< Esdras 7 >

1 Après ces choses, sous le règne d'Artaxerxès, roi de Perse, Esdras, fils de Seraja, fils d'Azaria, fils de Hilkija,
Bayan waɗannan abubuwa, a zamanin Artazerzes sarkin Farisa, sai Ezra ɗan Serahiya, ɗan Azariya, ɗan Hilkiya,
2 fils de Schallum, fils de Tsadok, fils d'Ahitub,
ɗan Shallum, ɗan Zadok, ɗan Ahitub,
3 fils d'Amaria, fils d'Azaria, fils de Meraïoth,
ɗan Amariya, ɗan Azariya, ɗan Merahiyot,
4 fils de Zérachia, fils d'Uzzi, fils de Bukki,
ɗan Zerahiya, ɗan Uzzi, ɗan Bukki,
5 fils d'Abischua, fils de Phinées, fils d'Éléazar, fils d'Aaron, le grand prêtre,
ɗan Abishuwa, ɗan Finehas, ɗan Eleyazar, ɗan Haruna babban firist.
6 cet Esdras monta de Babylone. Il était un scribe habile dans la loi de Moïse, que Yahvé, le Dieu d'Israël, avait donnée; et le roi lui accorda tout ce qu'il demandait, selon la main de Yahvé, son Dieu, sur lui.
Shi Ezra ɗin ya zo daga Babilon. Shi malami ne ya kuma san Dokar Musa sosai wadda Ubangiji, Allah na Isra’ila ya bayar. Sarki ya ba shi duk abin da ya roƙa, gama Ubangiji Allahnsa yana tare da shi.
7 Quelques-uns des enfants d'Israël, dont une partie des prêtres, des lévites, des chantres, des portiers et des serviteurs du temple, montèrent à Jérusalem la septième année du roi Artaxerxès.
Waɗansu Isra’ilawa, haɗe da firistoci, da Lawiyawa, da mawaƙa, da masu tsaron ƙofofi, da masu aiki a haikali su ma suka zo Urushalima a shekara ta bakwai a zamanin mulkin sarki Artazerzes.
8 Il arriva à Jérusalem au cinquième mois, c'est-à-dire la septième année du roi.
Ezra ya iso Urushalima a wata na biyar na shekara ta bakwai na kama mulkin sarkin.
9 En effet, le premier jour du premier mois, il commença à monter de Babylone, et le premier jour du cinquième mois, il arriva à Jérusalem, selon la bonne main de son Dieu sur lui.
Ya fara tafiyarsa daga Babilon a rana ta farko ga watan farko, ya kuma iso Urushalima a rana ta farko ga watan biyar, gama alherin Allahnsa yana tare da shi.
10 Car Esdras avait mis son cœur à rechercher la loi de Yahvé et à la mettre en pratique, et à enseigner les lois et les ordonnances en Israël.
Gama Ezra ya miƙa kansa ga bincike da kuma kiyaye Dokar Ubangiji, da kuma koya wa Isra’ilawa dokoki da kuma umarnan Ubangiji.
11 Et voici la copie de la lettre que le roi Artaxerxès donna au sacrificateur Esdras, le scribe, le rédacteur des paroles des commandements de l'Éternel et de ses statuts pour Israël:
Ga wasiƙar da sarki Artazerzes ya ba Ezra wanda yake firist da kuma malami, mutumin da yake cike da sani game da dokoki da kuma umarnan Ubangiji wa Isra’ila.
12 Artaxerxès, roi des rois, A Esdras le prêtre, le scribe de la loi du Dieu parfait du ciel. Or,
Artazerzes, sarkin sarakuna. Zuwa ga Ezra firist, malamin Dokar Allah na sama. Gaisuwa.
13 je décrète que tous ceux du peuple d'Israël, de ses prêtres et des lévites qui se trouvent dans mon royaume et qui ont l'intention de se rendre à Jérusalem de leur plein gré, iront avec vous.
Yanzu ina ba da umarni cewa duk wani mutumin Isra’ilan da yake cikin mulkina, haɗe da firistoci, da Lawiyawa, da suke so su tafi tare da kai zuwa Urushalima za su iya tafiya.
14 Car tu es envoyé par le roi et ses sept conseillers pour enquêter sur Juda et Jérusalem, selon la loi de ton Dieu qui est entre tes mains,
Sarki ne da mashawartansa guda bakwai suka aike ka don ka je ka ga halin da Yahuda da Urushalima suke ciki game da dokokin Allahnka, waɗanda suke a hannunka.
15 et pour porter l'argent et l'or que le roi et ses conseillers ont offert librement au Dieu d'Israël, dont la demeure est à Jérusalem,
Za ka kuma tafi da zinariya da azurfa waɗanda sarki da mashawartansa suka ba da kyautar yardar rai ga Allah na Isra’ila, wanda haikalinsa ke a Urushalima,
16 et tout l'argent et l'or que tu trouveras dans toute la province de Babylone, avec les offrandes volontaires du peuple et des prêtres pour la maison de leur Dieu qui est à Jérusalem.
haɗe da duk zinariya da azurfan da za ka iya samu a Babilon, da kuma duk bayarwar yardar rai daga mutane da firistoci, domin haikalin Allahnsu da yake a Urushalima.
