< Esdras 6 >

1 Alors le roi Darius donna un ordre, et l'on fouilla la maison des archives, où les trésors étaient déposés à Babylone.
Sarki Dariyus kuwa ya ba da umarni a bincika a duba cikin littattafan tarihin da suke a ajiye a wurin ajiyarsu a Babilon.
2 On trouva un rouleau à Achmetha, dans le palais qui est dans la province de Médie, et voici ce qui y était écrit pour mémoire:
Sai aka sami takarda a Ekbatana a yankin Mediya, ga kuma abin da yake rubuce a ciki. Abin tunawa.
3 La première année du roi Cyrus, le roi Cyrus donna un ordre: En ce qui concerne la maison de Dieu à Jérusalem, que la maison soit construite, le lieu où l'on offre des sacrifices, et que ses fondations soient solidement posées, avec sa hauteur de soixante coudées et sa largeur de soixante coudées;
A shekara ta farko ta mulkin sarki Sairus, sarki ya ba da umarni game da haikalin Allah a Urushalima, ya ce, Bari a sāke gina haikalin yă zama wurin miƙa hadayu, a kuma aza harsashin ginin haikalin. Tsayinsa zai zama ƙafa tasa’in, fāɗinsa kuma kamu tasa’in.
4 avec trois rangées de grandes pierres et une rangée de bois neuf. Les dépenses seront payées sur la maison du roi.
Za a jera manyan duwatsu jeri uku, da jeri ɗaya na katako. Daga asusun sarki kuma za a biya kuɗin aikin.
5 Que les objets d'or et d'argent de la maison de Dieu, que Nabuchodonosor a enlevés du temple de Jérusalem et transportés à Babylone, soient restaurés et ramenés dans le temple de Jérusalem, à leur place. Tu les mettras dans la maison de Dieu.
Kwanonin zinariya da na azurfan gidan Allah waɗanda Nebukadnezzar ya kwashe daga haikali a Urushalima ya kawo Babilon, a mayar da su wurinsu a haikali a Urushalima; a sa su cikin gidan Allah.
6 Maintenant, Tattenaï, gouverneur de l'autre côté du fleuve, Shetharbozenaï, et tes compagnons, les Apharsacites, qui sont de l'autre côté du fleuve, vous devez rester loin de là.
Saboda haka Tattenai, gwamnan Kewayen Kogin Yuferites, da Shetar-Bozenai, da ku masu muƙami na yankin, ku bar wurin.
7 Laissez l'ouvrage de cette maison de Dieu; laissez le gouverneur des Juifs et les anciens des Juifs construire cette maison de Dieu à sa place.
Kada ku hana wannan aiki na haikalin Allah. Bari gwamnan Yahudawa, da dattawan Yahudawa su sāke gina wannan gidan Allah a wurin da yake a dā.
8 J'établis un décret sur ce que vous devez faire pour ces anciens des Juifs, pour la construction de cette maison de Dieu: sur les biens du roi, sur le tribut de l'autre côté du fleuve, des dépenses doivent être faites en toute diligence pour ces hommes, afin qu'ils ne soient pas gênés.
Na kuma ba da umarni game da abin da za ku yi wa dattawan Yahudawa cikin aikin ginin wannan gidan Allah. Daga asusun sarki a kuɗin da yake shigo wa Kewayen Kogin Yuferites za a biya mutanen nan duka, domin kada aikin yă tsaya.
9 Ce dont ils ont besoin, jeunes taureaux, béliers et agneaux, pour les holocaustes au Dieu des cieux, ainsi que du blé, du sel, du vin et de l'huile, selon la parole des prêtres qui sont à Jérusalem, on le leur donnera chaque jour sans faute,
A tanada musu duk abin da suke bukata. A ba su’yan bijimai, da raguna, da’yan tumaki domin miƙa hadaya ta ƙonawa ga Allah na sama, haka kuma dole a tanada wa firistoci alkama, da gishiri, da ruwan inabi, da mai, kullum ba fasawa yadda firistoci suke yi a Urushalima
10 afin qu'ils puissent offrir des sacrifices d'une agréable odeur au Dieu des cieux, et prier pour la vie du roi et de ses fils.
domin su miƙa hadayu masu daɗi ga Allah na Sama, su kuma yi addu’a domin lafiyar sarki da’ya’yansa.
11 J'ai aussi décrété que celui qui altérera ce message, qu'on arrache une poutre de sa maison, qu'on le soulève et qu'on l'attache dessus, et que sa maison devienne un tas de fumier à cause de cela.
Na kuma yi umarni cewa duk wanda ya karya wannan doka sai a fitar da itace daga cikin gidansa, a fiƙe kan itacen, a tsire mutumin, sa’an nan a mai da gidansa juji.
