< Genèse 41 >

1 Au bout de deux années complètes, Pharaon eut un songe, et voici qu'il se tenait près du fleuve.
Bayan shekaru biyu cif, Fir’auna ya yi mafarki. A mafarkin, ya ga yana tsaye kusa da Nilu,
2 Et voici, sept bêtes sortaient du fleuve. Elles étaient sveltes et grasses, et elles se nourrissaient de l'herbe des marais.
sai ga shanu bakwai masu ƙiba mulmul, suka fito daga kogin, suna kiwo a cikin kyauro.
3 Et voici, sept autres bêtes sortaient du fleuve après elles, laides et maigres, et se tenaient près des autres bêtes, sur le bord du fleuve.
Bayansu, sai ga waɗansu shanu bakwai, munana, ramammu, suka fito daga Nilu, suka tsaya kusa da waɗancan masu ƙiban, a bakin kogin.
4 Les bêtes laides et maigres dévorèrent les sept bêtes sveltes et grasses. Pharaon se réveilla.
Shanun nan da suke munana ramammu, suka cinye shanu bakwai nan masu ƙiba mulmul. Sai Fir’auna ya farka.
5 Il dormit et rêva une seconde fois; et voici que sept épis de blé montèrent sur une seule tige, sains et bons.
Ya sāke yin barci, sai ya yi mafarki na biyu; ya ga kawuna bakwai na dawa, ƙosassu masu kyau, suka yi girma a kara guda.
6 Et voici, sept épis maigres, soufflés par le vent d'est, poussèrent après eux.
Bayansu, sai ga waɗansu kawuna bakwai na dawa, suka fito sirara waɗanda iskar gabas ta sa suka yanƙwane.
7 Les épis minces avalèrent les sept épis sains et pleins. Pharaon se réveilla, et voici, c'était un rêve.
Siraran dawan suka haɗiye kawuna bakwai nan ƙosassu masu kyau. Sai Fir’auna ya farka, ashe, mafarki ne.
8 Le matin, son esprit fut troublé, et il fit venir tous les magiciens et les sages d'Égypte. Pharaon leur raconta ses rêves, mais il n'y avait personne pour les interpréter à Pharaon.
Da safe sai hankalinsa ya tashi, saboda haka sai ya aika a kawo dukan masu duba da masu hikima na Masar. Fir’auna ya faɗa musu mafarkansa, amma babu wanda ya iya ba shi fassararsu.
9 Alors le chef des échansons parla à Pharaon, et dit: « Je me souviens aujourd'hui de mes fautes.
Sai shugaban masu shayarwa ya ce wa Fir’auna, “Yau an tuna mini da kāsawata.
10 Pharaon s'est mis en colère contre ses serviteurs et m'a fait enfermer dans la maison du chef des gardes, avec le chef des boulangers.
Sai ya ci gaba ya ce, Fir’auna ya taɓa husata da bayinsa, ya kuma jefa ni da shugaban masu tuya a cikin kurkuku a gidan shugaban masu tsaro.
11 Nous fîmes un rêve en une seule nuit, lui et moi. Chacun rêva selon l'interprétation de son rêve.
Kowannenmu ya yi mafarki a wani dare, kowane mafarki kuma ya kasance da ma’anarsa.
12 Il y avait là avec nous un jeune homme, un Hébreu, serviteur du chef des gardes. Nous lui avons raconté, et il nous a interprété nos rêves. Il interpréta à chacun selon son songe.
To, wani saurayi, mutumin Ibraniyawa ya kasance a can tare da mu, bawan shugaban masu tsaro. Sai muka faɗa masa mafarkanmu, ya kuwa fassara mana su, yana ba wa kowane mutum fassarar mafarkinsa.
13 Et il en fut ainsi, comme il nous l'interpréta. Il m'a rétabli dans mes fonctions, et il l'a pendu. »
Abubuwan kuwa suka kasance daidai yadda ya fassara su gare mu; aka mai da ni a matsayina, ɗaya mutumin kuwa aka rataye shi.”
14 Alors Pharaon envoya appeler Joseph, et on le fit sortir en toute hâte du cachot. Il se rasa, changea de vêtements, et entra chez Pharaon.
Sai Fir’auna ya aika a kawo Yusuf, aka kuwa kawo shi da sauri daga kurkuku. Sa’ad da ya yi aski, ya kuma canja tufafinsa, sai ya zo gaban Fir’auna.
