< Genèse 19 >

1 Les deux anges arrivèrent à Sodome le soir. Lot était assis à la porte de Sodome. Lot les vit et se leva pour aller à leur rencontre. Il se prosterna, le visage contre terre,
Mala’ikun nan biyu suka iso Sodom da yamma. Lot kuwa yana zama a hanyar shiga birnin. Da ya gan su, sai ya tashi don yă tarye su, ya kuma rusuna da fuskarsa har ƙasa.
2 et dit: « Voici, mes seigneurs, entrez dans la maison de votre serviteur, restez-y toute la nuit, lavez-vous les pieds, et vous pourrez vous lever de bonne heure et poursuivre votre route. » Ils ont dit: « Non, mais on va rester dans la rue toute la nuit. »
Ya ce, “Ranku yă daɗe, ina roƙonku ku ratsa zuwa gidan bawanku. Ku wanke ƙafafunku, ku kwana, sa’an nan ku kama hanyarku da sassafe.” Suka ce, “A’a, za mu kwana a dandali.”
3 Il les pressa beaucoup; ils vinrent avec lui, et entrèrent dans sa maison. Il leur fit un festin, il fit cuire des pains sans levain, et ils mangèrent.
Amma ya nace musu ƙwarai, sai suka tafi tare da shi, suka kuma shiga gidansa. Ya shirya musu abinci, ya gasa burodi marasa yisti, suka ci.
4 Mais avant qu'ils ne se couchent, les hommes de la ville, les hommes de Sodome, entourèrent la maison, jeunes et vieux, tous les gens de tous les quartiers.
Kafin suka shiga barci, sai ga dukan mutane, ƙanana da manya daga kowane ɓangare na birnin Sodom, suka kewaye gidan.
5 Ils appelèrent Lot et lui dirent: « Où sont les hommes qui sont entrés chez toi cette nuit? Fais-les sortir vers nous, afin que nous fassions l'amour avec eux. »
Suka kira Lot, suka ce, “Ina mutanen da suka zo wurinka a daren nan? Fito mana da su waje domin mu kwana da su.”
6 Lot sortit vers eux par la porte, et ferma la porte après lui.
Lot ya fita daga cikin gida, ya rufe ƙofar a bayansa. Ya je wurin mutanen
7 Il dit: « Je vous en prie, mes frères, n'agissez pas si méchamment.
ya ce musu, “A’a, abokaina kada ku yi wannan mummunan abu.
8 Voici, j'ai deux filles vierges. Laissez-moi vous les amener, et vous pourrez leur faire ce que vous voudrez. Mais ne faites rien à ces hommes, car ils sont venus à l'ombre de mon toit. »
Duba, ina da’ya’ya mata biyu waɗanda ba su taɓa sanin namiji ba, bari in kawo muku su ku yi kome da kuke so da su. Amma kada ku taɓa waɗannan mutane, gama su baƙina ne kuma dole in tsare su.”
9 Ils dirent: « Reculez! » Puis ils dirent: « Cet homme est venu vivre comme un étranger, et il se fait juge. Maintenant, nous allons faire pire avec toi qu'avec eux! » Ils pressèrent fortement l'homme Lot et s'approchèrent pour briser la porte.
Sai mutanen birnin suka amsa, “Ba mu wuri! Wannan mutum ya zo nan kamar baƙo, ga shi yanzu yana so yă zama alƙali! Za mu wulaƙanta ka fiye da su.” Suka ci gaba da matsa wa Lot lamba, suka matsa kusa domin su fasa ƙofar.
10 Mais les hommes tendirent la main, firent entrer Lot auprès d'eux dans la maison et fermèrent la porte.
Amma mutanen da suke ciki suka miƙa hannunsu, suka ja Lot zuwa cikin gida, suka rufe ƙofar.
11 Ils frappèrent de cécité les hommes qui étaient à la porte de la maison, petits et grands, de sorte qu'ils se fatiguèrent à trouver la porte.
Sai suka bugi mutanen da suke a bakin ƙofar gidan da makanta, ƙanana da manya duka, har suka gajiyar da kansu, suna lalluba inda ƙofar take.
12 Les hommes dirent à Lot: « As-tu quelqu'un d'autre ici? Beaux-fils, tes fils, tes filles, et tous ceux que tu as dans la ville, fais-les sortir de ce lieu;
Mutanen nan biyun suka ce wa Lot, “Kana da wani a nan, ko surukai, ko’ya’ya maza ko mata, ko kuwa wani dai a cikin birni wanda yake naka? Ka fitar da su daga nan,
13 car nous allons détruire ce lieu, car la protestation contre eux a été si grande devant Yahvé que Yahvé nous a envoyés pour le détruire. »
gama za mu hallaka wannan wuri. Kukan da aka yi ga Ubangiji game da mutanen birnin nan ya yi yawa sosai, ya sa har ya aiko mu domin mu hallaka birnin.”
