< Genèse 32 >

1 Jacob poursuivit son chemin, et les anges de Dieu vinrent à sa rencontre.
Yaƙub shi ma ya kama hanyarsa, sai mala’ikun Allah suka sadu da shi.
2 Quand il les vit, Jacob dit: « C'est l'armée de Dieu. » Il donna à ce lieu le nom de Mahanaïm.
Sa’ad da Yaƙub ya gan su sai ya ce, “Wannan sansanin Allah ne!” Saboda haka ya kira wannan wuri Mahanayim.
3 Jacob envoya devant lui des messagers à Ésaü, son frère, au pays de Séir, dans le champ d'Édom.
Sai Yaƙub ya aiki manzanni su sha gabansa zuwa wurin ɗan’uwansa Isuwa a ƙasar Seyir, a ƙauyen Edom.
4 Il leur donna cet ordre: « Voici ce que vous direz à mon seigneur Ésaü: « Voici ce que dit ton serviteur Jacob. J'ai vécu comme un étranger chez Laban, et j'y suis resté jusqu'à présent.
Ya umarce su, “Ga abin da za ku faɗa wa maigidana Isuwa, ‘Bawanka Yaƙub ya ce, na yi zama tare da Laban na kuwa kasance a can sai yanzu.
5 J'ai du bétail, des ânes, des troupeaux, des serviteurs et des servantes. J'ai envoyé le dire à mon seigneur, afin que je trouve grâce à tes yeux. »
Ina da shanu da jakuna, tumaki da awaki, bayi maza da mata. Yanzu ina aika da wannan saƙo zuwa ga ranka yă daɗe, don in sami tagomashi a idanunka.’”
6 Les messagers retournèrent auprès de Jacob, en disant: « Nous sommes allés voir ton frère Ésaü. Il vient à ta rencontre, et quatre cents hommes sont avec lui. »
Sa’ad da manzannin suka komo wurin Yaƙub, suka ce, “Mun tafi wurin ɗan’uwanka Isuwa, yanzu kuwa yana zuwa ya sadu da kai, da kuma mutum ɗari huɗu tare da shi.”
7 Alors Jacob eut une grande crainte et fut bouleversé. Il divisa en deux groupes les gens qui étaient avec lui, ainsi que les troupeaux, les bœufs et les chameaux.
Da tsoro mai yawa da kuma damuwa, Yaƙub ya rarraba mutanen da suke tare da shi ƙungiyoyi biyu, haka ma garkunan tumaki da awaki, da garkunan shanu da raƙuma.
8 Il dit: « Si Ésaü vient vers la première troupe et la frappe, la troupe qui reste échappera. »
Ya yi tunani, “In Isuwa ya zo ya fāɗa wa ƙungiya ɗaya, sai ƙungiya ɗayan da ta ragu ta tsira.”
9 Jacob dit: « Dieu de mon père Abraham et Dieu de mon père Isaac, Yahvé, qui m'a dit: Retourne dans ton pays et dans ta famille, et je te ferai du bien,
Sa’an nan Yaƙub ya yi addu’a, “Ya Allah na mahaifina Ibrahim, Allah na mahaifina Ishaku. Ya Ubangiji kai da ka ce mini, ‘Koma ƙasarka zuwa wurin danginka, zan kuma sa ka yi albarka.’
10 je ne suis pas digne de la moindre de toutes les bontés et de toute la vérité que tu as montrées à ton serviteur, car c'est avec mon seul bâton que j'ai traversé ce Jourdain, et maintenant je suis devenu deux compagnies.
Ban cancanci dukan alheri da amincin da ka nuna wa bawanka ba. Da sanda kaɗai nake sa’ad da na ƙetare wannan Urdun, amma ga shi yanzu na zama ƙungiyoyi biyu.
11 Délivre-moi de la main de mon frère, de la main d'Ésaü, car je le crains, de peur qu'il ne vienne me frapper, moi et les mères avec les enfants.
Ka cece ni, ina roƙonka daga hannun ɗan’uwana Isuwa, gama ina tsoro zai zo yă fāɗa mini, yă karkashe mu duka,’ya’ya da iyaye.
12 Tu as dit: « Je te ferai du bien, et je rendrai ta postérité comme le sable de la mer, qu'on ne peut compter, tant il est nombreux. »
Amma ka riga ka faɗa, ‘Tabbatacce zan sa ka yi albarka. Zan kuma sa zuriyarka su zama kamar yashin teku da ba a iya ƙirgawa.’”
13 Il resta là cette nuit-là, et prit dans ce qu'il avait avec lui un présent pour Ésaü, son frère:
Ya kwana a can, daga cikin abin da yake tare da shi kuwa, ya zaɓi kyauta domin ɗan’uwansa Isuwa,
14 deux cents chèvres et vingt boucs, deux cents brebis et vingt béliers,
awaki ɗari biyu da bunsurai ashirin, tumaki ɗari biyu da raguna ashirin,
15 trente chameaux de lait et leurs ânes, quarante vaches, dix taureaux, vingt ânesses et dix poulains.
raƙuma mata talatin tare da ƙananansu, shanu arba’in da bijimai goma, jakuna mata ashirin da kuma jakuna maza goma.
16 Il les remit entre les mains de ses serviteurs, chaque troupeau séparément, et dit à ses serviteurs: « Passez devant moi, et mettez un espace entre chaque troupeau. »
Ya sa su a ƙarƙashin kulawar bayinsa, kowane kashin garke ya kasance a ware. Ya ce wa bayinsa, “Ku sha gabana, ku kuma ba da rata tsakanin garke da garke.”
