< Genèse 24 >

1 Abraham était vieux, d'un âge avancé. Yahvé avait béni Abraham en toutes choses.
Yanzu fa Ibrahim ya tsufa, yana da shekaru masu yawa, Ubangiji kuma ya albarkace shi a kowace hanya.
2 Abraham dit à son serviteur, l'aîné de sa maison, qui régnait sur tout ce qu'il possédait: « Mets, je te prie, ta main sous ma cuisse.
Sai Ibrahim ya ce wa babban bawan gidansa, wanda yake lura da duk abin da yake da shi, “Sa hannunka a ƙarƙashin cinyata.
3 Je te ferai jurer par Yahvé, le Dieu du ciel et le Dieu de la terre, que tu ne prendras pas pour mon fils une femme parmi les filles des Cananéens au milieu desquels j'habite.
Ina so ka rantse da sunan Ubangiji Allah na sama da ƙasa, cewa ba za ka samo wa ɗana mata daga’yan matan Kan’aniyawa, waɗanda nake zama cikinsu ba.
4 Mais tu iras dans mon pays et dans ma famille, et tu prendras une femme pour mon fils Isaac. »
Amma za ka tafi ƙasata da kuma cikin’yan’uwana, ka samo mata saboda ɗana Ishaku.”
5 Le serviteur lui dit: « Et si la femme ne veut pas me suivre dans ce pays? Dois-je ramener ton fils dans le pays d'où tu viens? »
Bawan ya ce masa, “Me zai faru in matar ba tă yarda tă zo tare da ni zuwa wannan ƙasa ba? In komar da ɗanka a ƙasar da ka fito ne ke nan?”
6 Abraham lui dit: « Prends garde de ne plus y amener mon fils.
Ibrahim ya ce, “Ka tabbata ba ka komar da ɗana can ba.”
7 Yahvé, le Dieu des cieux, qui m'a enlevé de la maison de mon père et du pays où je suis né, qui m'a parlé et qui m'a juré: « Je donnerai ce pays à ta postérité », enverra son ange devant toi, et tu prendras de là une femme pour mon fils.
Ubangiji Allah na sama, wanda ya fitar da ni daga gidan mahaifina, da kuma ƙasar asalina wanda kuma ya yi magana da ni, ya yi mini alkawari da rantsuwa cewa, “Ga zuriyarka zan ba da wannan ƙasa, zai aika mala’ikansa yă sha gabanka domin ka samo wa ɗana mata daga can.
8 Si la femme ne veut pas te suivre, alors tu seras dégagé de ce serment envers moi. Seulement, tu n'y amèneras plus mon fils. »
In matar ba tă yarda tă zo tare da kai ba, za a kuɓutar da kai daga wannan rantsuwa. Sai dai kada ka kai ɗana a can.”
9 Le serviteur mit sa main sous la cuisse d'Abraham, son maître, et lui jura sur cette affaire.
Saboda haka bawan ya sa hannunsa a ƙarƙashin cinyar maigidansa Ibrahim, ya kuma rantse masa game da wannan al’amari.
10 Le serviteur prit dix chameaux de son maître, et s'en alla, ayant avec lui une foule de biens appartenant à son maître. Il se leva, et se rendit en Mésopotamie, dans la ville de Nachor.
Sai bawan ya ɗibi raƙuma goma na maigidansa ya tafi, ɗauke da kowane irin abubuwa masu kyau daga wurin maigidansa. Ya fita don yă tafi Aram-Naharayim, ya kama hanyarsa zuwa garin Nahor.
11 Il fit agenouiller les chameaux hors de la ville, près du puits d'eau, à l'heure du soir, heure à laquelle les femmes sortent pour puiser de l'eau.
Ya sa raƙuman suka durƙusa kusa da rijiya a bayan gari; wajen yamma ne, lokacin da mata sukan fita ɗiban ruwa.
12 Il dit: « Yahvé, le Dieu de mon maître Abraham, donne-moi aujourd'hui du succès et fais preuve de bonté envers mon maître Abraham.
Sai ya yi addu’a ya ce, “Ya Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim, ka ba ni nasara yau, ka kuma nuna alheri ga maigidana Ibrahim.
13 Voici que je me tiens près de la source d'eau. Les filles des hommes de la ville sortent pour puiser de l'eau.
Duba, ina tsaye a bakin rijiyar ruwa,’ya’ya matan mutanen gari kuma suna fitowa domin ɗiban ruwa.
