< Genèse 11 >

1 Toute la terre avait une seule langue et un seul langage.
To, a lokacin, yaren mutanen duniya ɗaya ne, maganarsu kuma ɗaya ce.
2 Comme ils voyageaient vers l'est, ils trouvèrent une plaine dans le pays de Shinar, et ils y habitèrent.
Yayinda mutane suke ta yin ƙaura zuwa gabas, sai suka sami fili a Shinar, suka zauna a can.
3 Ils se dirent les uns aux autres: « Venez, faisons des briques, et brûlons-les bien. » Ils avaient la brique pour pierre, et le goudron pour mortier.
Suka ce wa juna, “Ku zo, mu yi tubula, mu gasa su sosai.” Suka yi amfani da tubula a maimakon duwatsu, kwalta kuma a maimakon laka.
4 Ils dirent: « Venez, bâtissons-nous une ville et une tour dont le sommet atteint le ciel, et faisons-nous un nom, de peur que nous ne soyons dispersés sur la surface de toute la terre. »
Sa’an nan suka ce, “Ku zo, mu gina wa kanmu birni da hasumiyar da za tă kai har sammai, domin mu yi wa kanmu suna, don kada mu warwatsu ko’ina a doron ƙasa.”
5 Yahvé descendit pour voir la ville et la tour que les enfants des hommes avaient bâties.
Sai Ubangiji ya sauko don yă ga birni da kuma hasumiyar da mutanen suke gini.
6 L'Éternel dit: « Voici, ils forment un seul peuple, et ils ont tous une seule langue, et voici ce qu'ils commencent à faire. Maintenant, rien ne leur sera refusé de ce qu'ils ont l'intention de faire.
Ubangiji ya ce, “Ga su, su jama’a ɗaya ce, su duka kuwa harshensu guda ne. Wannan kuwa masomi ne kawai na abin da za su iya yi, babu kuma abin da suka yi shirya yi da ba za su iya yi ba.
7 Venez, descendons, et là nous confondrons leur langue, afin qu'ils ne comprennent pas le langage les uns des autres. »
Zo, mu sauka, mu rikitar da harshensu don kada su fahimci juna.”
8 Yahvé les dispersa donc à partir de là sur la surface de toute la terre. Ils cessèrent de construire la ville.
Saboda haka Ubangiji ya watsar da su daga wurin zuwa ko’ina a doron ƙasa, suka kuwa daina gina birnin.
9 C'est pourquoi on l'appela Babel, parce que Yahvé y confondit le langage de toute la terre. De là, Yahvé les dispersa sur la surface de toute la terre.
Shi ya sa aka kira birnin Babel, domin a can ne Ubangiji ya rikitar da harshen dukan duniya. Daga can Ubangiji ya watsar da su ko’ina a doron ƙasa.
10 Voici l'histoire des générations de Sem: Sem était âgé de cent ans lorsqu'il engendra Arpachshad, deux ans après le déluge.
Wannan shi ne labarin Shem. Shekara biyu bayan ambaliya, sa’ad da Shem ya yi shekara 100, sai ya haifi Arfakshad.
11 Sem vécut cinq cents ans après avoir engendré Arpacshad, et il engendra d'autres fils et d'autres filles.
Bayan ya haifi Arfakshad, Shem ya yi shekara 500, ya haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
12 Arpacshad vécut trente-cinq ans, et il engendra Shéla.
Sa’ad da Arfakshad ya yi shekara 35, sai ya haifi Shela.
13 Arpacshad vécut quatre cent trois ans après avoir engendré Shéla, et il engendra d'autres fils et d'autres filles.
Bayan ya haifi Shela kuwa, Arfakshad ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
14 Shéla vécut trente ans, et il engendra Eber.
Sa’ad da Shela ya yi shekaru 30, sai ya haifi Eber.
15 Shéla vécut quatre cent trois ans après avoir engendré Eber, et il engendra d'autres fils et d'autres filles.
Bayan ya haifi Eber, Shela ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
16 Eber vécut trente-quatre ans, et devint le père de Péleg.
Sa’ad da Eber ya yi shekaru 34, sai ya haifi Feleg.
17 Eber vécut quatre cent trente ans après avoir engendré Peleg, et il engendra d'autres fils et d'autres filles.
Bayan ya haifi Feleg, Eber ya yi shekara 430, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
18 Péleg vécut trente ans et devint le père de Reu.
Sa’ad da Feleg ya yi shekaru 30, sai ya haifi Reyu.
19 Péleg vécut deux cent neuf ans après avoir engendré Reu, et il engendra d'autres fils et d'autres filles.
Bayan ya haifi Reyu, Feleg ya yi shekara 209, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
20 Reu vécut trente-deux ans, et devint le père de Serug.
Sa’ad da Reyu ya yi shekaru 32, sai ya haifi Serug.
21 Reu vécut deux cent sept ans après avoir engendré Serug, et il engendra d'autres fils et d'autres filles.
Bayan ya haifi Serug, Reyu ya yi shekara 207, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
22 Serug vécut trente ans, et devint le père de Nachor.
Sa’ad da Serug ya yi shekaru 30, sai ya haifi Nahor.
23 Serug vécut deux cents ans après avoir engendré Nachor, et il engendra d'autres fils et d'autres filles.
Bayan ya haifi Nahor, Serug ya yi shekara 200, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
24 Nachor vécut vingt-neuf ans, et devint le père de Térah.
Sa’ad da Nahor ya yi shekaru 29, sai ya haifi Tera.
25 Nachor vécut cent dix-neuf ans après avoir engendré Térah, et il engendra d'autres fils et d'autres filles.
Bayan ya haifi Tera, Nahor ya yi shekara 119, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
26 Térah vécut soixante-dix ans et devint le père d'Abram, de Nahor et de Haran.
Bayan Tera ya yi shekaru 70, sai ya haifi Abram, Nahor da Haran.
27 Voici l'histoire des générations de Térah. Térah est le père d'Abram, de Nahor et de Haran. Haran est le père de Lot.
Wannan ita ce zuriyar Tera. Tera ya haifi Abram, Nahor da Haran. Haran kuma ya haifi Lot.
28 Haran mourut dans le pays où il était né, à Ur des Chaldéens, alors que son père Térah vivait encore.
Yayinda mahaifinsa Tera yana da rai, Haran ya rasu a Ur ta Kaldiyawa, a ƙasar haihuwarsa.
29 Abram et Nachor épousèrent des femmes. Le nom de la femme d'Abram était Saraï, et le nom de la femme de Nachor était Milca, fille de Haran, qui était aussi le père d'Isca.
Abram da Nahor suka yi aure. Sunan matar Abram, Saira ne, sunan matar Nahor kuwa Milka; ita’yar Haran ce, mahaifin Milka da Iska.
30 Saraï était stérile. Elle n'avait pas d'enfant.
Saira kuwa bakararriya ce, ba ta da yara.
31 Térah prit Abram, son fils, Lot, fils de Haran, fils de son fils, et Saraï, sa belle-fille, femme de son fils Abram. Ils partirent d'Ur des Chaldéens, pour aller au pays de Canaan. Ils arrivèrent à Haran et y habitèrent.
Tera ya ɗauki ɗansa Abraham, jikansa Lot ɗan Haran, da surukarsa Saira, matar Abram, tare kuwa suka bar Ur ta Kaldiyawa, don su tafi Kan’ana. Amma sa’ad da suka zo Haran sai suka zauna a can.
32 Les jours de Térah furent de deux cent cinq ans. Térah mourut à Haran.
Tera yi shekaru 205, ya kuma mutu a Haran.

< Genèse 11 >