< Genèse 4 >

1 L'homme connut Eve, sa femme. Elle conçut et donna naissance à Caïn, et dit: « J'ai obtenu un homme avec l'aide de Yahvé. »
Adamu ya kwana da matarsa Hawwa’u, ta kuwa yi ciki ta haifi Kayinu. Sai ta ce, “Da taimakon Ubangiji na sami ɗa namiji.”
2 Elle donna de nouveau naissance à Abel, frère de Caïn. Abel était gardien de moutons, mais Caïn était cultivateur de la terre.
Daga baya ta haifi ɗan’uwansa, ta kuma ba shi suna Habila. Sa’ad da suka yi girma sai Habila ya zama makiyayin tumaki, Kayinu kuwa ya zama manomi.
3 Au fil du temps, Caïn apporta une offrande à Yahvé avec les fruits du sol.
Ana nan sai Kayinu ya kawo waɗansu amfanin gona a matsayin hadaya ga Ubangiji.
4 Abel apporta aussi une partie des premiers-nés de son troupeau et de sa graisse. Yahvé respecta Abel et son offrande,
Amma Habila ya kawo mafi kyau daga’ya’yan fari na garkensa. Ubangiji ya yi farin ciki da sadakar da Habila ya kawo,
5 mais il ne respecta pas Caïn et son offrande. Caïn fut très irrité, et l'expression de son visage tomba.
amma bai yi farin ciki da sadakar da Kayinu ya kawo ba. Saboda haka Kayinu ya ji fushi sosai, fuskarsa kuma ta ɓace.
6 Yahvé dit à Caïn: « Pourquoi es-tu en colère? Pourquoi l'expression de ton visage est-elle tombée?
Sai Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Don me kake fushi? Don me fuskarka ta ɓace?
7 Si tu fais bien, ne sera-t-elle pas élevée? Si tu ne fais pas le bien, le péché est accroupi à la porte. C'est toi qu'il désire, mais c'est toi qui dois le dominer. »
Da ka yi abin da yake daidai, ai, da ka sami karɓuwa. Amma tun da ba ka yi abin da ba daidai ba, zunubi zai yi fakonka don yă rinjaye ka kamar naman jeji. Yana so yă mallake ka, amma tilas ka rinjaye shi.”
8 Caïn dit à Abel, son frère: « Allons dans le champ. » Pendant qu'ils étaient dans le champ, Caïn se souleva contre Abel, son frère, et le tua.
To, Kayinu ya ce wa ɗan’uwansa Habila, “Mu tafi gona.” Yayinda suke a gona, sai Kayinu ya tasar wa Habila ya buge shi ya kashe.
9 Yahvé dit à Caïn: « Où est Abel, ton frère? » Il a dit: « Je ne sais pas. Suis-je le gardien de mon frère? »
Sai Ubangiji ya ce wa Kayinu, “Ina ɗan’uwanka Habila?” Sai Kayinu ya ce, “Ban sani ba, ni mai gadin ɗan’uwana ne?”
10 Yahvé dit: « Qu'as-tu fait? La voix du sang de ton frère crie vers moi depuis la terre.
Ubangiji ya ce, “Me ke nan ka yi? Saurara! Ga jinin ɗan’uwanka yana mini kuka daga ƙasa.
11 Maintenant, tu es maudit à cause de la terre, qui a ouvert sa bouche pour recevoir de ta main le sang de ton frère.
Yanzu, kai la’ananne ne, an kuma kore ka daga ƙasa wadda ta buɗe bakinta ta shanye jinin ɗan’uwanka daga hannunka.
12 Désormais, quand tu laboureras la terre, elle ne te cédera plus sa force. Tu seras un fugitif et un vagabond sur la terre. »
In ka nome ƙasa, ba za tă ƙara ba ka hatsinta ba. Za ka kuma zama mai yawo barkatai a duniya.”
13 Caïn dit à Yahvé: « Mon châtiment est plus grand que ce que je peux supporter.
Kayinu ya ce wa Ubangiji, “Horon nan ya sha ƙarfina.
14 Voici, tu m'as chassé aujourd'hui de la surface de la terre. Je serai caché de ta face, et je serai un fugitif et un vagabond sur la terre. Celui qui me trouvera me tuera. »
Ga shi, yau kana kori na daga ƙasar, zan zama a ɓoye daga fuskarka, zan kuma zama mai yawo barkatai, duk wanda ya same ni kuwa zai kashe ni.”