14 Que la jeune fille à qui je dirai: « Abaisse ta cruche pour que je boive », puis qui dira: « Bois et je donnerai à boire à tes chameaux », soit celle que tu as désignée pour ton serviteur Isaac. Je saurai ainsi que tu as fait preuve de bonté envers mon maître. »
Bari yă zama sa’ad da na ce wa wata yarinya, ‘Ina roƙonki ki saukar da tulunki domin in sha,’ in ta ce, ‘Ka sha, zan kuma ba wa raƙumanka ma’; bari tă zama ita ce ka zaɓa wa bawanka Ishaku. Ta haka zan san cewa ka nuna wa maigidana alheri.”
15 Avant qu'il ait fini de parler, voici que sortait Rébecca, née de Bethuel, fils de Milca, femme de Nachor, frère d'Abraham, avec sa cruche sur l'épaule.
Kafin ya gama addu’a, sai Rebeka ta fito da tulu a kafaɗarta. Ita’yar Betuwel ɗan Milka, matar Nahor, ɗan’uwan Ibrahim.
16 La jeune femme était très belle à voir, elle était vierge. Aucun homme ne l'avait connue. Elle descendit à la source, remplit sa cruche et remonta.
Yarinyar kuwa kyakkyawa ce, budurwa, ba namijin da ya taɓa kwana da ita. Ta gangara zuwa rijiyar, ta cika tulunta ta kuma hauro.
17 La servante courut à sa rencontre et dit: « Je t'en prie, donne-moi à boire, un peu d'eau de ta cruche. »
Bawan ya yi sauri ya same ta ya ce, “Ina roƙonki ki ba ni ɗan ruwa daga tulunki.”
18 Elle dit: « Bois, mon seigneur. » Elle se hâta, laissa tomber sa cruche sur sa main et lui donna à boire.
Ta ce, “Ka sha, ranka yă daɗe,” ta yi sauri ta saukar da tulun a hannuwanta, ta kuma ba shi, ya sha.
19 Lorsqu'elle eut fini de lui donner à boire, elle dit: « Je vais aussi puiser pour tes chameaux, jusqu'à ce qu'ils aient fini de boire. »
Bayan ta ba shi ya sha, sai ta ce, “Zan ɗebo wa raƙumanka ruwa su ma, har sai sun gama sha.”
20 Elle se dépêcha de vider sa cruche dans l'auge, courut de nouveau au puits pour puiser, et puisa pour tous ses chameaux.
Sai ta yi sauri ta juye ruwan da yake tulunta cikin kwami, ta koma zuwa rijiyar da gudu don ta ƙara ɗebo ruwa, ta kuma ɗebo isashe saboda dukan raƙumansa.
21 L'homme la regardait fixement, en gardant le silence, pour savoir si l'Éternel avait fait prospérer son voyage ou non.
Mutumin bai ce uffam ba, ya dai kalle ta sosai don yă san ko Ubangiji ya ba shi nasara a tafiyarsa ko babu.
22 Comme les chameaux avaient fini de boire, l'homme prit un anneau d'or du poids d'un demi-sékel et deux bracelets pour ses mains du poids de dix sicles d'or,
Sa’ad da raƙuman suka gama shan ruwa, mutumin ya fitar da zoben hanci na zinariya mai nauyin giram biyar da woroworo biyu na zinariya masu nauyin shekel goma, ya ba ta.
23 et dit: « De qui es-tu la fille? Dis-moi, je t'en prie. Y a-t-il de la place dans la maison de ton père pour nous loger? »
Sa’an nan ya tambaye ta ya ce, “Ke’yar wace ce? Ina roƙonki ki faɗa mini, akwai wuri a gidan mahaifinki da za mu kwana?”
24 Elle lui répondit: « Je suis la fille de Bethuel, fils de Milca, qu'elle a enfanté à Nachor. »
Sai ta ce masa, “Ni’yar Betuwel ce ɗan da Milka ta haifa wa Nahor.”
25 Elle lui dit encore: « Nous avons de la paille et du fourrage en quantité suffisante, et de quoi nous loger. »
Ta ƙara da cewa, “Muna da isashen ciyawa da abincin dabbobi, da kuma wuri domin ku kwana.”
26 L'homme baissa la tête et se prosterna devant Yahvé.
Sa’an nan mutumin ya rusuna ya yi wa Ubangiji sujada,
27 Il dit: « Béni soit Yahvé, le Dieu de mon maître Abraham, qui n'a pas renoncé à sa bonté et à sa fidélité envers mon maître. Quant à moi, Yahvé m'a conduit sur le chemin de la maison des parents de mon maître. »
yana cewa, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim, wanda bai daina nuna alheri da amincinsa ga maigidana ba. Ni kam, Ubangiji ya bishe ni a tafiyata zuwa gidan’yan’uwan maigidana.”
