< Ézéchiel 7 >
1 La parole de Yahvé me fut adressée, en ces termes:
Maganar Ubangiji ta zo gare ni cewa,
2 « Toi, fils d'homme, le Seigneur Yahvé dit au pays d'Israël: C'est fini! La fin est arrivée aux quatre coins du pays.
“Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yake cewa wa ƙasar Isra’ila, “‘Ƙarshe ya zo! Ƙarshe ya zo a kan kusurwoyi huɗu na ƙasar.
3 Maintenant la fin est sur toi, et j'enverrai ma colère sur toi, et je te jugerai selon tes voies. Je ferai retomber sur vous toutes vos abominations.
Ƙarshe yanzu yana a kanki. Zan fashe fushina a kanki. Zan shari’anta ki bisa ga halinki in sāka miki kuma saboda dukan ayyukan banƙyamar da kika yi.
4 Mon œil ne vous épargnera pas, et je n'aurai pas de pitié; mais je ferai venir sur vous vos voies, et vos abominations seront au milieu de vous. Alors vous saurez que je suis Yahvé ».
Ba zan dube ki da tausayi; ko in ƙyale ki ba. Tabbatacce zan sāka miki saboda halinki da kuma ayyukanki masu banƙyama a cikinki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji.’
5 « Le Seigneur Yahvé dit: « Un désastre! Un désastre unique! Voici qu'il arrive.
“Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, “‘Masifa! Masifar da ba a taɓa gani ba tana zuwa.
6 La fin est venue. La fin est venue! Elle se réveille contre toi. Voici, elle arrive.
Ƙarshe ya zo! Ƙarshe ya zo! Ya farka a kanki. Ga shi, ya zo!
7 Ta fin est arrivée, habitant du pays! L'heure est venue! Le jour est proche, jour de tumulte, et non de cris de joie, sur les montagnes.
Ƙaddara ta auko miki, ya ke wadda ke zama cikin ƙasar. Lokaci ya yi, rana ta gabato; akwai fargaba, ba farin ciki ba, a kan duwatsu.
8 Maintenant, je vais bientôt répandre sur toi ma fureur, accomplir ma colère contre toi, et te juger selon tes voies. Je ferai retomber sur toi toutes tes abominations.
Ina gab da fasa hasalata a kanki in kuma aukar da fushina a kanki; zan shari’anta ke bisa ga halinki in kuma sāka miki saboda dukan ayyukanki masu banƙyama.
9 Mon œil n'épargnera pas, et je n'aurai pas de pitié. Je vous punirai selon vos voies. Vos abominations seront au milieu de vous. Alors vous saurez que c'est moi, Yahvé, qui frappe.
Ba zan dube ki da tausayi ko in ƙyale ke ba; zan sāka miki bisa ga halinki da kuma ayyukan masu banƙyama a cikinki. Sa’an nan za ki san cewa ni ne Ubangiji wanda yake bugunki.
10 "'Voici le jour! Voici qu'il arrive! Ta malédiction est sortie. La verge a fleuri. L'orgueil a bourgeonné.
“‘Ga shi ranar ta zo! Ta iso! Ƙaddararki ta keto, sandar ta yi toho, girman kai ya yi fure!
11 La violence s'est élevée en un bâton de méchanceté. Il ne restera rien d'eux, ni de leur multitude, ni de leurs richesses. Il n'y aura rien de précieux parmi eux.
Rikici ya yi girma ya zama sandar da za a hukunta mugunta; babu wani daga cikin mutanen da za a bari, babu wani dukiyarsu da za a bari, babu wani abin amfani.
12 Le temps est venu! Le jour approche. Que l'acheteur ne se réjouisse pas, et que le vendeur ne se lamente pas, car la colère est sur toute sa multitude.
Lokaci ya yi! Ranar ta gabato! Kada mai saya ya yi farin ciki ko kuwa mai sayarwa ya yi baƙin ciki, gama hasala tana a kan dukan jama’a.
13 Car le vendeur ne reviendra pas à ce qui est vendu, bien qu'ils soient encore en vie; car la vision concerne toute sa multitude. Nul ne reviendra. Nul ne se fortifiera dans l'iniquité de sa vie.
Mai sayarwa ba zai mayar da ƙasar da ya sayar tuntuni ba muddin dukansu suna da rai, gama ba za a sauya wahayin da ya shafi dukan jama’a ba. Saboda zunubansu, babu ɗayansu da zai adana ransa.
14 Ils ont sonné de la trompette et se sont préparés; mais personne ne va au combat, car ma colère s'abat sur toute sa multitude.
“‘Ko da yake suna busa ƙaho suna kuma shirya kome, ba wanda zai tafi yaƙi, gama hasalata tana a kan dukan jama’a.