15 Pharaon dit à Joseph: « J'ai fait un rêve, et il n'y a personne qui puisse l'interpréter. J'ai entendu dire de toi que, lorsque tu entends un rêve, tu peux l'interpréter. »
Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Na yi mafarki, kuma babu wanda ya iya fassara shi. Amma na ji an ce sa’ad da ka ji mafarki, kana iya fassara shi.”
16 Joseph répondit à Pharaon: « Ce n'est pas en moi. Dieu donnera à Pharaon une réponse de paix. »
Yusuf ya amsa wa Fir’auna ya ce, “Ba ni ne da iyawar ba, Allah zai iya ba wa Fir’auna amsar da yake nema.”
17 Pharaon dit à Joseph: « Dans mon rêve, voici, je me tenais sur le bord du fleuve;
Sa’an nan Fir’auna ya ce wa Yusuf, “A cikin mafarkina, na ga ina tsaye a bakin Nilu,
18 et voici, sept bêtes grasses et élégantes sont sorties du fleuve. Ils se nourrissaient de l'herbe des marais.
sai ga shanu bakwai masu ƙiba mulmul, suka fito daga kogin, suna kiwo a cikin kyauro.
19 Et voici que sept autres bêtes montaient après eux, pauvres, très laides et maigres, comme je n'en ai jamais vu dans tout le pays d'Égypte pour leur laideur.
Bayansu kuma, sai ga waɗansu shanu bakwai suka fito ƙanjamammu, munana, ramammu. Ban taɓa ganin irin munanan shanu haka a cikin dukan ƙasar Masar ba.
20 Les bêtes maigres et laides mangèrent les sept premières bêtes grasses;
Ramammun shanun nan munana, suka cinye shanun nan bakwai masu ƙiba da suka fito da fari.
21 et quand elles les eurent mangées, on ne put savoir qu'elles les avaient mangées, mais elles étaient toujours aussi laides, comme au début. Alors je me réveillai.
Amma ko bayan da suka cinye su, babu wanda zai iya faɗa cewa sun yi haka; suna nan dai munana kamar yadda suke a dā. Sai na farka.
22 Je regardai en songe, et voici que sept épis de blé montaient sur une tige, pleins et bons;
“Har yanzu kuma, a cikin mafarkina na ga kawuna bakwai na dawa ƙosassu masu kyau, suna girma a kara guda.
23 et voici que sept épis de blé, desséchés, maigres, et soufflés par le vent d'orient, montaient après eux.
Bayansu, sai ga waɗansu kawuna bakwai suka fito, yanƙwananne sirara waɗanda iskar gabas ta yanƙwane.
24 Les épis maigres avalèrent les sept bons épis. Je l'ai raconté aux magiciens, mais il n'y avait personne qui pût me l'expliquer. »
Siraran kawunan dawan nan suka haɗiye kawuna bakwai nan masu kyau. Na faɗa wannan wa masu duba, amma ba wanda ya iya fassara mini shi.”
25 Joseph dit à Pharaon: « Le rêve de Pharaon est unique. Ce que Dieu va faire, il l'a annoncé à Pharaon.
Sai Yusuf ya ce wa Fir’auna, “Mafarkan Fir’auna, ɗaya ne. Allah ya bayyana wa Fir’auna abin da yake shirin yi.
26 Les sept bonnes bêtes sont sept ans, et les sept bonnes épis sont sept ans. Le rêve est unique.
Shanu masu kyau nan, shekaru bakwai ne, kawunan dawa bakwai ƙosassun nan kuwa shekaru bakwai ne; mafarkan iri ɗaya ne.
27 Les sept bêtes maigres et laides qui sont montées après elles, ce sont sept ans, et aussi les sept épis vides, soufflés par le vent d'orient; ce seront sept années de famine.
Shanun nan ramammu, munana, da suka zo daga baya, shekaru bakwai ne, haka ma kawuna dawan nan shanyayyu da iskar gabas ta yanƙwane. Shekaru ne bakwai na yunwa.
28 C'est ce que j'ai dit à Pharaon. Dieu a montré à Pharaon ce qu'il allait faire.
“Haka yake kamar yadda na faɗa wa Fir’auna cewa Allah ya nuna wa Fir’auna abin da yake shirin yi.
29 Voici, sept années de grande abondance dans tout le pays d'Égypte vont venir.
Shekaru bakwai na yalwar abinci suna zuwa a dukan ƙasar Masar,
30 Sept années de famine surviendront après elles, et toute l'abondance sera oubliée dans le pays d'Égypte. La famine consumera le pays,
amma shekaru bakwai na yunwa za su biyo bayansu. Tsananin yunwar za tă sa a manta da dukan isashen abincin da aka samu a ƙasar Masar, yunwa kuwa za tă rufe dukan ƙasar.
