< Ézéchiel 9 >

1 Alors il cria à mes oreilles d'une voix forte, en disant: « Fais approcher ceux qui ont la garde de la ville, chacun avec son arme de destruction à la main. »
Sai na ji ya yi kira da babbar murya yana cewa, “Kawo matsaran birni a nan, kowanne da makami a hannunsa.”
2 Et voici que six hommes arrivèrent par le chemin de la porte supérieure, qui se trouve vers le nord, chacun avec son arme de destruction à la main. Un homme au milieu d'eux était vêtu de lin, avec un cornet d'écrivain à son côté. Ils entrèrent et se placèrent à côté de l'autel de bronze.
Na kuma ga mutane shida suna zuwa daga kowane gefen ƙofar ta bisa, wadda take fuskantar arewa, kowanne da makamin kisa a hannunsa. Tare da su akwai mutum saye da lilin yana rataye da jaka ƙunshe da kayan rubutu a gefensa. Suka shiga suka tsaya kusa da bagaden tagulla.
3 La gloire du Dieu d'Israël monta du chérubin, où il se trouvait, jusqu'au seuil de la maison; et il appela l'homme vêtu de lin, qui tenait à son côté l'encornoir de l'écrivain.
To, fa, ɗaukakar Allah na Isra’ila ta haura daga bisa kerubobi, inda ta kasance, ta tashi zuwa bakin madogarar ƙofar haikali. Sai Ubangiji ya kira mutumin da yake saye da lilin wanda ya rataye jaka ƙunshe da kayan rubutu a gefensa
4 Yahvé lui dit: « Passe par le milieu de la ville, par le milieu de Jérusalem, et mets une marque sur le front des hommes qui soupirent et qui pleurent sur toutes les abominations qui se commettent dans son sein. »
ya ce masa, “Ka ratsa birnin Urushalima ka sa shaida a goshin waɗanda suke baƙin ciki da kuma makoki a kan dukan abubuwan banƙyamar da ake yi a cikinsa.”
5 Aux autres, il dit à mon oreille: « Traversez la ville après lui, et frappez. Ne laissez pas votre œil épargner, et n'ayez pas de pitié.
Yayinda nake saurara, sai ya ce wa waɗansu, “Ku bi shi ta birnin ku kuma kashe, babu tausayi ko kuwa jinƙai.
6 Tuez par interdit le vieillard, le jeune homme, la vierge, les petits enfants et les femmes; mais n'approchez pas de l'homme qui porte la marque. Commence par mon sanctuaire. » Puis ils se sont attaqués aux vieillards qui étaient devant la maison.
Ku kashe tsofaffi da samari da’yan mata, mata da yara, amma kada ku taɓa wani wanda yake da shaida. Ku fara a wuri mai tsarkina.” Saboda haka suka fara da dattawan da suke gaban haikali.
7 Il leur dit: « Souillez la maison, et remplissez les parvis de morts. Sortez! » Ils sont sortis, et ont frappé dans la ville.
Sa’an nan ya ce musu, “Ku ƙazantar da haikalin ku kuma cika filayen da kisassu. Ku tafi!” Saboda haka suka fita suka kuma fara kisa a duk birnin.
8 Pendant qu'ils tuaient, et que je restais, je tombai sur ma face, et je criai, en disant: « Ah! Seigneur Yahvé! Détruiras-tu tout le reste d'Israël en déversant ta colère sur Jérusalem? »
Yayinda suke kisan sai aka bar ni kaɗai, na fāɗi rubda ciki, na yi kuka na ce, “Kash, Ubangiji Mai Iko Duka! Za ka hallaka dukan raguwar Isra’ila a wannan zafin fushinka a Urushalima?”
9 Puis il me dit: « L'iniquité de la maison d'Israël et de Juda est extrêmement grande, le pays est plein de sang, et la ville pleine de perversion; car ils disent: « Yahvé a abandonné le pays, et Yahvé ne voit pas.
Ya amsa mini ya ce, “Zunubin gidan Isra’ila da Yahuda ya yi girma ainun; ƙasar ta cika da rashin adalci. Suna cewa, ‘Ubangiji ya yashe ƙasar; Ubangiji ba ya gani.’
10 Quant à moi aussi, mon œil n'épargnera pas, je n'aurai pas de pitié, mais je ferai retomber leur voie sur leur tête. »
Saboda haka ba zan dube su da tausayi ko kuwa in ƙyale su ba, amma zan kawo wa kansu abin da suka yi.”
11 Voici que l'homme vêtu de lin, qui tenait l'encornoir à son côté, fit son rapport en disant: « J'ai fait ce que tu m'as ordonné. »
Sai mutumin da yana saye da lilin yake kuma rataye da jaka ƙunshe da kayan rubutu a gefensa ya mayar da magana, yana cewa, “Na yi yadda ka umarci ni.”

< Ézéchiel 9 >