17 Il donna cet ordre aux premiers: « Quand Ésaü, mon frère, viendra à ta rencontre et t'interrogera en disant: « De qui es-tu? Où vas-tu? A qui sont ces choses devant toi?
Ya umarci wanda yake jagorar ya ce, “Sa’ad da ɗan’uwana Isuwa ya sadu da ku ya kuma yi tambaya, ‘Ku na wane ne, ina za ku, kuma wane ne mai dukan dabbobin nan da suke gabanku?’
18 Tu répondras: « Elles sont à ton serviteur, Jacob. C'est un présent envoyé à mon seigneur Ésaü. Voici qu'il est aussi derrière nous ».
Sai ku ce, ‘Na bawanka Yaƙub ne. Kyauta ce wa maigidana Isuwa, yana kuma tafe a bayanmu.’”
19 Il donna aussi des ordres au second, au troisième et à tous ceux qui suivaient les troupeaux, en disant: « Voici comment vous parlerez à Ésaü, lorsque vous le trouverez.
Yaƙub ya kuma umarci na biyu da na uku da kuma dukan waɗansu da suka bi garkunan, “Sai ku faɗa irin abu guda ga Isuwa sa’ad da kuka sadu da shi.
20 Vous direz: « Non seulement cela, mais voici que ton serviteur Jacob est derrière nous ». Car, dit-il, « je l'apaiserai avec le présent qui me précède, et après, je verrai son visage. Peut-être m'acceptera-t-il. »
Ku kuma tabbata kun ce, ‘Bawanka Yaƙub yana tafe a bayanmu.’” Gama Yaƙub ya yi tunani cewa, “Zan kwantar da ran Isuwa da waɗannan kyautai, kafin mu sadu fuska da fuska, wataƙila yă karɓe shi.”
21 Et le présent passa devant lui, et il resta lui-même cette nuit-là dans le camp.
Saboda haka kyautai Yaƙub suka sha gabansa, amma shi kansa ya kwana a sansani.
22 Il se leva cette nuit-là, prit ses deux femmes, ses deux serviteurs et ses onze fils, et traversa le gué du Jabbok.
A wannan dare Yaƙub ya tashi ya ɗauki matansa biyu, da matan nan biyu masu hidima da’ya’yansa goma sha ɗaya ya haye rafin Yabbok.
23 Il les prit, leur fit traverser le torrent, et leur fit passer ce qui lui appartenait.
Bayan ya sa suka haye rafin, haka ma ya tura dukan mallakarsa zuwa hayen.
24 Jacob resta seul, et il lutta là avec un homme jusqu'au point du jour.
Saboda haka sai aka bar Yaƙub shi kaɗai. Sai ga wani mutum ya zo ya yi kokawa da shi har wayewar gari.
25 Comme il voyait qu'il ne l'emportait pas sur lui, l'homme toucha le creux de sa cuisse, et le creux de la cuisse de Jacob était tendu pendant qu'il luttait.
Da mutumin ya ga cewa bai fi ƙarfin Yaƙub ba, sai ya bugi kwarin ƙashin cinyar Yaƙub, sai gaɓar ƙashin cinyarsa ya goce, a sa’ad da yake kokawa da mutumin.
26 L'homme dit: « Laisse-moi partir, car le jour se lève. » Jacob a dit: « Je ne te laisserai pas partir si tu ne me bénis pas. »
Sa’an nan mutumin ya ce, “Bar ni in tafi, gama gari ya waye.” Amma Yaƙub ya amsa ya ce, “Ba zan bar ka ka tafi ba, sai ka sa mini albarka.”
27 Il lui dit: « Quel est ton nom? » Il a dit, « Jacob ».
Mutumin ya tambaye shi ya ce, “Mene ne sunanka?” Yaƙub ya amsa ya ce, “Yaƙub.”
28 Il dit: « Ton nom ne sera plus Jacob, mais Israël; car tu as combattu avec Dieu et avec les hommes, et tu as vaincu. »
Sai mutumin ya ce, “Sunanka ba zai ƙara zama Yaƙub ba, amma Isra’ila, gama ka yi kokawa da Allah da mutane, ka kuwa yi rinjaye.”
29 Jacob lui demanda: « Dis-moi ton nom, s'il te plaît. » Il a dit: « Pourquoi demandez-vous mon nom? » Alors il l'a béni là.
Yaƙub ya ce, “Ina roƙonka, faɗa mini sunanka.” Amma mutumin ya amsa ya ce, “Me ya sa kake tambayata sunana?” Sa’an nan ya albarkace shi.
30 Jacob donna à ce lieu le nom de Peniel, car il dit: « J'ai vu Dieu face à face, et ma vie est sauve. »
Saboda haka Yaƙub ya kira wurin Feniyel, yana cewa, “Domin na ga Allah fuska da fuska, duk da haka aka bar ni da rai.”
31 Le soleil se leva sur lui lorsqu'il passa à Peniel, et il boitait à cause de sa cuisse.
Rana ta yi sama a sa’ad da ya wuce Fenuwel yana kuma ɗingishi saboda ƙashin cinyarsa.
32 C'est pourquoi les enfants d'Israël ne mangent pas le tendon de la hanche, qui se trouve au creux de la cuisse, jusqu'à ce jour, car il a touché le creux de la cuisse de Jacob dans le tendon de la hanche.
Wannan ya sa har wa yau Isra’ilawa ba sa cin jijiyar ƙashin cinya wadda take a kwarin ƙashin cinya, domin an taɓa kwarin ƙashin cinyar Yaƙub kusa da jijiyar.

< Genèse 32 >