< Genèse 26 >

1 Il y eut une famine dans le pays, qui s'ajouta à la première famine qui eut lieu du temps d'Abraham. Isaac alla chez Abimélec, roi des Philistins, à Guérar.
Aka yi yunwa a ƙasar; ban da yunwar da aka yi da fari a zamanin Ibrahim, sai Ishaku ya tafi wurin Abimelek sarkin Filistiyawa a Gerar.
2 Yahvé lui apparut et lui dit: « Ne descends pas en Égypte. Habite dans le pays dont je te parlerai.
Ubangiji kuwa ya bayyana ga Ishaku ya ce, “Kada ka gangara zuwa Masar; ka yi zauna a ƙasar da zan faɗa maka.
3 Habite dans ce pays, et je serai avec toi, et je te bénirai. Car je te donnerai, à toi et à ta postérité, tous ces pays, et j'accomplirai le serment que j'ai fait à Abraham, ton père.
Ka zauna a wannan ƙasa na ɗan lokaci, zan kuwa kasance tare da kai, zan kuma albarkace ka. Gama zan ba da waɗannan ƙasashe gare ka da kuma zuriyarka. Zan kuma cika rantsuwar da na yi wa mahaifinka Ibrahim.
4 Je multiplierai ta descendance comme les étoiles du ciel, et je donnerai tous ces pays à ta descendance. En ta descendance seront bénies toutes les nations de la terre,
Zan sa zuriyarka ta yi yawa kamar taurari a sararin sama zan kuwa ba su dukan waɗannan ƙasashe, ta wurin’ya’yanka kuma za a albarkaci dukan al’umman duniya,
5 parce qu'Abraham a obéi à ma voix, et qu'il a gardé mes exigences, mes commandements, mes statuts et mes lois. »
domin Ibrahim ya yi mini biyayya ya kuma kiyaye umarnaina, ƙa’idodina da kuma dokokina.”
6 Isaac habitait à Guérar.
Sai Ishaku ya zauna a Gerar.
7 Les gens du lieu l'interrogèrent sur sa femme. Il répondit: « C'est ma sœur », car il avait peur de dire: « Ma femme », de peur, pensait-il, que les gens du lieu ne me tuent pour Rebecca, car elle est belle à regarder. »
Sa’ad da mutanen wurin suka tambaye shi game da matarsa, sai ya ce, “’Yar’uwata ce,” gama yana tsoro yă ce, “Ita matata ce.” Ya yi tunani, “Mutane wannan wuri za su kashe ni ta dalili Rebeka, domin kyakkyawa ce.”
8 Comme il était là depuis longtemps, Abimélec, roi des Philistins, regarda par une fenêtre et vit, et voici, Isaac caressait Rebecca, sa femme.
Sa’ad da Ishaku ya daɗe a can, sai Abimelek sarkin Filistiyawa ya duba daga taga ya ga Ishaku yana rungumar matarsa Rebeka.
9 Abimélec appela Isaac et dit: « Voici, elle est bien ta femme. Pourquoi as-tu dit: « C'est ma sœur »? » Isaac lui dit: « Parce que j'ai dit: « De peur que je ne meure à cause d'elle ».
Saboda haka Abimelek ya aika Ishaku yă je, sa’an nan ya ce, “Tabbatacce ita matarka ce! Me ya sa ka ce, ‘Ita’yar’uwata ce?’” Ishaku ya amsa masa ya ce, “Don na yi tsammani zan rasa raina saboda ita.”
10 Abimélec dit: « Qu'est-ce que tu nous as fait? L'un des gens du peuple aurait pu facilement coucher avec ta femme, et tu nous aurais rendus coupables! ».
Sa’an nan Abimelek ya ce, “Me ke nan ka yi mana? Da a ce wani daga mazanmu ya kwana da matarka, ai, da ka jawo laifi a kanmu.”
