< Genèse 10 >

1 Voici l'histoire des générations des fils de Noé, de Sem, de Cham et de Japhet. Des fils leur sont nés après le déluge.
Wannan shi ne labarin Shem, Ham da Yafet,’ya’yan Nuhu maza, waɗanda su ma sun haifi’ya’ya maza bayan ambaliyar.
2 Les fils de Japhet étaient: Gomer, Magog, Madai, Javan, Tubal, Meshech et Tiras.
’Ya’yan Yafet maza su ne, Gomer, Magog, Madai da Yaban, Tubal, Meshek, da kuma Tiras.
3 Les fils de Gomer étaient: Ashkenaz, Riphath et Togarmah.
’Ya’yan Gomer maza su ne, Ashkenaz, Rifat, da Togarma.
4 Les fils de Javan étaient: Élischa, Tarsis, Kittim et Dodanim.
’Ya’yan maza Yaban su ne, Elisha, Tarshish, Kittim da Rodanim.
5 C'est de là que datent les îles des nations, réparties selon leurs terres, chacun selon sa langue, selon ses familles, selon ses nations.
(Daga waɗannan mutane ne masu zama a bakin teku suka bazu zuwa cikin ƙasashensu da kuma cikin al’ummansu, kowanne da yarensa.)
6 Les fils de Cham étaient: Cush, Mizraïm, Put et Canaan.
’Ya’yan Ham maza su ne, Kush, Masar, Fut, da Kan’ana.
7 Les fils de Cush étaient: Seba, Havilah, Sabtah, Raamah et Sabteca. Les fils de Raama étaient: Saba et Dedan.
’Ya’yan Kush maza su ne, Seba, Hawila, Sabta, Ra’ama da Sabteka.’Ya’yan Ra’ama maza kuwa su ne, Sheba da Dedan.
8 Cush fut le père de Nimrod. Celui-ci commença à être puissant sur la terre.
Kush shi ne mahaifin Nimrod wanda ya yi girma ya zama jarumin yaƙi a duniya.
9 Il fut un puissant chasseur devant Yahvé. C'est pourquoi on dit: « comme Nimrod, un puissant chasseur devant Yahvé ».
Shi babban maharbi ne a gaban Ubangiji. Shi ya sa akan ce, kamar Nimrod babban maharbi a gaban Ubangiji.
10 Le commencement de son royaume était Babel, Erech, Accad et Calneh, dans le pays de Shinar.
Cibiyoyin mulkinsa na farko su ne Babilon, Erek, Akkad, da Kalne a cikin Shinar.
11 De ce pays, il alla en Assyrie, et bâtit Ninive, Rehoboth Ir, Calah,
Daga wannan ƙasa, sai ya tafi Assuriya, inda ya gina Ninebe, Rehobot Ir, Kala
12 et Resen entre Ninive et la grande ville de Calah.
da Resen, wadda take tsakanin Ninebe da Kala; wanda yake babban birni.
13 Mizraïm engendra Ludim, Anamim, Lehabim, Naphtuhim,
Mizrayim shi ne mahaifin Ludiyawa, Anamawa, Lehabiyawa, Naftuhiyawa,
14 Pathrusim, Casluhim (dont descendent les Philistins) et Caphtorim.
Fetrusiyawa, da Kasluhiyawa (inda Filistiyawa suka fito) da kuma Kaftorawa.
15 Canaan engendra Sidon, son premier-né, Heth,
Kan’ana shi ne mahaifin, Sidon ɗan farinsa, da na Hittiyawa,
16 les Jébusiens, les Amorites, les Girgashites,
Yebusiyawa, Amoriyawa, Girgashiyawa,
17 les Hivites, les Arkites, les Sinites,
Hiwiyawa, Arkiyawa, Siniyawa,
18 les Arvadites, les Zemarites et les Hamathites. Par la suite, les familles des Cananéens se sont dispersées.
Arbadiyawa, Zemarawa, da Hamawa. Daga baya zuriyar Kan’aniyawa suka yaɗu
19 La frontière des Cananéens s'étendait de Sidon, en allant vers Gerar, à Gaza, en allant vers Sodome, Gomorrhe, Adma et Zéboïm, à Lasha.
har iyakar Kan’ana ta kai Sidon ta wajen Gerar har zuwa Gaza, sa’an nan ta milla zuwa Sodom, Gomorra, Adma da Zeboyim, har zuwa Lasha.
20 Voici les fils de Cham, selon leurs familles, selon leurs langues, dans leurs pays et leurs nations.
Waɗannan su ne’ya’yan Ham maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
21 Des enfants naquirent aussi à Sem (frère aîné de Japhet), père de tous les enfants d'Eber.
Aka kuma haifa wa Shem, wan Yafet,’ya’ya maza. Shem shi ne kakan’ya’yan Eber duka.
22 Les fils de Sem furent: Élam, Asshur, Arpachshad, Lud et Aram.
’Ya’yan Shem maza su ne, Elam, Asshur, Arfakshad, Lud da Aram.
23 Les fils d'Aram étaient: Uz, Hul, Gether et Mash.
’Ya’yan Aram maza su ne, Uz, Hul, Geter da Mash.
24 Arpacshad engendra Shéla. Schéla engendra Eber.
Arfakshad ne mahaifin Shela. Shela kuma shi ne mahaifin Eber.
25 A Eber naquirent deux fils. Le nom de l'un était Peleg, car en son temps la terre fut divisée. Le nom de son frère était Joktan.
Aka haifa wa Eber’ya’ya maza biyu. Aka ba wa ɗaya suna Feleg, gama a zamaninsa ne aka raba duniya; aka kuma sa wa ɗan’uwansa suna Yoktan.
26 Joktan engendra Almodad, Sheleph, Hazarmaveth, Jerah,
Yoktan shi ne mahaifin, Almodad, Shelef, Hazarmawet, Yera,
27 Hadoram, Uzal, Diklah,
Hadoram, Uzal, Dikla,
28 Obal, Abimael, Sheba,
Obal, Abimayel, Sheba,
29 Ophir, Havilah et Jobab. Tous ceux-là étaient fils de Joktan.
Ofir, Hawila da Yobab. Dukan waɗannan’ya’yan Yoktan maza ne.
30 Leur demeure s'étendait depuis Mesha, en allant vers Séphar, la montagne de l'orient.
Yankin da suka zauna ya miƙe daga Mesha zuwa wajen Sefar a gabashin ƙasar tudu.
31 Ce sont là les fils de Sem, selon leurs familles, selon leurs langues, leurs terres et leurs nations.
Waɗannan su ne’ya’yan Shem maza bisa ga zuriyarsu da yarurrukansu, cikin ƙasashensu da kuma al’ummominsu.
32 Ce sont là les familles des fils de Noé, selon leurs générations, en fonction de leurs nations. Les nations se sont divisées à partir de celles-ci sur la terre après le déluge.
Waɗannan su ne zuriyar’ya’yan Nuhu maza bisa ga jerin zuriyarsu cikin al’ummominsu. Daga waɗannan ne al’ummomi suka bazu ko’ina a duniya bayan ambaliya.

< Genèse 10 >