15 "'L'épée est au dehors, la peste et la famine au dedans. Celui qui est dans les champs mourra par l'épée. Celui qui est dans la ville sera dévoré par la famine et la peste.
A waje takobi ne, a ciki annoba ne da yunwa; waɗanda suke fili za su mutu ta wurin takobi, waɗanda kuma suke cikin birni yunwa da annoba za su cinye su.
16 Mais ceux qui échapperont, ils s'échapperont et seront sur les montagnes comme les colombes des vallées, tous gémissant, chacun dans son iniquité.
Duk waɗanda suka tsira suka tsere za su kasance a cikin duwatsu, suna kuka kamar kurciyoyin kwaruruka, kowanne saboda zunubansa.
17 Toutes les mains seront affaiblies, et tous les genoux seront faibles comme de l'eau.
Kowane hannu zai raunana, kowace gwiwa kuma za tă zama marar ƙarfi kamar ruwa.
18 Ils se revêtiront de sacs, et l'horreur les couvrira. La honte sera sur tous les visages, et la calvitie sur toutes leurs têtes.
Za su sa tufafin makoki su kuma rufu da fargaba. Fuskokinsu kuma za su rufu da kunya a kuma aske kawunansu.
19 Ils jetteront leur argent dans les rues, et leur or sera comme une chose impure. Leur argent et leur or ne pourront les délivrer au jour de la colère de Yahvé. Ils ne rassasieront pas leurs âmes et ne rempliront pas leurs ventres, car ils ont été la pierre d'achoppement de leur iniquité.
“‘Za su zubar da azurfarsu a tituna, zinariyarsu kuma za tă zama ƙazantacciyar aba. Azurfarsu da zinariyarsu ba za su iya cetonsu a ranar hasalar Ubangiji ba. Ba za su ƙosar da yunwansu ko su cika cikinsu da shi ba, gama su ne sanadin tuntuɓensu cikin zunubi.
20 Quant à la beauté de sa parure, il l'a placée dans la majesté; mais eux, ils y ont placé les images de leurs abominations et de leurs choses détestables. C'est pourquoi je l'ai rendu pour eux comme une chose impure.
Sun yi fariya kyan kayan adonsu suka kuma yi amfani da su don su yi gumakansu masu banƙyama, da ƙazantattun abubuwa.
21 Je la livrerai aux mains des étrangers comme butin, et aux méchants de la terre comme pillage, et ils la profaneront.
Zan ba da su duka kamar ganima ga baƙi da kuma kamar abin da aka washe ga mugayen duniya, za su kuma ƙazantar da su.
22 Je détournerai aussi ma face d'eux, et ils profaneront mon lieu secret. Des voleurs y entreront, et le profaneront.
Zan juye fuskata daga gare su, za su kuwa ƙazantar da wurina mai daraja;’yan fashi za su shiga su kuma ƙazantar da shi.
23 "'Faites des chaînes, car le pays est plein de crimes sanglants, et la ville est pleine de violence.
“‘Ka shirya sarƙoƙi, domin ƙasar ta cika da alhakin jini, birnin kuma ya cika da rikici.
24 C'est pourquoi je ferai venir les pires des nations, et elles posséderont leurs maisons. Je ferai aussi cesser l'orgueil des puissants. Leurs lieux saints seront profanés.
Zan kawo al’ummai mafi mugunta su mallaki gidajenku; zan kawo ƙarshen fariyar masu ƙarfi, Wurare Masu Tsarkinsu za su ƙazantu.
25 La destruction arrive! Ils chercheront la paix, et il n'y en aura pas.
Sa’ad da wahala ta zo, za su nemi salama, amma ba za su same ta ba.
26 La calamité succédera à la calamité, et la rumeur à la rumeur. Ils chercheront la vision du prophète; mais la loi disparaîtra du sacrificateur, et le conseil des anciens.
Masifa a kan masifa za su zo, jita-jita kuma a kan jita-jita. Za su yi ƙoƙarin samun wahayi daga annabi; koyarwar doka ta wurin firist za tă ɓace, kamar yadda shawarar dattawa za tă ɓace.
27 Le roi sera dans le deuil, et le prince sera revêtu de désolation. Les mains des habitants du pays seront troublées. Je les traiterai selon leur voie, et je les jugerai selon leurs propres jugements. Alors ils sauront que je suis Yahvé.'"
Sarki zai yi makoki, yerima zai fid da zuciya, hannuwan mutanen ƙasar kuma za su yi rawa. Zan sāka musu bisa ga ayyukansu, zan kuma hukunta su bisa ga ma’auninsu. Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji.’”