28 La jeune femme courut, et rapporta ces paroles à la maison de sa mère.
Yariyan ta gudu ta faɗa wa mutanen gidan mahaifiyarta game da abubuwan nan.
29 Rébecca avait un frère, qui s'appelait Laban. Laban courut vers l'homme, vers la source.
Rebeka fa tana da wani ɗan’uwa mai suna Laban, sai ya yi hanzari ya fita zuwa wurin mutumin a rijiyar.
30 Lorsqu'il vit l'anneau et les bracelets aux mains de sa sœur, et qu'il entendit les paroles de Rebecca, sa sœur, disant: « C'est ce que l'homme m'a dit », il vint vers l'homme. Voici, il se tenait près des chameaux, à la source.
Nan da nan da ya ga zoben hancin da woroworo a hannuwan’yar’uwansa, ya kuma ji Rebeka ta faɗa abin da mutumin ya ce mata, sai ya fita zuwa wurin mutumin, ya same shi yana tsaye wajen raƙuma kusa da rijiyar.
31 Il dit: « Entre, béni de Yahvé. Pourquoi te tiens-tu dehors? Car j'ai préparé la maison, et de la place pour les chameaux. »
Sai ya ce, “Zo, ya kai mai albarka na Ubangiji, don me kake tsaye a waje? Gama na shirya gida da wuri domin raƙuma.”
32 L'homme entra dans la maison, et il déchargea les chameaux. Il donna de la paille et de la nourriture pour les chameaux, et de l'eau pour laver ses pieds et ceux des hommes qui étaient avec lui.
Don haka mutumin ya tafi gidan, aka kuma saukar da kaya kan raƙuman. Aka kawo wa raƙuman ciyawa da abincin dabbobi, aka kuma kawo ruwa dominsa da mutanensa su wanke ƙafafunsu.
33 On lui mit à manger devant lui, mais il dit: « Je ne mangerai pas avant d'avoir dit mon message. » Laban a dit: « Parle. »
Sa’an nan aka ajiye abinci a gabansa, amma ya ce, “Ba zan ci ba, sai na faɗi abin da yake tafe da ni.” Sai Laban ya ce, “Faɗa mana.”
34 Il répondit: « Je suis le serviteur d'Abraham.
Saboda haka ya ce, “Ni bawan Ibrahim ne.
35 Yahvé a fait de mon maître une grande bénédiction. Il est devenu grand. Yahvé lui a donné des troupeaux, de l'argent et de l'or, des serviteurs et des servantes, des chameaux et des ânes.
Ubangiji ya albarkaci maigidana sosai, ya kuma zama mai arziki. Ya ba shi tumaki, shanu, azurfa, zinariya, bayi maza da mata, raƙuma, da kuma jakuna.
36 Sara, la femme de mon maître, a enfanté un fils à mon maître quand elle était vieille. Il lui a donné tout ce qu'il possède.
Saratu matar maigidana ta haifa masa ɗa a tsufanta, ya kuma ba shi duk mallakarsa.
37 Mon maître m'a fait jurer en disant: « Tu ne prendras pas pour mon fils une femme parmi les filles des Cananéens, dans le pays desquels j'habite,
Maigidana ya sa na yi rantsuwa, ya kuma ce, ‘Kada ka ɗauko wa ɗana mata daga’ya’ya matan Kan’aniyawa, waɗanda nake zama a ƙasarsu,
38 mais tu iras dans la maison de mon père et dans ma parenté, et tu prendras une femme pour mon fils ».
amma ka tafi wajen gidan mahaifina da kuma dangina, ka ɗauko wa ɗana mata.’
39 J'ai demandé à mon maître: « Et si la femme ne veut pas me suivre? »
“Sai na ce wa maigidana, ‘A ce matar ba tă yarda tă zo tare da ni ba fa?’
40 Il m'a répondu: « L'Éternel, devant qui je marche, enverra son ange avec toi et fera prospérer ton chemin. Tu prendras pour mon fils une femme de ma famille et de la maison de mon père.
“Maigidana ya ce, ‘Ubangiji wanda yake tare da ni zai aiki mala’ikansa tare da kai, yă kuma sa tafiyarka tă yi nasara, don ka samo wa ɗana mata daga dangina, daga kuma gidan mahaifina.
41 Tu seras ainsi libéré de mon serment, quand tu iras chez mes parents. S'ils ne te la donnent pas, tu seras libéré de mon serment.