31 et l'abondance ne sera pas connue dans le pays, à cause de la famine qui suivra, car elle sera très douloureuse.
Ba za a tuna da isashen abincin da aka samu a ƙasar ba, domin yunwar da za tă biyo baya za tă zama da tsanani ƙwarai.
32 Le rêve a été doublé pour Pharaon, car la chose est établie par Dieu, et Dieu l'accomplira bientôt.
Dalilin da aka ba wa Fir’auna mafarkan nan kashi biyu kuwa shi ne cewa Allah ya riga ya ƙaddara al’amarin. Allah zai aikata shi, ba da daɗewa ba.
33 « Maintenant, que Pharaon cherche un homme discret et sage, et qu'il l'établisse sur le pays d'Égypte.
“Yanzu fa, bari Fir’auna yă nemi mutum mai basira da kuma hikima, yă sa shi yă shugabanci ƙasar Masar.
34 Que Pharaon fasse cela, qu'il nomme des surveillants sur le pays, et qu'ils prélèvent le cinquième de la production du pays d'Égypte pendant les sept années d'abondance.
Bari Fir’auna yă naɗa komishinoni a kan ƙasar don su karɓi kashi ɗaya bisa biyar na girbin Masar a lokacin shekaru bakwai na yalwar abinci.
35 Qu'ils rassemblent toutes les denrées de ces bonnes années à venir, et qu'ils stockent le grain sous la main de Pharaon pour le nourrir dans les villes, et qu'ils le gardent.
Ya kamata su tara dukan abincin waɗannan shekaru masu kyau da suke zuwa, su yi ajiyar hatsin a ƙarƙashin ikon Fir’auna, don a ajiye a birane don abinci.
36 Ces vivres serviront à approvisionner le pays contre les sept années de famine qui s'abattront sur le pays d'Égypte, afin que le pays ne périsse pas par la famine. »
Ya kamata a adana abincin nan don ƙasar, kāriya shekaru bakwai na yunwa, domin a yi amfani da shi a lokacin shekarun yunwan da za su zo wa Masar, saboda kada ƙasar ta lalace da yunwa.”
37 La chose était bonne aux yeux de Pharaon et aux yeux de tous ses serviteurs.
Shirin ya yi wa Fir’auna da kuma dukan hafsoshinsa kyau.
38 Pharaon dit à ses serviteurs: « Peut-on trouver un tel homme, un homme en qui réside l'Esprit de Dieu? ».
Saboda haka Fir’auna ya tambaye su, “Za mu iya samun wani kamar wannan mutum, wannan wanda Ruhun Allah yake cikinsa?”
39 Pharaon dit à Joseph: « Puisque Dieu t'a montré tout cela, il n'y a personne d'aussi discret et d'aussi sage que toi.
Sai Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Da yake Allah ya ba ka sanin dukan waɗannan, babu wani mai basira da kuma hikima kamar ka.
40 Tu seras à la tête de ma maison. Tout mon peuple sera gouverné selon ta parole. Ce n'est que sur le trône que je serai plus grand que toi. »
Za ka shugabanci fadata, kuma dukan mutanena za su zama a ƙarƙashinka. Da sarauta kaɗai zan fi ka girma.”
41 Pharaon dit à Joseph: « Voici, je t'ai établi sur tout le pays d'Égypte. »
Saboda haka Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Ga shi na sa ka zama shugaban dukan ƙasar Masar.”
42 Pharaon ôta sa bague de sa main et la mit à la main de Joseph; il le revêtit d'une robe de fin lin, et lui mit un collier d'or au cou.
Sa’an nan Fir’auna ya zare zoben sarauta daga yatsarsa, ya sa shi a yatsan Yusuf. Ya sanya masa rigar lallausan lilin, ya kuma sa masa sarƙar zinariya a wuyansa.
43 Il le fit monter dans le second char qu'il avait. Ils criaient devant lui: « Agenouillez-vous! » Il l'établit sur tout le pays d'Égypte.
Ya sa shi ya hau keken yaƙi a matsayi mai binsa na biyu, mutane kuwa suka yi shela a gabansa suna cewa, “A ba da hanya!” Ta haka ya sa shi shugaba a kan dukan ƙasar Masar.
44 Pharaon dit à Joseph: « Je suis Pharaon. Sans toi, personne ne lèvera la main ni le pied dans tout le pays d'Égypte. »
Sa’an nan Fir’auna ya ce wa Yusuf, “Ni ne Fir’auna, amma in ba tare da umarninka ba, ba wanda zai ɗaga hannu ko ƙafa a cikin dukan Masar.”