14 Lot sortit et parla à ses gendres, qui s'étaient engagés à épouser ses filles, et dit: « Levez-vous! Sortez de ce lieu, car Yahvé va détruire la ville! » Mais il sembla à ses gendres qu'il plaisantait.
Saboda haka Lot ya tafi ya yi magana da surukansa waɗanda suka yi alkawari za su aure’ya’yansa mata. Ya ce, “Ku yi sauri ku fita daga wannan wuri, gama Ubangiji yana gab da hallaka birnin.” Amma surukansa suka ɗauka wasa yake yi.
15 Le matin venu, les anges pressèrent Lot en disant: « Lève-toi! Prends ta femme et tes deux filles qui sont ici, de peur que tu ne sois consumé par l'iniquité de la ville. »
Gari na wayewa, sai mala’ikun nan suka ƙarfafa Lot suna cewa, “Yi sauri! Ka ɗauki matarka da’ya’yanka biyu mata waɗanda suke a nan, don kada a shafe ku sa’ad da ake hukunta birnin.”
16 Mais il s'attarda; les hommes saisirent sa main, la main de sa femme et les mains de ses deux filles, Yahvé étant miséricordieux envers lui; ils le firent sortir et le déposèrent hors de la ville.
Da yana jan jiki, sai mutanen suka kama hannunsa da hannuwan matarsa da na’ya’yansa biyu mata, suka kai su bayan birni, gama Ubangiji ya nuna musu jinƙai.
17 Lorsqu'ils les eurent fait sortir, il dit: « Sauve-toi pour sauver ta vie! Ne regardez pas derrière vous, et ne restez pas dans la plaine. Fuyez vers les montagnes, de peur que vous ne soyez consumés! ».
Da suka fitar da su, sai ɗaya daga cikin mala’ikun ya ce, “Ku gudu domin ranku; kada ku duba baya, kada kuma ku tsaya ko’ina cikin kwarin! Ku gudu zuwa cikin duwatsu, don kada a hallaka ku!”
18 Lot leur dit: « Oh, non, mon seigneur.
Amma Lot ya ce musu, “A’a, ranka yă daɗe, ka yi haƙuri!
19 Vois maintenant, ton serviteur a trouvé grâce à tes yeux, et tu as magnifié ta bonté, dont tu as fait preuve à mon égard en me sauvant la vie. Je ne peux pas m'échapper vers la montagne, de peur que le mal ne m'atteigne et que je meure.
Bawanku ya riga ya sami tagomashi daga gare ku, kun kuma nuna mini alheri mai yawa. Ba zan iya in gudu zuwa duwatsu ba, wannan masifa za tă same ni, zan kuma mutu.
20 Vois maintenant, cette ville est proche pour y fuir, et c'est une petite ville. Oh! que je m'y échappe (n'est-ce pas une petite?), et mon âme vivra. »
Ga ɗan gari can ya fi kusa inda zan gudu in fake. Bari in gudu zuwa can, in tsirar da raina.”
21 Il lui dit: « Voici que j'ai exaucé ta demande concernant cette chose aussi, à savoir que je ne renverserai pas la ville dont tu as parlé.
Sai ya ce masa, “Na yarda da abin da ka ce, ba zan hallakar da garin da ka ambata ba.
22 Dépêche-toi de t'y échapper, car je ne peux rien faire tant que tu n'y seras pas arrivé. » C'est pourquoi le nom de la ville fut appelé Zoar.
Gaggauta, ka gudu zuwa can, ba zan yi kome ba sai ka isa can.” (Domin haka ne ake kira garin Zowar.)
23 Le soleil s'était levé sur la terre lorsque Lot arriva à Zoar.
A lokacin da Lot ya isa Zowar, rana ta hau.
24 Alors Yahvé fit pleuvoir du ciel sur Sodome et sur Gomorrhe du soufre et du feu, de la part de Yahvé.
Sai Ubangiji ya yi ta zuba kibiritu a bisa Sodom da Gomorra daga sama.
25 Il détruisit ces villes, toute la plaine, tous les habitants des villes et ce qui poussait sur le sol.
Haka ya hallakar da waɗannan birane da kuma kwarinsu gaba ɗaya, haɗe da dukan waɗanda suke zama a biranen, da kuma dukan shuke-shuke da suke cikin ƙasar.