Ta haka za ka kuɓuta daga rantsuwata sa’ad da ka tafi wurin dangina, ko ma sun ƙi su ba ka ita, za ka kuɓuta daga rantsuwata.’
42 Je suis venu aujourd'hui à la source et j'ai dit: « Yahvé, Dieu de mon maître Abraham, si maintenant tu fais prospérer le chemin que j'emprunte,
“Sa’ad da na zo rijiya a yau, na ce, ‘Ya Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim, ina roƙonka ka ba ni nasara a tafiyar da na yi.
43 voici que je me tiens près de cette source d'eau. Que la jeune fille qui vient puiser, à qui je dirai: « Donne-moi un peu d'eau de ta cruche pour boire »,
Duba, ina tsaye kusa da wannan rijiya; in wata yarinya ta fito domin tă ɗiba ruwa, wadda in na ce mata, “Ina roƙonki bari in ɗan sha ruwa daga tulunki,”
44 et qui me dira: « Bois, et je puiserai aussi pour tes chameaux », soit la femme que Yahvé a désignée pour le fils de mon maître.
in ta ce, “Ka sha, zan kuma ba wa raƙumanka ma,” bari tă zama wadda Ubangiji ya zaɓar wa ɗan maigidana.’
45 Avant que j'aie fini de parler en mon cœur, voici que Rebecca sortit, sa cruche sur l'épaule. Elle est descendue à la source et a puisé. Je lui ai dit: « Laisse-moi boire, je te prie ».
“Kafin in gama addu’ar, a zuciyata, sai ga Rebeka ta fito da tulunta a kafaɗarta. Ta gangara zuwa rijiyar ta ɗebo ruwa, na kuma ce mata, ‘Ina roƙonki ki ba ni ɗan ruwa daga tulunki.’
46 Elle s'empressa de laisser tomber sa cruche de son épaule et dit: « Bois, et je donnerai aussi à boire à tes chameaux. Je bus donc, et elle donna aussi à boire aux chameaux.
“Ta yi sauri ta saukar da tulun daga kafaɗarta ta ce, ‘Sha, zan kuma ba wa raƙumanka su ma.’ Sai na sha, ta kuma shayar da raƙumana su ma.
47 Je l'ai interrogée, et j'ai dit: « De qui es-tu la fille? Elle répondit: « Fille de Bethuel, fils de Nachor, que Milca lui a enfantée ». Je mis l'anneau à son nez, et les bracelets à ses mains.
“Na tambaye ta, ‘Ke’yar wane ne?’ “Ta ce, ‘’Yar Betuwel ɗan Nahor, wanda Milka ta haifa masa.’ “Sai na sa mata zobe a hancinta, woroworo kuma a hannuwata,
48 Je me suis incliné, j'ai adoré Yahvé et j'ai béni Yahvé, le Dieu de mon maître Abraham, qui m'a conduit dans la bonne voie pour prendre la fille du frère de mon maître pour son fils.
na kuma sunkuya na yi wa Ubangiji sujada. Na yabi Ubangiji Allah na maigidana Ibrahim wanda ya bi da ni a hanyar da take daidai, don in samo wa ɗan maigidana jikanyar ɗan’uwansa.
49 Maintenant, si tu veux traiter mon maître avec bonté et sincérité, dis-le moi. Sinon, dis-le moi, afin que je me tourne à droite ou à gauche. »
Yanzu fa in za ku nuna wa maigidana alheri da aminci, ku faɗa mini, in kuma ba haka ba, ku faɗa mini, don in san hanyar da zan juya.”
50 Laban et Béthuel répondirent: « La chose procède de Yahvé. Nous ne pouvons pas te parler en mal ou en bien.
Laban da Betuwel suka ce, “Wannan daga wurin Ubangiji ne, ba abin da za mu ce I, ko a’a ba.
51 Voici, Rebecca est devant vous. Prends-la, va, et qu'elle soit la femme du fils de ton maître, comme l'a dit Yahvé. »
Ga Rebeka, ɗauke ta ku tafi, bari tă zama matar ɗan maigidanka, yadda Ubangiji ya umarta.”
52 Lorsque le serviteur d'Abraham entendit leurs paroles, il se prosterna en terre devant Yahvé.
Sa’ad da bawan Ibrahim ya ji abin da suka ce, sai ya rusuna har ƙasa a gaban Ubangiji.
53 Le serviteur sortit des bijoux d'argent, des bijoux d'or et des vêtements, et il les donna à Rebecca. Il donna aussi des objets précieux à son frère et à sa mère.
