< Esdras 5 >

1 Les prophètes, Aggée le prophète et Zacharie le fils d'Iddo, prophétisèrent aux Juifs qui étaient en Judée et à Jérusalem. Ils leur prophétisèrent au nom du Dieu d'Israël.
Sai annabi Haggai, da annabi Zakariya zuriyar Iddo, suka yi wa Yahudawa a Yahuda da Urushalima annabci a cikin sunan Allah na Isra’ila wanda yake da mulki a kansu.
2 Alors Zorobabel, fils de Shealtiel, et Josué, fils de Jozadak, se levèrent et commencèrent à bâtir la maison de Dieu qui est à Jérusalem; et avec eux les prophètes de Dieu, qui les aidaient.
Sa’an nan Zerubbabel ɗan Sheyaltiyel da Yeshuwa ɗan Yozadak suka yi shiri suka kama aikin sāke gina gidan Allah a Urushalima. Annabawan Allah kuwa suna tare da su, suna taimakonsu.
3 Au même moment, Tattenaï, gouverneur de l'autre côté du fleuve, vint vers eux, avec Shetharbozenaï et leurs compagnons, et leur demanda: « Qui vous a donné l'ordre de construire cette maison et d'achever ce mur? »
A wannan lokaci, Tattenai gwamnan Kewayen Kogin Yuferites, da Shetar-Bozenai da abokansu suka je wurinsu suka tambaye su cewa, “Wa ya ba ku iko ku sāke gina wannan haikali har ku gyara katangar?”
4 Ils demandèrent aussi les noms des hommes qui construisaient cette maison.
Suka kuma tambaye su “Ina sunayen waɗanda suke wannan gini?”
5 Mais l'œil de leur Dieu était sur les anciens des Juifs, et ils ne les firent pas cesser jusqu'à ce que l'affaire parvienne à Darius, et qu'une réponse leur soit donnée par lettre à ce sujet.
Amma Allah yana tsaron dattawan Yahudawa, saboda haka ba a hana su aikin ba har sai rahoto ya kai wurin Dariyus aka kuma sami amsarsa a rubuce tukuna.
6 Voici la copie de la lettre que Tattenaï, gouverneur de l'autre côté du fleuve, Schetharbozenaï et ses compagnons, les Apharsachites qui étaient de l'autre côté du fleuve, envoyèrent au roi Darius.
Ga wasiƙar da Tattenai, gwamnan Kewayen Kogin Yuferites, da Shetar-Bozenai da abokansu masu riƙe da muƙamai a Kewayen Kogin Yuferites suka aika wa Sarki Dariyus.
7 Ils lui envoyèrent une lettre, dans laquelle était écrit: Au roi Darius, toute la paix.
Ga rahoton da suka aika masa. Zuwa ga Sarki Dariyus. Gaisuwa da fatan alheri.
8 Sachez au roi que nous sommes allés dans la province de Juda, à la maison du grand Dieu, qui se construit avec de grosses pierres et dont les murs sont couverts de bois. Cet ouvrage se poursuit avec diligence et prospère entre leurs mains.
Ya kamata sarki yă sani cewa mun je yankin Yahuda, zuwa gidan Allah mai girma. Muka ga mutanen suna ginin haikalin da manyan duwatsu, suna sa katakai a bangon. Ana aikin da ƙwazo, aikin kuma yana cin gaba sosai, suna kuma lura da shi.
9 Alors nous avons interrogé ces anciens, et nous leur avons dit ainsi: « Qui vous a donné l'ordre de construire cette maison et d'achever cette muraille? »
Mun tambayi dattawan muka ce musu, “Wa ya ba ku iko ku sāke gina wannan haikali, ku kuma sāke gyara katangarsa?”
10 Nous leur demandâmes aussi leurs noms, afin que nous puissions écrire les noms des hommes qui étaient à leur tête.
Muka kuma tambaye su sunayensu don mu rubuta mu sanar da kai waɗanda suke shugabanninsu.
11 Ils nous répondirent en disant: « Nous sommes les serviteurs du Dieu du ciel et de la terre et nous bâtissons la maison qui a été construite il y a tant d'années, qu'un grand roi d'Israël a bâtie et achevée.
Wannan ita ce amsar da suka ba mu. “Mu bayin Allah na sama da ƙasa ne, muna sāke gina haikalin da aka gina tun shekaru da yawa da suka wuce, da wani babban sarkin Isra’ila ya gina ya kuma gama.
12 Mais après que nos pères eurent provoqué le Dieu du ciel à la colère, il les livra entre les mains de Nabuchodonosor, roi de Babylone, le Chaldéen, qui détruisit cette maison et emmena le peuple à Babylone.
Amma domin kakanninmu sun ɓata wa Allah na sama rai, sai ya bari suka fāɗa cikin hannun Nebukadnezzar mutumin Kaldiya, sarkin Babilon, wanda ya rushe wannan haikali, ya kuma kwashe mutane zuwa Babilon.
13 Mais la première année de Cyrus, roi de Babylone, le roi Cyrus donna l'ordre de construire cette maison de Dieu.
“Duk da haka, a shekara ta farko ta mulkin Sairus sarkin Babilon, Sarki Sairus ya ba da umarni cewa a sāke gina wannan gidan Allah.
14 Les objets d'or et d'argent de la maison de Dieu, que Nabuchodonosor avait enlevés du temple de Jérusalem et transportés dans le temple de Babylone, le roi Cyrus les enleva aussi du temple de Babylone et les remit à un certain Sheshbazzar, qu'il avait nommé gouverneur.
Ya kuma kwashe kwanonin zinariya da azurfa na gidan Allah daga haikalin Babilon waɗanda Nebukadnezzar ya kwasa daga haikali a Urushalima. Sa’an nan sarki Sairus ya ba wa wani mutum mai suna Sheshbazzar umarni wanda ya sa ya zama gwamna,
15 Il lui dit: « Prends ces ustensiles, va les mettre dans le temple de Jérusalem, et que la maison de Dieu soit bâtie à sa place ».
ya ce masa, ‘Ka kwashe kayan nan ka je ka zuba su a cikin haikalin Allah a Urushalima. Ka kuma sāke gina gidan Allah a wurin da yake a dā.’
16 Alors le même Sheshbazzar vint et posa les fondations de la maison de Dieu qui est à Jérusalem. Depuis ce temps-là, jusqu'à maintenant, elle a été construite, et pourtant elle n'est pas achevée.
“Saboda haka Sheshbazzar ya so ya aza harsashin gina gidan Allah a Urushalima. Tun daga wancan lokaci har zuwa yau ana kan gina shi amma ba a gama ba.”
17 Maintenant, si le roi le trouve bon, que l'on cherche dans la maison du trésor du roi, qui est là à Babylone, s'il est vrai qu'un décret a été pris par le roi Cyrus pour construire cette maison de Dieu à Jérusalem; et que le roi nous envoie son bon plaisir à ce sujet. »
Yanzu in sarki yana so, bari a duba cikin littattafan tarihi na sarakuna na Babilon a gani ko lalle sarki Sairus ya ba da umarni a sāke gina gidan Allah a Urushalima. Bari sarki yă aiko mana da abin da ya gani game da wannan abu.

< Esdras 5 >