas des espions, mais que vous êtes des hommes honnêtes. Je vous livrerai donc votre frère, et vous ferez du commerce dans le pays.'"
Amma ku kawo mini ƙaramin ɗan’uwanku domin in san cewa ku ba’yan leƙen asiri ba ne, amma mutane ne masu gaskiya. Sa’an nan zan mayar muku da ɗan’uwanku, ku kuma iya yin sana’a a ƙasar.’”
35 Comme ils vidaient leurs sacs, voici que chacun avait dans son sac son paquet d'argent. Lorsqu'ils virent leurs liasses d'argent, eux et leur père eurent peur.
Yayinda suke juyewa hatsi daga buhunansu, sai ga ƙunshin azurfan kowane mutum a buhunsa! Sa’ad da su da mahaifinsu suka ga ƙunshe-ƙunshen kuɗi, suka firgita.
36 Jacob, leur père, leur dit: « Vous m'avez privé de mes enfants! Joseph n'est plus, Siméon n'est plus, et vous voulez m'enlever Benjamin. Toutes ces choses sont contre moi. »
Yaƙub mahaifinsu, ya ce musu, “Kun sa ni rashin’ya’yana. Yusuf ya rasu, Simeyon kuma ba ya nan, yanzu kuma kuna so ku ɗauki Benyamin. Kome yana gāba da ni!”
37 Ruben parla à son père et dit: « Tue mes deux fils, si je ne te le ramène pas. Confie-le à mes soins, et je te le ramènerai. »
Sai Ruben ya ce wa mahaifinsa, “Ka kashe dukan’ya’yana maza, in ban dawo da shi gare ka ba. Ka sa shi ga kulawata, zan kuwa dawo da shi.”
38 Il dit: « Mon fils ne descendra pas avec toi, car son frère est mort et il ne reste que lui. S'il lui arrive malheur sur le chemin que vous empruntez, vous ferez descendre mes cheveux blancs avec tristesse au séjour des morts. » (Sheol h7585)
Amma Yaƙub ya ce, “Ɗana ba zai gangara zuwa can tare da ku ba, ɗan’uwansa ya rasu, shi ne kaɗai ya rage. In wani abu ya faru da shi a tafiyar da za ku yi, za ku sa furfurata ta gangara zuwa kabari cikin baƙin ciki.” (Sheol h7585)

< Genèse 42 >