17 Tu achèteras avec cet argent des taureaux, des béliers et des agneaux, avec leurs offrandes et leurs libations, et tu les offriras sur l'autel de la maison de ton Dieu qui est à Jérusalem.
Ka tabbata ka yi amfani da kuɗin nan don ka sayi bijimai, da raguna, da’yan raguna, da hadayu na gari, da na sha, ka kuma miƙa su a kan bagade na haikalin Allahnka a Urushalima.
18 Tout ce que vous et vos frères jugerez bon de faire avec le reste de l'argent et de l'or, faites-le selon la volonté de votre Dieu.
Sa’an nan kai da’yan’uwanka Yahudawa ku yi abin da kuka ga ya fi kyau da sauran zinariya da azurfa ɗin bisa ga nufin Allah.
19 Les objets qui vous seront donnés pour le service de la maison de votre Dieu, livrez-les devant le Dieu de Jérusalem.
Ka kai wa Allah na Urushalima duk kayan da aka ba ka amanarsu don yin sujada a haikalin Allahnka.
20 Tout ce qui sera nécessaire pour la maison de ton Dieu et que tu auras l'occasion de donner, donne-le de la maison du trésor du roi.
Duk kuma wani abin da ake bukata domin haikalin Allahnka, daga ɗakunan ajiya sarki za ka fitar da kuɗin.
21 Moi, le roi Artaxerxès, j'ordonne à tous les trésoriers qui sont de l'autre côté du fleuve que tout ce que le prêtre Esdras, le scribe de la loi du Dieu des cieux, vous demandera, vous le ferez avec toute la diligence voulue,
Yanzu fa ni, Sarki Artazerzes, ina ba da umarni ga kowane ma’aji na Kewayen Kogin Yuferites su tanada duk abin da Ezra firist, wanda kuma yake malamin Dokar Allah na sama zai bukaci,
22 jusqu'à cent talents d'argent, cent cors de froment, cent baths de vin, cent baths d'huile, et du sel, sans qu'il soit nécessaire d'en indiquer la quantité.
har zuwa talenti ɗari na azurfa, da mudu ɗari na alkama, da garwa ɗari na ruwan inabi, da garwa ɗari na man zaitun, da kuma gishiri ba iyaka.
23 Tout ce qui est ordonné par le Dieu des cieux, que cela soit fait exactement pour la maison du Dieu des cieux; car pourquoi y aurait-il de la colère contre le royaume du roi et de ses fils?
A yi duk abin da Allah na sama ya ce don haikalin Allah na sama, sai a yi shi da himma. Me zai sa a jawo wa sarki da’ya’yansa fushin Allah?
24 Nous vous informons également qu'il ne sera pas permis d'imposer un tribut, une coutume ou un péage aux prêtres, aux lévites, aux chantres, aux gardiens des portes, aux employés du temple ou aux ouvriers de cette maison de Dieu.
Ku kuma san cewa, ba ku da ikon sa firistoci, da Lawiyawa, da mawaƙa, da masu tsaron ƙofofin haikali, da masu aiki a gidan Allah, ko waɗansu masu aiki a haikali su biya haraji, ko kuɗin shiga.
25 Toi, Esdras, selon la sagesse de ton Dieu qui est dans ta main, nomme des magistrats et des juges qui puissent juger tout le peuple qui est au-delà du fleuve, qui tous connaissent les lois de ton Dieu, et instruire celui qui ne les connaît pas.
Kai kuma Ezra, bisa ga hikimar da Allah ya ba ka, sai ka zaɓi mahukunta da alƙalai waɗanda za su zama masu yanke hukunci ga dukan mutanen Kewayen Kogin Yuferites, duk waɗanda suka san dokokin Allahnka, ka kuma koya wa duk waɗanda ba su san dokokin ba.
26 Si quelqu'un ne se conforme pas à la loi de ton Dieu et à la loi du roi, que le jugement soit exécuté sur lui avec toute la diligence voulue, que ce soit la mort, le bannissement, la confiscation des biens ou la prison.
Ba shakka duk wanda bai yi biyayya da dokokin Allahnka ba, da kuma dokokin sarki ba dole a yanke masa hukuncin kisa, ko hukuncin kora, ko hukuncin raba shi da mallakarsa, ko kuma hukuncin kulle shi a kurkuku.
27 Béni soit Yahvé, le Dieu de nos pères, qui a mis une telle chose dans le cœur du roi, pour embellir la maison de Yahvé qui est à Jérusalem;
Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah na kakanninmu, ya taɓa zuciyar sarki don yă kawo ɗaukaka ga haikalin Allah a Urushalima ta wannan hanya.
28 et qui m'a accordé sa bienveillance devant le roi et ses conseillers, et devant tous les princes puissants du roi. J'ai été fortifié selon la main de Yahvé mon Dieu sur moi, et j'ai rassemblé des chefs d'Israël pour monter avec moi.
Wanda kuma ya sa na sami tagomashi a gaban sarki da mashawartansa, da kuma duk manyan masu muƙami nasa. Gama Ubangiji Allahna yana tare da ni, sai na sami ƙarfin hali na tattara shugabannin mutane daga Isra’ila, don mu tafi tare.

< Esdras 7 >