Sa’an nan bawan ya fito da kayan ado na zinariya da azurfa da kayayyaki na tufafi ya ba wa Rebeka; ya kuma ba wa ɗan’uwanta da mahaifiyarta kyautai masu tsada.
54 Ils mangèrent et burent, lui et les hommes qui étaient avec lui, et passèrent la nuit. Ils se levèrent le matin, et il dit: « Envoie-moi chez mon maître. »
Sa’an nan shi da mutanen da suke tare da shi suka ci, suka sha, suka kuma kwana a can. Kashegari da safe da suka tashi sai ya ce, “A sallame ni in koma wurin maigidana.”
55 Son frère et sa mère ont dit: « Que la jeune fille reste avec nous quelques jours, au moins dix. Après cela, elle partira. »
Amma ɗan’uwanta da mahaifiyarta suka ce, “Bari yarinyar ta ɗan zauna tare da mu kwana goma ko fiye, sa’an nan ka ta fi.”
56 Il leur dit: « Ne me faites pas obstacle, puisque l'Éternel a favorisé mon chemin. Faites-moi partir pour que j'aille vers mon maître. »
Amma ya ce musu, “Kada ku tsai da ni, tun da Ubangiji ya ba ni nasara a tafiyata. Ku sallame ni domin in tafi wurin maigidana.”
57 Ils dirent: « Nous appellerons la jeune fille, et nous lui demanderons. »
Sa’an nan suka ce, “Bari mu kira yarinyar mu tambaye ta game da zancen.”
58 Ils appelèrent Rebecca, et lui dirent: « Veux-tu aller avec cet homme? » Elle a dit: « Je vais y aller. »
Saboda haka suka kira Rebeka suka ce mata, “Za ki tafi tare da mutumin nan?” Sai ta ce, “Zan tafi.”
59 Ils envoyèrent Rebecca, leur sœur, avec sa nourrice, le serviteur d'Abraham et ses hommes.
Saboda haka suka sallame Rebeka,’yar’uwarsu, duk da uwar goyonta da bawan Ibrahim da mutanensa.
60 Ils bénirent Rebecca et lui dirent: « Notre sœur, que tu sois la mère de milliers de dix mille, et que ta descendance possède la porte de ceux qui les haïssent. »
Suka kuma albarkaci Rebeka suka ce mata, “’Yar’uwarmu, bari ki zama mahaifiyar dubu dubbai, bari zuriyarki su mallaki ƙofofin abokan gābansu.”
61 Rebekah se leva avec ses dames. Elles montèrent sur les chameaux, et suivirent l'homme. Le serviteur prit Rebecca, et s'en alla.
Sa’an nan Rebeka da bayinta mata suka shirya suka hau raƙumansu suka koma tare da mutumin. Da haka bawan ya ɗauki Rebeka ya tafi.
62 Isaac vint du chemin de Beer Lahai Roi, car il habitait dans le pays du Sud.
Ishaku kuwa ya zo daga Beyer-Lahai-Royi, gama yana zama a Negeb.
63 Le soir, Isaac sortit pour méditer dans les champs. Il leva les yeux et regarda. Et voici, des chameaux arrivaient.
Wata rana da yamma ya fita zuwa fili domin yă yi tunani, sa’ad da ya ɗaga ido, sai ya ga raƙuma suna zuwa.
64 Rebecca leva les yeux, et quand elle vit Isaac, elle descendit du chameau.
Rebeka ma ta ɗaga ido sai ta ga Ishaku. Ta sauka daga raƙuminta da sauri,
65 Elle dit au serviteur: « Qui est l'homme qui marche dans le champ à notre rencontre? » Le serviteur a dit: « C'est mon maître. » Elle prit son voile, et se couvrit.
ta ce wa bawan, “Wane ne mutumin can a fili, da yake zuwa yă tarye mu?” Bawan ya ce, “Maigidana ne.” Saboda haka ta ɗauki mayafinta to rufe kanta.
66 Le serviteur raconta à Isaac toutes les choses qu'il avait faites.
Sai bawan ya faɗa wa Ishaku duk abin da ya yi.
67 Isaac la fit entrer dans la tente de Sara, sa mère; il prit Rebecca, et elle devint sa femme. Il l'aima. Isaac fut donc réconforté après la mort de sa mère.
Ishaku ya kawo ta cikin tentin mahaifiyarsa Saratu, ya kuma auri Rebeka. Ta haka ta zama matarsa, ya kuwa ƙaunace ta; Ishaku kuma ya ta’azantu bayan rasuwar mahaifiyarsa.

< Genèse 24 >