15 Yahvé lui dit: « C'est pourquoi, si quelqu'un tue Caïn, il se vengera sept fois plus. » Yahvé avait prévu un signe pour Caïn, afin que celui qui le trouverait ne le frappe pas.
Amma Ubangiji ya ce masa, “Ba haka ba ne! Duk wanda ya kashe Kayinu, za a ninƙa hukuncinsa har sau bakwai.” Sa’an nan Ubangiji ya sa wa Kayinu alama don duk wanda ya same shi kada yă kashe shi.
16 Caïn quitta la présence de Yahvé et habita dans le pays de Nod, à l'est d'Eden.
Saboda haka Kayinu ya yi tafiyarsa ya rabu da Ubangiji, ya je ya zauna ƙasar Nod a gabashin Eden.
17 Caïn connut sa femme. Elle devint enceinte et donna naissance à Hénoc. Il bâtit une ville, et donna à la ville le nom de son fils, Hénoc.
Kayinu ya kwana da matarsa, ta kuwa yi ciki, ta haifi Enok. A lokacin Kayinu yana gina birni, sai ya sa wa birnin sunan ɗansa Enok.
18 Irad naquit d'Hénoc. Irad devint le père de Mehujael. Mehujael devint le père de Methushael. Methushael engendra Lamek.
Aka haifa wa Enok Irad, Irad kuma ya haifi Mehujayel, Mehujayel kuma ya haifi Metushayel, Metushayel kuma ya haifin Lamek.
19 Lamek prit deux femmes: le nom de la première était Ada, et le nom de la seconde était Zilla.
Lamek ya auri mata biyu, ana ce da ɗaya Ada, ɗayan kuma Zilla.
20 Ada donna naissance à Jabal, qui fut le père de ceux qui habitent dans des tentes et qui ont du bétail.
Ada ta haifi Yabal, shi ne mahaifi waɗanda suke zama a tentuna, suna kuma kiwon dabbobi.
21 Le nom de son frère était Jubal, qui était le père de tous ceux qui manient la harpe et le chalumeau.
Sunan ɗan’uwansa Yubal, shi ne mahaifin dukan makaɗan garaya da masu hura sarewa.
22 Zilla donna aussi naissance à Tubal Caïn, le forgeur de tous les instruments tranchants en bronze et en fer. La sœur de Tubal Caïn était Naama.
Zilla ma ta haifi ɗa, Tubal-Kayinu, shi ne wanda ya ƙera kowane iri kayan aiki daga tagulla da kuma ƙarfe.’Yar’uwar Tubal-Kayinu ita ce Na’ama.
23 Lamek dit à ses femmes, « Adah et Zillah, entendez ma voix. Femmes de Lamech, écoutez mon discours, car j'ai tué un homme pour m'avoir blessé, un jeune homme pour m'avoir meurtri.
Wata rana, Lamek ya ce wa matansa, Ada da Zilla, “Ku saurara, matan Lamek, ku ji maganata. Na kashe wani saboda ya yi mini rauni, na kashe wani saurayi saboda ya ji mini ciwo.
24 Si Caïn sera vengé sept fois, vraiment Lamech soixante-dix-sept fois. »
Idan za a rama wa Kayinu har sau bakwai, lalle za a rama wa Lamek sau saba’in da bakwai ke nan.”
25 Adam connut de nouveau sa femme. Elle donna naissance à un fils, qu'elle appela Seth, en disant: « Dieu m'a donné un autre enfant à la place d'Abel, car Caïn l'a tué. »
Sai Adamu ya sāke kwana da matarsa, ta haifi ɗa, aka kuma ba shi suna Set, gama ta ce, “Allah ya ba ni wani yaro a madadin Habila, tun da yake Kayinu ya kashe shi.”
26 Un fils naquit aussi à Seth, et il le nomma Enosh. En ce temps-là, les hommes commencèrent à invoquer le nom de Yahvé.
Set ma ya haifi ɗa, ya kuma kira shi Enosh. A lokaci ne, mutane suka fara kira ga sunan Ubangiji.

< Genèse 4 >