45 Pharaon donna à Joseph le nom de Zaphenath-Paneah. Il lui donna pour femme Asenath, fille du prêtre Potiphéra d'On. Joseph parcourut le pays d'Égypte.
Fir’auna ya ba wa Yusuf suna Zafenat-Faneya, ya kuma ba shi Asenat’yar Fotifera firist na On, ta zama matarsa. Yusuf kuwa ya zaga dukan ƙasar Masar.
46 Joseph était âgé de trente ans lorsqu'il se présenta devant Pharaon, roi d'Égypte. Joseph sortit de la présence de Pharaon, et parcourut tout le pays d'Égypte.
Yusuf yana zuwa shekara talatin sa’ad da ya shiga hidimar Fir’auna sarkin Masar. Yusuf kuwa ya fita daga gaban Fir’auna, ya zaga ko’ina a Masar.
47 Pendant les sept années d'abondance, la terre produisit en abondance.
A shekaru bakwai na yalwa, ƙasar ta ba da amfani mai yawa.
48 Il ramassa toutes les provisions des sept années qui s'étaient écoulées dans le pays d'Égypte, et il les mit en réserve dans les villes. Il stocka dans chaque ville des aliments provenant des champs qui entouraient cette ville.
Yusuf ya tattara dukan abincin da aka samu a waɗannan shekaru bakwai na yalwa a Masar, ya kuma yi ajiyarsu a cikin birane. A kowane birni, ya sa abincin da aka nome a kewayensa.
49 Joseph accumula du grain comme le sable de la mer, en très grande quantité, jusqu'à ce qu'il cesse de compter, car il était sans nombre.
Sai Yusuf ya tara hatsi da yawan gaske, kamar yashi a bakin teku, har sai da ya kāsa iya auna shi, gama ba a iya aunawa.
50 Il naquit à Joseph, avant l'année de la famine, deux fils qu'Asenath, fille de Potiphéra, prêtre d'On, lui enfanta.
Kafin shekarun yunwa su zo, Asenat’yar Fotifera, firist na On, ta haifa wa Yusuf’ya’ya maza biyu.
51 Joseph donna à l'aîné le nom de Manassé, car, dit-il, Dieu m'a fait oublier tout mon labeur et toute la maison de mon père. »
Yusuf ya ba wa ɗansa na fari suna Manasse ya ce, “Gama Allah ya sa na mance dukan wahalata da dukan gidan mahaifina.”
52 Le nom du second, il l'appela Ephraïm: « Car Dieu m'a rendu fécond dans le pays de mon affliction. »
Ya ba wa ɗansa na biyu suna Efraim ya ce, “Gama Allah ya wadata ni cikin wahalata.”
53 Les sept années d'abondance qui existaient dans le pays d'Égypte prirent fin.
Shekaru bakwai na yalwa a Masar suka zo ga ƙarshe,
54 Les sept années de famine commencèrent à venir, comme l'avait dit Joseph. Il y eut de la famine dans tous les pays, mais dans tout le pays d'Égypte, il y avait du pain.
sai shekaru bakwai na yunwa suka soma shigowa, kamar yadda Yusuf ya faɗa. Aka yi yunwa ko’ina amma ban da ƙasar Masar. Don akwai abinci.
55 Lorsque tout le pays d'Égypte fut affamé, le peuple cria au Pharaon pour avoir du pain. Le Pharaon dit à tous les Égyptiens: « Allez voir Joseph. Faites ce qu'il vous dira. »
Sa’ad da dukan Masar ta fara jin yunwa, sai mutane suka yi wa Fir’auna kuka don abinci. Sai Fir’auna ya ce wa dukan Masarawa, “Ku tafi wurin Yusuf, ku kuma yi abin da ya faɗa muku.”
56 La famine sévissait sur toute la surface de la terre. Joseph ouvrit tous les magasins et vendit aux Égyptiens. La famine était grande dans le pays d'Égypte.
Sa’ad da yunwa ta bazu a dukan ƙasar, sai Yusuf ya buɗe gidajen ajiya, ya kuma sayar da hatsi ga Masarawa, gama yunwa ta yi tsanani a dukan Masar.
57 Tous les pays venaient en Égypte, chez Joseph, pour acheter du blé, car la famine sévissait sur toute la surface de la terre.
Dukan ƙasashe kuwa suka zo Masar don saya hatsi daga Yusuf, gama yunwa ta yi tsanani a dukan duniya.

< Genèse 41 >