11 Abimélec donna un ordre à tout le peuple, en disant: « Celui qui touchera cet homme ou sa femme sera certainement mis à mort. »
Saboda haka Abimelek ya yi umarni ga dukan mutane. “Duk wanda ya fitine wannan mutum ko matarsa, tabbatacce za a kashe shi.”
12 Isaac sema dans ce pays, et il récolta la même année cent fois ce qu'il avait planté. L'Éternel le bénit.
Ishaku ya shuka hatsi a wannan ƙasa, a shekaran nan ya yi girbi ninki ɗari, domin Ubangiji ya albarkace shi.
13 L'homme devint grand, et il grandit de plus en plus jusqu'à devenir très grand.
Mutumin ya arzuta, arzikinsa ya yi ta haɓaka har ya zama attajiri.
14 Il possédait des troupeaux, des troupeaux de bétail et une grande maison. Les Philistins l'enviaient.
Ya kasance da garkunan tumaki da na shanu da bayi masu yawa, har Filistiyawa suka yi ƙyashinsa.
15 Or, tous les puits que les serviteurs de son père avaient creusés du temps d'Abraham, son père, les Philistins les avaient bouchés et remplis de terre.
Saboda haka dukan rijiyoyin da bayin mahaifinsa suka haƙa a kwanakin da mahaifinsa Ibrahim yake da rai, Filistiyawa sun toshe su, suka kuma ciccike su da ƙasa.
16 Abimélec dit à Isaac: « Va-t'en loin de nous, car tu es beaucoup plus puissant que nous. »
Sai Abimelek ya ce wa Ishaku, “Fita daga cikinmu; ka fi ƙarfinmu.”
17 Isaac partit de là, campa dans la vallée de Gerar et y demeura.
Saboda haka Ishaku ya fita daga can, ya yi sansani a Kwarin Gerar, ya kuma zauna a can.
18 Isaac creusa de nouveau les puits d'eau qu'on avait creusés du temps d'Abraham, son père, car les Philistins les avaient arrêtés après la mort d'Abraham. Il leur donna des noms semblables à ceux par lesquels son père les avait appelés.
Ishaku ya sāke tona rijiyoyi waɗanda dā aka haƙa a zamanin Ibrahim mahaifinsa, gama Filistiyawa suka tattoshe bayan mutuwar Ibrahim, ya kuma sa musu sunayen da mahaifinsa ya ba su.
19 Les serviteurs d'Isaac creusèrent dans la vallée et y trouvèrent un puits d'eau vive.
Barorin Ishaku suka haƙa cikin kwarin suka kuwa sami rijiya mai ruwa mai kyau a can.
20 Les bergers de Gerar discutèrent avec les bergers d'Isaac, en disant: « L'eau est à nous. » Isaac donna donc au puits le nom d'Esek, parce qu'ils se disputaient avec lui.
Amma makiyayan Gerar suka yi faɗa da na Ishaku suka ce, “Ruwan namu ne!” Saboda haka Ishaku ya ba wa rijiyar suna Esek, domin sun yi faɗa da shi.
21 Ils creusèrent un autre puits, et ils se disputèrent aussi à son sujet. Il l'appela donc Sitna.
Sai suka haƙa wata rijiya, amma suka yi faɗa a kanta ita ma, saboda haka ya ce da ita Sitna.
22 Il quitta ce lieu, et creusa un autre puits. Ils ne se disputèrent pas pour celui-là. Il l'appela donc Rehoboth. Il dit: « Car maintenant Yahvé nous a fait une place, et nous serons féconds dans le pays. »
Sai Ishaku ya matsa daga can ya sāke haƙa wata rijiyar, babu wani kuma da yi faɗa a kanta. Sai ya ba ta suna Rehobot, yana cewa, “Yanzu Ubangiji ya ba mu wuri, za mu kuwa yi ta haihuwa a ƙasar.”
23 De là, il monta à Beer Schéba.
Daga can ya haura zuwa Beyersheba.