12 Que le Dieu qui y a fait résider son nom renverse tous les rois et les peuples qui tendent la main pour altérer ceci, pour détruire cette maison de Dieu qui est à Jérusalem. Moi, Darius, j'ai pris un décret. Que cela soit fait avec toute la diligence voulue.
Bari Allah yă sa sunansa yă kasance, yă hamɓarar da duka wani sarki ko mutanen da za su sa hannu don a sāke wannan doka, ko kuma don su rushe haikalin nan a Urushalima. Ni Dariyus na ba da wannan umarni, bari a yi biyayya babu wasa.
13 Alors Tattenai, gouverneur de l'autre côté du fleuve, Shetharbozenai et leurs compagnons firent tout cela avec diligence, car le roi Darius avait envoyé un décret.
Saboda umarnin da sarki Dariyus ya aika, sai Tattenai, gwamnan Kewayen Kogin Yuferites da Shetar-Bozenai da abokansu suka yi biyayya da umarnin babu wasa.
14 Les anciens des Juifs bâtirent et prospérèrent, grâce à la prophétie d'Aggée, le prophète, et de Zacharie, fils d'Iddo. Ils la bâtirent et l'achevèrent, selon le commandement du Dieu d'Israël et selon le décret de Cyrus, de Darius et d'Artaxerxès, roi de Perse.
Dattawan Yahuda kuwa suka ci gaba da ginin suna yin nasara ta wurin wa’azin Haggai annabi da Zakariya ɗan Iddo. Suka kuma gama ginin haikalin bisa ga umarnin Allah na Isra’ila da kuma umarnin Sairus da Artazerzes, sarakunan Farisa.
15 Cette maison fut achevée le troisième jour du mois d'Adar, la sixième année du règne du roi Darius.
An gama ginin haikalin a rana ta uku na watan Adar a shekara ta shida ta mulkin Sarki Dariyus.
16 Les enfants d'Israël, les sacrificateurs, les Lévites et le reste des enfants de la captivité, célébrèrent avec joie la dédicace de cette maison de Dieu.
Sai mutanen Isra’ila, firistoci, Lawiyawa da kuma sauran waɗanda suka dawo daga bauta suka yi bikin keɓe gidan Allah, cike da farin ciki.
17 Ils offrirent à la dédicace de cette maison de Dieu cent taureaux, deux cents béliers, quatre cents agneaux, et en sacrifice pour le péché pour tout Israël, douze boucs, selon le nombre des tribus d'Israël.
Suka miƙa bijimai guda ɗari, da raguna ɗari biyu, da’yan raguna ɗari huɗu. Suka kuma miƙa hadayu don zunubi saboda dukan Isra’ila, suka kuma miƙa bunsurai guda goma sha biyu don hadaya ta zunubi, kowane bunsuru ɗaya don kowace kabila ta Isra’ila.
18 Ils établirent les sacrificateurs selon leurs divisions et les Lévites selon leurs classes, pour le service de Dieu qui est à Jérusalem, comme il est écrit dans le livre de Moïse.
Suka kuma naɗa firistoci a gundumominsu da kuma Lawiyawa a ƙungiyoyinsu don hidimar Allah a Urushalima, bisa ga abin da aka rubuta a Littafin Musa.
19 Les enfants de la captivité célébrèrent la Pâque le quatorzième jour du premier mois.
A rana ta goma sha huɗu ga watan farko, sai waɗanda suka dawo daga bauta suka yi Bikin Ƙetarewa.
20 Comme les prêtres et les lévites s'étaient purifiés ensemble, ils étaient tous purs. Ils immolèrent la Pâque pour tous les enfants de la captivité, pour leurs frères les prêtres et pour eux-mêmes.
Firistoci da Lawiyawa suka tsarkake kansu, suka zama da tsabta. Lawiyawa suka yanka ragon Bikin Ƙetarewa domin dukan waɗanda suka dawo daga bauta, da kuma domin’yan’uwansu firistoci, da kuma domin kansu.
21 Les enfants d'Israël revenus de la captivité et tous ceux qui s'étaient séparés de la souillure des nations du pays pour chercher Yahvé, le Dieu d'Israël, mangèrent,
Sai Isra’ilawa waɗanda suka dawo daga bauta suka ci tare da duk waɗanda suka keɓe kansu daga halin ƙazanta na Al’ummai maƙwabtansu, don su nemi Ubangiji, Allah na Isra’ila.
22 et célébrèrent avec joie la fête des pains sans levain pendant sept jours, car Yahvé les avait rendus joyeux et avait tourné vers eux le cœur du roi d'Assyrie, pour fortifier leurs mains dans l'œuvre de Dieu, la maison d'Israël.
Suka yi kwana bakwai suna Bikin Burodi Marar Yisti, suna cike da farin ciki, gama Ubangiji ya cika su da farin ciki don ya sa sarkin Assuriya ya canja tunaninsa, ya taimake su cikin aikin gidan Allah, Allah na Isra’ila.

< Esdras 6 >