26 Mais la femme de Lot regardait derrière lui, et elle devint une colonne de sel.
Amma matar Lot ta waiwaya baya, ta kuma zama ginshiƙin gishiri.
27 Abraham se leva de bon matin au lieu où il s'était tenu devant Yahvé.
Da sassafe kashegari, Ibrahim ya tashi ya koma wurin da dā ya tsaya a gaban Ubangiji.
28 Il regarda vers Sodome et Gomorrhe, et vers tout le pays de la plaine, et il vit que la fumée du pays montait comme la fumée d'une fournaise.
Ya duba ta wajen Sodom da Gomorra, da wajen dukan filayen ƙasar, sai ya ga hayaƙi baƙin ƙirin yana tashi daga ƙasar kamar hayaƙi daga matoya.
29 Lorsque Dieu détruisit les villes de la plaine, il se souvint d'Abraham et fit sortir Lot du milieu de la destruction, lorsqu'il détruisit les villes dans lesquelles Lot habitait.
Saboda haka sa’ad da Allah ya hallaka waɗannan biranen kwarin, ya tuna da Ibrahim, ya kuma fitar da Lot daga masifar da ta hallaka biranen da Lot ya zauna.
30 Lot monta de Tsoar et habita dans la montagne, avec ses deux filles, car il avait peur d'habiter à Tsoar. Il habita dans une grotte avec ses deux filles.
Lot da’ya’yansa biyu mata suka bar Zowar suka kuma zauna a cikin duwatsu, gama ya ji tsoro yă zauna a Zowar. Shi da’ya’yansa biyu mata suka zauna a ciki wani kogo.
31 L'aînée dit à la cadette: « Notre père est vieux, et il n'y a pas d'homme sur la terre pour entrer chez nous à la manière de toute la terre.
Wata rana’yarsa babba ta ce wa ƙanuwarta, “Mahaifinmu ya tsufa, kuma babu wani mutum kusa a nan da zai yi mana ciki mu haifi’ya’ya; yadda al’ada take a ko’ina a duniya.
32 Venez, faisons boire du vin à notre père, et nous coucherons avec lui, afin de préserver la lignée de notre père. »
Bari mu sa mahaifinmu yă sha ruwan inabi, sa’an nan sai mu kwana da shi, don kada zuriyar mahaifinmu ta ƙare.”
33 Ils firent boire du vin à leur père cette nuit-là; l'aînée entra et coucha avec son père. Il ne sut ni quand elle se coucha, ni quand elle se leva.
A wannan dare, suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi,’yar farin ta shiga ta kwana da shi. Shi kuwa bai san sa’ad da ta kwanta ko sa’ad da ta tashi ba.
34 Le lendemain, l'aînée dit au cadet: « Voici, j'ai couché cette nuit avec mon père. Faisons-lui boire du vin encore cette nuit. Tu entres et tu couches avec lui, afin que nous préservions la lignée de notre père. »
Kashegari,’yar farin ta ce wa ƙanuwar, “Jiya da dare na kwana da mahaifina. Bari mu sa yă sha ruwan inabi kuma yau da dare, ke ma ki shiga ki kwana da shi, domin kada zuriyar mahaifinmu ta ƙare.”
35 Ils firent boire du vin à leur père cette nuit-là aussi. La plus jeune alla se coucher avec lui. Il ne sut ni quand elle se coucha, ni quand elle se leva.
Sai suka sa mahaifinsu ya sha ruwan inabi, a wannan dare ma, ƙanuwar ta shiga ta kwana da shi. Bai kuwa san sa’ad da ta kwanta ko sa’ad da ta tashi ba.
36 Ainsi, les deux filles de Lot furent enceintes de leur père.
Ta haka’ya’yan Lot biyu mata duk suka yi ciki daga mahaifinsu.
37 L'aînée enfanta un fils, qu'elle appela Moab. Il est le père des Moabites, jusqu'à ce jour.
’Yar farin ta haifi ɗa, ta kuma ba shi suna Mowab, shi ne mahaifin Mowabawa a yau.
38 La cadette enfanta aussi un fils, qu'elle appela Ben Ammi. Il est le père des enfants d'Ammon jusqu'à ce jour.
’Yar ƙaramar ma ta haifi ɗa, ta kuwa ba shi suna Ben-Ammi, shi ne mahaifin Ammonawa a yau.

< Genèse 19 >