24 Yahvé lui apparut la même nuit, et dit: « Je suis le Dieu d'Abraham, ton père. Ne crains pas, car je suis avec toi, je te bénirai et je multiplierai ta descendance à cause de mon serviteur Abraham. »
A wannan dare Ubangiji ya bayyana gare shi ya ce, “Ni ne Allah na mahaifinka Ibrahim. Kada ka ji tsoro, gama ina tare da kai, zan albarkace ka, zan kuma ƙara yawan zuriyarka saboda bawana Ibrahim.”
25 Il y bâtit un autel, invoqua le nom de Yahvé et y dressa sa tente. Les serviteurs d'Isaac y creusèrent un puits.
Sai Ishaku ya gina bagade a can, ya kuma kira bisa sunan Ubangiji. A can ya kafa tentinsa, a can kuma bayinsa suka haƙa wata rijiya.
26 Alors Abimélec vint à lui de Guérar, avec Ahuzzath, son ami, et Phicol, le chef de son armée.
Ana cikin haka, sai Abimelek ya zo wurinsa daga Gerar, tare da Ahuzzat mai ba shi shawara da Fikol shugaban mayaƙansa.
27 Isaac leur dit: « Pourquoi êtes-vous venus vers moi, puisque vous me haïssez et que vous m'avez chassé de chez vous? ».
Ishaku ya tambaye su, “Me ya kawo ku gare ni, da yake kun yi gāba da ni, kuka kuma kore ni?”
28 Ils dirent: « Nous avons vu clairement que Yahvé était avec toi. Nous avons dit: « Qu'il y ait maintenant un serment entre nous, même entre nous et toi, et faisons alliance avec toi,
Suka amsa, “Mun ga a zahiri cewa Ubangiji yana tare da kai; saboda haka muka ce, ‘Dole rantsuwa ta kasance tsakaninmu da kai.’ Bari mu yi yarjejjeniya da kai
29 que tu ne nous fasses aucun mal, comme nous ne t'avons pas touché, et comme nous ne t'avons fait que du bien, et que nous t'avons renvoyé en paix. Vous êtes maintenant les bénis de Yahvé. »
cewa ba za ka cuce mu ba, kamar yadda ba mu fitine ka ba, amma muka yi maka kirki, muka kuma sallame ka cikin salama. Yanzu kuwa kai albarkatacce ne na Ubangiji.”
30 Il leur fit un festin, et ils mangèrent et burent.
Sai Ishaku ya shirya musu liyafa, suka ci suka kuma sha.
31 Ils se levèrent un peu plus tard dans la matinée et se jurèrent l'un à l'autre. Isaac les renvoya, et ils s'éloignèrent de lui en paix.
Kashegari da sassafe sai mutanen suka yi wa juna rantsuwa. Sa’an nan Ishaku ya sallame su, suka kuwa tafi cikin salama.
32 Le même jour, les serviteurs d'Isaac vinrent lui parler du puits qu'ils avaient creusé, et lui dirent: « Nous avons trouvé de l'eau. »
A wannan rana bayin Ishaku suka zo suka faɗa masa game da rijiyar da suka haƙa. Suka ce, “Mun sami ruwa!”
33 Il l'appela « Shibah ». C'est pourquoi le nom de la ville est encore aujourd'hui « Beersheba ».
Sai ya kira ta Shiba, don haka har wa yau ana kira garin Beyersheba.
34 Lorsque Ésaü eut quarante ans, il prit pour femme Judith, fille de Beeri, le Hittite, et Basemath, fille d'Élon, le Hittite.
Sa’ad da Yaƙub ya kai shekaru arba’in da haihuwa, sai ya auri Yudit’yar Beyeri mutumin Hitti, da kuma Basemat’yar Elon mutumin Hitti.
35 Elles affligèrent l'esprit d'Isaac et de Rebecca.
Su ne suka zama sanadin baƙin ciki ga Ishaku da Rebeka.

< Genèse 26 >